Chapter 4
Chapter 4
cikin unguwar” Bana da wata dabara ta da wuce na hau ɗin, babu tantanma idan har na zaɓi zuwa a ƙafa zan wahala sosai. Abun ka da mai nema sai kawai na gyara zane na na haye mashin kamar na yayana ko kuma na ce na Ubana. Bilal ba baƙona ba ne hakan yasa na sake da shi sosai muna fira har muka isa bakin ƙofar gidansu Zinatu. Na sauka ina masa godiya. “Am Nawancy na manta ban labarta miki wani abu ba, mun samu sabon shugaba a kamfaninmu kuma ya buƙaci sauye-sauye saboda yana da zafi sosai, kuma duk ya zubar da ma'aikatan gurin ya ce sabbi za a ɗauka, sai dai be faɗi rana ba, so ina fatar idan za a ɗauki wasu zaki yi applying” “Kai ka ce kai ma kun tsallake rijiya da baya” “Wallahi mun tsallake kan, domin mutumen akwai zafi sosai, gashi baya ganin kowa da mutuncin, ko dan yana kamfanin Mahaifinsa ban sani ba” “Ai fa ka ji to mu da ba wani zurfin ilmi mukayi an ya zai ɗauke mu kuwa, Bilal kafa san SSCE ne kawai da ni” “Abun sa'a ne Nawancy zaki iya shiga kuma ki yi sa'ar samu, ai kisan mataki mataki ne” “Naga Babban kamfani ne Bilal” Yayi wani abu da fuska yana matse hancin, irin yadda yake min a duk lokacin da zai zolayeni. “Trust me girl zaki samu babu tantama” Na yi murmushin da ya fitar da dimple ɗina, ina ƙara jan gyalena dan rufe jikina. “Ni zan wuce aiki kar na yi latti ya kore, dan ya faɗa mana idan ka ƙara minti ɗaya zai koreka daga kamfanin” “Tau Allah ya kiyaye na gode” Hannunsa ya ɗaga min. “Ina gaida abokina Noor” Kai na ɗaga masa as respond na juya kamar zan shiga gidansu Zinatu, ina hango ya kama hanya, na juyo dan har ga Allah ba gidansu Zinatu zanje ba na san ma by this time bata gida, ko ma tana nan mi zanje na yi a gidansu yarinyar da bata ƙaunar zuwa gidanmu. Miƙe ti-tin gawon nama na yi har na ɓullo ta gurin gidan Alu, wato tsohon gonnan, na miƙe na tsallaka babban titi na doshi Candy Restaurant. Restaurant ne mai kyau da tsari ga tsafta, ba laifi ma'aikatan gurin suna na'am-na'am da mutane tun a farkon zuwana na lura da hakan. Kai tsaye na nufi gurin wanda na ke zaton babbansu mai sanye da riga orange an rubuta mata Candy Restaurant da fafaren harufa. “Assalamu Alaikum” “Wa'alaikissalam” “Sannu ko ka gane ni?” “Gaskiya ban gane ki ba, abun da yawa” “Ni ce wacce na zo kwanakin baya ka ce min Khadeeja Candy bata nan” “Ayya Allah sarki, sai kuma kika ƙara rashin sa'a yau ma bata nan” “Dan Allah ko kasan yadda za'ayi ma sameta?” “Gaskiya bata garin nan tana Gusau kusan yanzu a can take zama, ko tana garin ma da wahala ta shigo nan” “Dan Allah ko zaka taimaka min da numberta?” “Gaskiya ba zan iya baki numberta ta saboda matsala ta tsaro, amman ke zaki iya barin Number idan ta shigo gari sai na sanar da ke” A take na rubuta masa Number Jidda domin bana da waya, kuma Baba ko Inna babu mai waya a cikinsu. “Idan ka kira ka ce Nawwara kake nema” “Tau Inshallah” “Na gode” “Yauwa a sauka lafiya” Jiki ba ƙwari na juya na fito. Har ga Allah ban jidaɗin rashin ta tararda mai restaurant ɗin ba, ga kuma uwar hanyar da zan miƙe duk da yaƙe rana be yi sosai ba, sai dai ina jin kamar zan wahalar da kaina tafiya a ƙafa har zuwa unguwarmu. “Allah ƙa zame min gata” Na