Chapter 5
Chapter 5
BIYU...♥️🖤* Wattpad @Khadeeja_Candy 4⃣ Inna ta doso inda na ke a yayinda da juyo cikin gida hawaye na bin fuskata. “Nawwara lafiya?” Ban san ta ya zan faɗa mata ba, sai dai babu wata damar ɓoye mata dole na faɗa mata gaskiya. “Wai Baba aka kama, yana station ɗin ƴan sanda” “Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un” Ta faɗa tana dafe kanta fuskarta na bayyana tashin hankalin da ke zuciyarta. “Mi yayi musu?” “Nima ban sani ba, na tambaya ya ce idan na je can zan sani” “Mun shiga uku muna cikin wannan halin kuma wani za mu shiga” “Ina ganin sharar fage ne ga wata sabuwar rayuwa” Na faɗa ina hawaye. Bata kula zance ba ta shiga ɗaki ta ɗauko tsohon Hijabinta ta saka tana ce min. “Zan je na faɗawa Dahiru muje tare, ke kije ki faɗa a babban gida” Bata ko tsaya jiran abunda zan faɗa ba ta fita hankalinta a tashe. A take nima na saɓi mayafina, na ja ƙofar gidan na nufi babban gida wato gidan kakaninmu. Babban gida ne mai ginin ƙasa da laka irin gidan nan da ake a zamanin baya wanda a yanzu ake kira da family house, ba kasafai na ke son zuwa gidan ba saboda mutanen da ke ganin mutunci na da na ubana basa a raye a yanzu, wato kakanin na kenan waɗanda suka haifi ubana, sai dai ƙanen da ƴaƴansu da suke ganin kamar Baba yayi mana gata dan ya ware mu daban, duk laifin duniya da ganin kamar mu munfi kowa sai suka ɗauka suka ɗora mana har wasu na cewa wai dan Tsoho ba shi da rai ne tasa Baba yin haka. Alhalin ba haka ne kawai Baba baya son rigima ne da ƙaƙanan maganganu da yawan anyi an'ce kamar ya kashesu. Sashensu Yakumbo na fara shiga wato gwaggo Babana, tana ganin hawaye a fuskata tasan ba lafiya. “Tsohuwa Lafiya?” “Baba aka kama” “Kama kamar ya? Kamu na ƴan sanda ko mi?” A take ya zayyana mata komai ina hawaye. Miƙewa ta yi tsaye ta fita tsakar gida duk da jikin nata babu wani dogon ƙwari saboda tsufa. Kan ka ce kwabo har ƙofarta ta cika da ƴan cikin gida kowa na tambayar ba'asi, abunda na faɗa mata shi na faɗa musu, sai tasa aka kira ƙannen Babana wanɗanda basa nan a waya ta sanar musu. Ban baro gidan ba sai da aka kira sallah azahar kuma har lokacin Inna bata dawo ba. Sakina da Jamila kan suna tsakar gida zaune, Noor ne kawai yake sha'aninsa, ina shiga suka yo kaina da tambaya. “Anty ina kika je?” “Baban gida na je” “Me kika je yi, ina Inna?” Yara ne ƙanana a tunani be kamata na sanar su wannan maganar yanzu ba. “Na riga Inna fita ban san inda taje ba, ni na je gaishe su ne kawai” Noor ya zo ya riƙe min hannu. “Momy yunwa na ke ji, kunon da na sha ya ƙare” Hannu da ke cikin nasa na sunce na nufi ɗaki dan bana son yaga ƙwalla da suka cika min ido. Ɗan kuka na yi kaɗan a ɗakin domin idan na yi da yawa zai tona asirin abunda na ke ɓoyewa Sakina da Jamila ne, fito na yi waje na yi alwala na koma ɗakin na shinfiɗa ɗankwalina na yi sallah azahar, babu irin addu'ar da ban yi am Baba ba duk ya ke ban san halin da yake ciki ba ko kuma dalilin kama ɗin shi ɗin ba, na roƙar masa mafita da sauƙi ga Allah, tun a cikin sujudar ƙarshe har a cikin zaman tahiya zuwa addu'ar da ake bayan sallamewa. Ƙarfe biyu da kwata Habiba ta dawo gida cikin uniform