Chapter 10
Chapter 10
sanda na take masa baya. Na yi baƙin cikin haɗa ido da shi domin a yanzu ko mutuwa ban tsana kamar yadda na tsanesa ba, da saninsa aka yi ma mahaifina komai saboda ƴar'uwarsa har suka kashe shi. Bayan fitarsa Baba Sulaiman ya shigo yana mana bayanin yadda abun ya wakana lokacin da suka isa station ɗin. “Ko da muka je dpo baya nan, muka faɗawa ƴan sanda da ke nan, sai suka ce wai matarsa ce ta danka ta zo ta tafi da shi da ɗansa, Ayuba ya ce ai ba shi da ɗa namiji ma, kuma jiya mun zo nan kuka hana mana shi, sai suka ce bayan tafiyar mu matar da ɗansa suka zo suka tafi da shi, a gurin aka riƙa rigima wai su zayi ma ƙazafi, ɗayan su har da barazanar a barshi ya harbe mu, da suka ga abun na mu bana wasa ba ne yasa suka kira dpo, yana zuwa ya rufe su da faɗa, yasa aka tuɓe kayan ƴan sanda da suka yi aikin dare aka shigar da su cell, ya bamu dubu ashirin ɗin sai kuma ya biyo mu nan yana ƙara ba mu haƙuri” Baba Dahiru yaja tsaki. “Allah ya waddaran ƙasar nan, ai daga gani da saninsa aka yi komai, kuma babu matakin da zasu ɗauka, Allah dai ya isar ma ɗan'uwanmu kawai” Ni kaina jikina be bani za a ɗauki wani matakin ba, saboda na san mahaifina ba kowa ba ne a cikin unguwarmu balle kuma a gari. Maƙocin mu ne yayi ma Baba wanka saboda Inna ta kasa duk da kasancewar ta iya raunin zuciya be barta ta iya masa wanka ba, ban tabbatar da mai rai ba a bakin komai ya ke ba sai da aka ɗauko karaga aka saka gawar Baba aka fita da shi waje dan yi masa Sallah. Allahu akbar shine abunda na iya faɗa a zuciyata, na kwantar da kaina jikin Jidda hawaye na bin fuskata. Baba ya samu mutane sosai daman mutumen mutane ne, kuma wannan abun da ya faru ya ƙarawa mutane ƙaunarsa, har wasu na baranar idan ba a ɗauki mataki ba zasu ƙona station ɗin. Bayan an kai shi makocinsa suka dawo, mazan unguwa na ta shigowa suna mana gaisuwa, ciki har da Bilal da Babansa. Mutanen da suke zuwa mana gaisuwa kamar turo su ake, maza da mata ta ko'ina gaisuwa suke zuwa mana suna yi ma Baba addu'ah, maƙota kuma na ta kawo mana abinci, sai kuma gidan Baban gida da suka haɗa kuɗi duka siyo mana buhun shimkafa. Can da yamma Baba Sulaiman ya shigo yana tambayar mu ko ana binsa bashi. “Sai dai a tambaya guraren da yake zama amman Malam be cika cin bashi ba, shi dai bar shi da zuwa gidan ciyaman neman kuɗi” “Toh zamu bincika, Alhaji Sani ma ya zo nan yace yana muku gaisuwa” “Toh muna amsawa, Allah ya bada lada” Baba Sulaiman ne yayi ta ɗawainiya da mu tun da Baba ya rasu har ranar da aka yi addu'ah ukunsa. A daren ranar sai gidan ya zame nama wayan kamar Baba be taɓa wanzuwa a cikin gidan ba. Ina daga cikin ɗaki na hango Habiba ta ɗauki tabarma ta je ta shimfiɗa gurin da Baba yake zama ta kwanta. Tausayinta ne ya kama ni na unƙura na tashi naje kusa da ita na zauna, sai ta ɗago kai ta kalleni. “Nawwara” “Na'am” Na amsa mata ina danne tausayinta da ke raina. “Yanzu ya zan yi Baba ya yafe min? Na yi tunanin Baba zai rayu na roƙi gafararsa wata rana” Hannu na kai na ɗaga kanta