Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 79

Chapter 79

Rai Biyu Book 1 Complete Hausa Novel 1,199 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

son ta bayan shi, abu daya yake ce masa tuwo a kwarya a yanzu ba komai bane face rashin iya karatun kur'anen, haka zai dauko kur'anen ya rike but he can't read it ko baki be iya hadawa balle har ya tada ya karanta aya, and now he need to know his religion more than everything, yana son yasan abunda Allah ya ce da kuma wanda ya hana, zuciyarsa na raya masa idan har ya shiryu ya zama na kwarai Nawwara zata so shi, a duk lokacin da ya tuna da dansa yana asibiti sai ya ji kamar zai mutu saboda yana son naje ganinsa sai dai yasan Nawwara ba zata bari ba. Haka ya jera kwana uku be sake saka Noor a ido ba a duk lokacin da tunaninsa ya taso masa sai ya dauki cocaine din ya sha sannan ya samu sassauci. Misalin karfe biyu dare yana zaune saman carpet yana istigifari sai ga Abbah ya kirashi, da fari ya ji tsoro dan yasan Abbah be saba kiranshi a irin wannan lokacin ba, sai kuma daga baya wani tunanin ya zo masa na cewar wata kila Abbah zai masa fada ne akan rashin zuwa aiki da ya yi kwana biyu. “Hello” “Jibril kana lafiya?” “Lafiya kalau Abbah” “Ka tabbata?” “Lafiya ta kalau” “Allah ya tsare ka, kawai na yi wani mafarki ne marar kyau ina fatar babu komai ko? ” “Babu komai Abbah sai damuwa, Nawwara ta ki fahimta ta Abbah kuma akwai da a tsakaninmu” “Ni ma na samu wannan labarin lokacin da na je zan bawa iyalanta da kuma ita kanta hakuri akan abunda ka yi musu, sai dai ba samu ganin yaron ba” “Abbah da gaske? Yaushe ka zo?” “An kwana biyu, kawai dan ban fada maka ba ne” Abbah ya labarta masa komai daga zuwansa da kuma abubuwan da suka faru, Jibril ya ji dadi hakan ya tabbatar masa da mahaifinsa yana sonsa kuma yana tare da shi. “Abbah ka taimaka ka min izinin zuwa gidansu Nawwara Dan Allah” “Ka yi alkawarin ba zaka yi wani abu marar kyau ba?” “Taya mai neman hanyar gyara zai yi wani abu marar kyau? Wallahi Abbah ina son Nawwara sosai kamar zan hauka ce” “Amman da muka zaba maka ita ai cewa ka yi baka son ta” Ya yi shiru be ce komai ba, sai Abbah ya kara da “Kuma kasan sai dai ka yi hauka dan babu aure a tsakaninku ko? Kasan saki uku ka yi mata fa” Idanuwansa sun cika da kwalla. “Yanzu Abbah babu wani gyara da za a iya yi? Ba wata mafita?” “Babu zan kwanta sai da safe” Abbah ya kashe wayarsa, sai Jibril ya fara surutai “Dole akwai mafita Wallahi, dole a samu mafita No no no” Wannan tunanin ne ya hana shi bachi har garin Allah ya waye, tun da asuba ya shirya ya fita, kai tsaye asibitin ya nufa. Ya taki sa'a yau Nawwara ce kwana asibitin, ko da ya tura kofar dakin ya shiga zuciyarsa na bugawa dan ya yi tunanin zai samu Inna a ciki ne ko kuma ya tararda Nawwara a farke, sai ya tarar tana kwance bayan Noor saman gadon asibitin suna ta bachinsu a tare, karasawa ya yi kusa da su fuskarsa dauke da murmushi yana kallon iyalinsa. Wayarsa yasa ya dauke su hoto sannan ya cire jacket dinsa ya lulluba musu ya zauna saman kujerar da ke facing dinsu yana ta kallonsu cike da shauki. “Na bata komai, da yanzu muna nan a iyali daya” Kadan kadan yake maganar amman