ɗinta na makaranta. Tun da ta yi sallama na kasa amsa mata ta fahimci akwai matsala. Hijabi ne kawai ya zame mata dole ta cire ta nufo inda na ke zaune ta dafa ni. “Nawwara mi ya faru” Idan na ce zan ɓoye mata hawayena to zan yaudareta ne kawai, domin ta riga ta ga yadda hawayen ya ke sauƙowa daga idona, bakina kuma a gumɗe ina gintse kuka da ke son fito. “Ki faɗa min mana ina Inna?” Ta sake tambaya idonta na cika da ƙwalla. “Habiba ƴan sanda sun kama Baba, tun safe Inna ta je har yanzu bata dawo ba” Ta ɗora hannu saman kai. “Mun shiga uku? Mi yayi musu?” “Wallahi ni ma ban sani ba” A gurin ta zauna ta fara kuka kamar an yi mana mutuwa, daman Habiba bata da taurin zuciya irina, zan iya ɓoye kukana ko kuma bayyanawa a duk lokacin da nake buƙatar hakan amman Habiba bata iya wannan, a duk lokacin da abun kukan ya sameta a take zaka gane. Sakina da Jamila har da Noor suka shigo ɗakin a guje suna kallonta, nima kallonsu na ke hawaye na bin fuskata. Sallamar Inna da muka ji ne yasa muka ɗunguma gaba ɗaya muka fita waje, tana kallonmu sai ta fashe da kuka ta faɗi zaune. Daga ni har Habiba kasa tambaya mukayi kowa da abunda yake saƙawa a zuciyarsa, musamman ni da nake zargin ko sun kashe she ni. Jamila da Sakina ne suka ƙarasa inda take suna tambayarta. “Sata ake zargin mahaifinku yayi ta kimanin dubu ɗari biyu da saba'in” Tana faɗar haka ta ƙara fashewa da kuka, Habiba ta faɗi zaune irin jikinta ya mutu sosai, ni kuma na lumshe ido wasu zafafan hawaye suka zubo min. *RAI BIYU...♥️🖤* Wattpad @Khadeeja_Candy 5⃣ Haƙiƙa mahaifina talaka ne, amman bana tunanin wannan talaucin zai saka Baba sata, sai idan wani tsautsayin ne ko ma zai sata ba zai saci kuɗi har naira dubu dari biyu da saba'in ba, tau ina zai kaisu? “Miya ɗauka har na dubu ɗari biyu saba'in?” Habiba ta yi tambayar da na ke da niyar yi ma Inna. “Dako ya je yi kasuwa, wacce yaje yi ma dakon wayoyinta da ɗankunenta na zinari ya ɓata, ta ce wayoyinta na dubu ɗari da ashirin ne, ɗankunen zinarinta kuma dubu ɗari da hansi” Sulalewa na yi ƙasa hawaye na min zuba, babu zancen da nake tunawa kamar maganar mu ta ɗazu da safe, yadda na ke nanata masa kar yaje dakon nan kamar na san abunda zai faru. “Babu irin roƙon da ba'ayi mata ba ta ce ita ba zata haƙura sai an biyata” Inna ta faɗa cikin kuka. Sai duk muka saka kuka har su Sakina da Jamila, daman Habiba bakinta a buɗe yake tana aikin kukan. “Ku daina mana kuka tun da ba mutuwa aka yi ba” Cewar Inna tana share hawayenta. Bayan Inna ta bar gurin na miƙe tsaye na koma cikin ɗakin na zauna ina aikin kuka. Haka muna yi sallah isha'i cikin zullumi da tunanin makomar Baba har ma da tamu gaba ɗaya, bayan an yi sallah isha'i ne maƙota suƙa riƙa shigowa suna mana jaje. Ban taɓa yarda tashin hankali na hana bachi ba sai a wannan karon ina ji ina gani bachi ya ƙaurace daga idona. Alwala na fara gabatarwa kamin sallar nafila, har aka kira sallah asuba ina zaune saman ɗankwalina ina tasbihi, bayan na gama na yi ma Baba addu'a sannan na gabatar da sallah asuba. Tun da dungu-dungun safiya muka ji an buga mana ƙofa, Habiba ce ya je
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119