na ɗora saman cinyata yayinda fuskarta ke fuskantar ƙofar ɗakin Inna, cikin ƙarfin hali da dauriya na soma mata magana. “Idan har Allah ya yafe miki, to Baba ma ya yafe miki, amman Habiba kin ga abunda kika aikata be amfana miki komai ba, tun da kuɗin ma be amfana komai ba, da kin yi haƙuri da baki siyar da mutuncinki ba” “Wallahi Nawwara ban ɗauka Baba zai mutu ba, a tunani zai rayu ne, kuma ni ina ganin kamar bamu da wata mafita sai wannan” “Da sata kika je kika yi Habiba ko kika yi bara, zai fi wannan abun da kika aikata” Shiru ta yi tana shesshekar kuka, yayinda ni nake hawaye. Can ƙasa-ƙasa ta soma magana. “Masu kuɗi suna da kuɗi Nawwara amman basa taimako, babu ruwansu da matsalar mu, idan mun ci babu ruwansu idan ba mu ci ba sai dai mu mutu” Ajiyar zuciya na sauke cike da gasgata zancen Habiba, haƙiƙa masu abu na da shi amman babu ruwansu da mu, ko ɗan abincin nan a zuba a abawa maƙota basa yi. Tashi ta yi zaune tana kallona, cikin kuka ta soma magana. “Nawwara sai da na je gidan Hajiya Murja na faɗa mata halin da muke ciki, har ƙarya na yi mata Inna na ce tace a ara mata kuɗi, ta ce min bata da kuɗi amman dai za ta yi ma mijinta magana. Da na fito sai na haɗu da ɗanta Mustapha a harabar gidan, shi ya kirani ya tambayeni miya kawo ni gidan, na faɗa masa sai ya ce zai bani kuɗin amman na masa alƙawarin duk abunda ya ce zan masa, na ce na yi, muka fita daga gidan gaba ɗaya, ya fiddo kuɗi da yawa a aljihunsa ya ƙirga dubu ashirin, har zai ba ni sai kuma ya fasa, ya ce sai idan na aminta na na bashi abunda ya ke so yanzu, na ce mi yake so, ya ce kawai taɓa jikina zai yi sai ya bani kuɗi shi ba iskanci zai yi da ni ba, har da min ratsuwa” Ta yi shiru. Can kuma sai ta cigaba. “Na ƙi yarda na nufo haɓyar gida, har na kawo sai kuma na ga ba mu da wata mafita sai wannan, dole tasa na koma, ko da na koma ya fita, sai nasa mai gadinsa ya kirashi a waya yace ina nemansa, sai yace na same shi gidansu killers, haka na je gidan na same shi shi kaɗai a gidan, sai... Sai... Sai. Ya ya.. Riƙani Wallahi Nawwara cewa kawai yayi zai taɓa jikina ya ba ni kuɗi, amman shi ne ya kira har da abokinsa suka.. Suka.. Suka yi.. Yi iskaci da ni...” Ba shiri na buɗe baki ina kallonta hawaye na bin fuskata. *RAI BIYU...♥️🖤* Wattpad @Khadeeja_Candy 9⃣ “Miyasa ba ki masa ihu ba?” “Mi zai sa na yi masa bayan ni na kaina? Idan na masa ihu ba zai ba ni kuɗin ba kuma zai iya dukana ma” Kwantar da ita na yi jikina, ina kuka kamar yadda ita na take. Har dare ya bara muna zaune ni da ita a gurin muna aikin kuka. Wannan abu shi ya zame min jiki, a duka lokacin da na keɓe ni kaɗai na kan yi kukana sosai, saboda tausayin rayuwar Inna da Sakina da Jamila, sai kuma Habiba da kullum na ke zullumin idan ciki be shige ta ba. Yau ce ranar da Baba ya cika sati ɗayda rasuwa, har kuma tsawon lokacin ba mu sake jin wani abu daga gurin ƴan sandan ba, da yamma Baba Sulaiman ya samu Inna a gida yana faɗa mata gobe zasu je su ji
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119