hakan be hana Noor farkawa daga guntun bachinsa ba, sosai da sosai yake kallon Jibril ganin wani babban mutum mai kama da shi, sai kuma ya unkura ya tashi zaune zai yi magana Jibril ya dora hannunsa saman bakinsa ya yi masa alama da ya yi shiru. “Shiiiiiiiiiiii” Sai ya mika masa hannu alamar ya zo, ba musu Noor ya mika masa nashi hannayen sai ya dauke shi ya zaunar saman jikinsa ya rumgume ya lumshe ido. Hawayen farinciki da bakinciki suka cika masa ido lokaci daya. “Waye kai kai likita ne?” Noor ya tambaya da muryarsa yar karama. Sai Jibril ya girgiza masa kai alamar a a ba tare da ya bude idon ba. Shi kuma sai ya sake tambaya cike da mamaki yana ta kallon fuskarsa. “Kai ne wanda Inna ta ce min zaka zo ka ganki? Kai ne Uncle din?” Ya gyada masa kai still be bude idon ba dan baya son Noor ya ga hawayensa, Nawwara kam bachi kawai take abinta bama san ana yi ba. NAWWARA POV. karar bude kofar da aka yi ne ya tasheni daga dogon bachin da na ke, sai turaren da na fi tsana a duniya ya yi marhaban sannan na kula da jacket din da aka lulluba min saman jiki. Inna na gani zaune tana jan karbi ba Noor a kusa da ni kamar yadda muka kwanta, saurin zabura na yi. “Ina Noor?” “Yana gurin Babansa” “Dauke sa ya yi? Miyasa kika bari ya shigo?” “Ke ya kamata na tambaya dan nan na shigo na sameshi” Na sauka saman gadon hankalina a tashe sai Inna ta rike hannuna. “Ba gudu zai yi da shi ba, sun fita waje ne su sha iska, ina tunanin ya canja Nawwara a nan ya durkusa yana ta ba ni hakuri, wannan abincin karyawar da kika gani daga kamfani yasa aka kawo” “Wallahi zai iya gudun min da da mugu ne” Na fita daga dakin hankalina a tashe, ina fitowa harabar asibitin sai na hango Noor saman motarsa zaune shi kuma na jikina jikin motar ya rumgume Noor. Karasa na yi ina masa fada. “Waya baka izinin fitar min da da?” Sai ya dago ya kalleni sai ya sauko da Noor da ko riga babu a jikinsa. “Ki yi hakuri na fita da shi ne ya sha iska” Daukar Noor na yi na koma da shi ciki, shi ko sai zuba min tambaya yake akan wannan Uncle din nasa da Inna take fada masa zai zo ya duba shi. A ranar duk wanda ya kawo mana ziyarar dubiya ya tararda Jibril a asibitin saboda nan ya wuni, duk wani tafiyar numfashin Noor yana kula shi hannun kuma maikaraya yana kula da shi sosai, na yi mamakin da Zinatu ta zo ganin Noor ko da yake ba abun mamaki ba ne duba da Jibril yana cikin asibitin, yau kan Bilal dake zuwa kullum duba Noor ya tarar da Jibril wanda hakan yasa shi kin sakewa sosai daman kwana biyu nan na rasa gane kansa, hakan be min dadi ba dan ban jidadin ganin da Bilal ya yi ma Jibril a asibitin ba, ni kuma na raka shi har gurin gate din asibitin sannan na dawo. A lokacin Jibril ne kawai cikin dakin Jibril ne kawai sai Noor suna rike da hannun juna, daman Inna waje ta koma da zama bata iya zama a cikin dakin matukar Jibril na ciki. Kamar jira yake na shigo sai ya mike tsaye ya nuna ni da yatsa fuskarasa a kumbure saboda bacin rai ya ce. “Kar Bilal ya sake zuwa duba min yaro wannan ya zama na farko kuma na karshe...” Kallonsa na ke sai ma na rasa abunda zan ce masa, daman

Table of Contents

Chapters

119 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});