furta a fili ina busar da iskar bakina. Dabarar na je gidansu Zinatu ne ya faɗo min a rai duk da ban yi niyar hakan ba. Haka na kama hanya na miƙe na koma ta inda na fito har na isa ƙofar gidansu Zinatu. Har na kai hannu zan buga ƙofar gate ɗin sai mai gaɗinsu ya wangale gate ɗin gaba ɗaya daga can ciki. Zinatu hakince a motarta ta kunno kai da alama fita zata yi, har ta yi kamar zata wuce sai kuma ta tsaya ta sauke gilashin motarta tana kallona ta cikin baƙin gilashin da yake idonta. “Khadija Musa Kafinta” Ta kirani da sunan da nake amfani da shi a makaranta, nima kuma sai na kirata da nata. “Zinatu Alhasan Hamshaƙi” Ta yi wani shu'umin murmushi tana cire gilashin idonta. “Nawwara ashe ana ganinki ko dai hanya ce ta biyo da ke?” “A'a haka kawai yau na ce zan kawo miki ziyara” Ta yi ƙis a ƙasan maƙoshinta wato ƙwafa na ƙasan maƙoshi. “Aiko kin kyauta gashi kuma zan fita, ki shigo na saukeki gida kawai” Na ji wani sanyi a raina daman abunda nake nema kenan. “Okay” Na faɗa sannan na buɗe motar na shiga. Jefi-jefi muke firar makarantarmu wato Nana Girl's Secondary School, kamin na ɗauko mata zancen masters da naji ance ta fara yi. “Wallahi ina nan ina yi yanzu haka kuma na samu aiki a wani babban kamfani this monday zan fara” “Mashallah, Allah ya taimaka” “Amin ai ke kin ƙi karatu ko?” “Uhmm” Na yi murmushi kawai ina danne abunda ke raina, yawancin mutane sukan faɗa min haka musamman abokaina wai na ƙi karatu bayan kuma karatun ne ya ƙi ni tun da komau sai da kuɗi, hawan napep zuwa da dawowa ma ai sai da kuɗi. Har ta sauke ni ƙofar gidanmu bata kalma bata sake fita daga bakinta, nima kuma ban sake ce mata wani abun ba. “Na gaida Inna” Ta faɗa lokacin da ta ga na buɗe mota zan fita. “Inna zata ji na gode” “Okay” A bakin ƙofar gidanmu na tsaya ina kallonta cike da sha'awar rayuwarta, duk mutune da yayi karatu burgeni yake, balle ita da ta fara cin amfanin karatun a yanzu. Sai da na daina hangota kan kwanar gunguwarmu mai kwatannin sannan na shiga gida. Inna na samu a tsakar gida tana shara, gyale na kawai na yaye ya karɓi tsintsinyar dake hannunta na cigaba da shara. “Allah yasa dai an yi sa'a” “Wallahi ba'ayi ba Inna wacce na je nema bata nan, amman na bada number wayata aje mata” “Allah yasa mu da ce, amman dai daga yau karki saki zuwa wani gurin ki haƙura idan ” “Amin, inshallah nima zan haƙura indai da rabon na samu zan samu” “Allah ya miƙi albarka” “Amin” Ta shinfiɗa tabarma ta zauna ni kuma na cigaba da sharar ina labarta mata cewar Zinatu ce ta kawo ni gida. Bayan na gam sharar na tattara na kwashe, muka ji ana sallama a ƙofar gida. Inna ce ta amsa ni kuma na nufi ƙofar dan duba ko wanene. Ganin mutun sanye da kakin ƴan sanda yasa gabana faɗuwa sosai. “Nan ne gidan Musa Kafinta?” “Eh Nan ne” Na amsa murya na rawa. “Musa Kafinta yana police station na guiwa locos, ana son a sanar da iyalansa ne kuma baya da waya shiyasa na zo” “Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, miya faru?” “Idan kika je can zaki ji” Ya juya yayi tafiyarsa, ni kuma na juyo cikin gida idona na zubar da ƙwalla. MAI KUKE TSAMANI A PAGE NA GABA? *RAI
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119