Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 93

Chapter 93

Gidan Aro Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Kinji koh..” Safeenah ta jinjina kai tana kuma goge fuskarta da mayafin dogon rigarta. Mommy tai k’wafa tana kad’a kai “Eh yayi.. Dole ka mata hud’uba kar Ta d’auki irin halayyana.. Duk abubuwan arziki na alkhairi da nai a baya ba’a gani ba sai yanzu za’a sami bakin kasheni da shike na gama jinyar nakasasshiyar matarka ba..” “Hajaraa!” Daddy ya darara mata tsawa yana mai d’ago hannu kaman zai kai mata mari.. Lokaci guda yake nunata da ‘yar yatsa “Ki iya bakinki kuma kar ki sake zagar mun mata, a yanda take a nakashe tafimun ke sau babu adadi.. Kuma da sannu zaki gani Allah zai bata lafiya ta dawo cikin gidan nan.. Tamkar bata tab’a jinya ba..!” Ya dubi Safeenah yace “Shige muje..” Babu musu Safeenah ta janyo suitcases d’inta tabi bayan Daddy. Aka bar Mommy baki sake tana duban bayansu har suka fice.. Yau itace Marwan yake cewa nakasasshiyar can ta fi masa ita, matar da ma cushe aka masa ba cewa yai yana sonta ba tun fil azal.. Lallai tun kafin ta makara gwara ta tura Shemau ta koma ta duba mata wanne hali Nuratu ke ciki.. Da wannan tunanin Mommy ta haura sama tana kiran Shemau. Shemau tana jin Mommy na kiranta tai rounding up wayar da suke da mijinta Salman. Ta dubi Mommy dake sakin huci ta tambayeta ya akai. Mommy ta sanar da ita komai cewa Daddy yakai Safeenah gidan Mu’azzam dukda irin cin kashin da Mu’azzam d’in yai masu, harda cewa da Daddy yai Nuratu tafi masa Ita. Tab’e baki kad’an Shemau tai tace “Ai kuwa gwara ki tabbata Nuratu bata sami lafiya ba dan da alama mijinki ya fara sonta tin kafin ta warke daga jinya.. Ina ji miki tsoro kar ta dawo Gidanki a kan k’afafunta bayan an fitar da ita a kwance.” Mommy ta sauk’e fuci tace “Kin mance cewa gidan mijina tamkar dai GIDAN ARO yake a wajenta.. Ai yanda aka fitar da ita a kwance Saidai a turata rami a haka.. Gidana ya haramta a gareta.. Yanda idan aka mutu ba’a sake dawowa Gidan Duniya haka itama yanda Ta fice daga gidan nan bata kuma dawowa.. Shemau ya kamata ki koma gida tinda dai Safeenar ta tare ki duba mana halin da nakasasshiyar cen ke ciki.” Shemau ta jinjina kai tace “Gawa zakice dan kullum jikinta dad’a gaba yake yanzu haka wayar da nayi da Salman abinda ya sanar dani kenan cewa jikin Nuratu yak’i dad’i har Inne ta fara tinanin ko mai magani za’a canza..” Mommy ta zaro ido dafe da k’irji tace “Shemau kar ki bari a canza mai magani.. Asirinmu zai tonu.!” Shemau ta murmusa kafin tace “Baki da damuwa hakan bazai tab’a yuwa ba.. Bazan bar hakan ta kasance ba. Yanzu Salman yace zai taho Abujan gobe Ina tsammanin Business trip ne, zai kwana biyu sai mu koma tare. Kinsan nace miki Su Husna sunata shirin waec ga twins ma na barsu wajen mai aiki gwara na koma sai naci gaba da saka mana idanu kan Nuratu.” Mommy ta jinjina kai tace “Hakan yayi.. Allah yasa kafin gobe muji Labarin nakasasshiyar nan ta mirgina..” Suka saki shewa suna masu tafe hannaye. ** Assad yana k’arasowa yai masa knocking da yatsar saman glass, lokaci guda Mu’azzam d’in ya danna unlock Assad ya ya bud’e ya shiga.. Kallo d’aya yaiwa Mu’azzam d’in ya basa tausayi.. Kai da gani Kasan abubuwa sun taru sun masa yawa k’arfin hali kurum yake. Assad yace “Ya jikin Mamy..?” Lumshe idanunsa kad’an Mu’azzam yai a hankali kafin yace “Munyi waya da Inne da safe tace mun jikin nata da sauki an gode Allah..” Assad ya jinjina kai yace “Allah ya bata alfiya yasa kaffara ne.. Allah ya tashi kafad’unta..” Mu’azzam ya amsa da “Ameen ya Allah..” “Safeenah fah..? Wanne kake ciki da nata batun..?” Ya d’an tab’e bakinsa kad’an kafin yace “I still don’t know.. Ban Sani ba Assad..” Assad ya fuzar da fuci kad’an cikeda tausayin Mu’azzam d’in kafin yace “Kar ka damu Mu’azzam Ubangiji yana jarabtar bayinsa ta ko wacce hanya.. Ba wai yak’ika bane yake aiko maka da jarabawa daki daki, daga wannan sai wancan.. Kai hak’uri sannan kai addu’a Allah ya baka ikon cin jarabawarka Brother..” Mu’azzam ya d’an kaikaito ya dubi Assad d’in kafin ya jinjina kai a hankali ba tareda ya iya furta koda kalma ba. Assad yace “Ta ina zamu fara yanzu..?” Mu’azzam ya d’ago yana dubansa kafin yakai ga basa amsa wayar Daddy ya shigo masa. “I’ll take this call, Daddy ne mai kira.” Assad ya jinjina masa kai ba tareda yace komai ba. Mu’azzam ya d’aga da sallama yana mai gaida Daddyn. Daga d’aya b’angaren Daddy ya amsa cikin sakin fuska kafin yace “Baka gida ne, gashi munzo bamu taddaka ba sai gateman.” Ya d’an dubi Assad kafin ya girgiza kai cikeda mamakin jin Daddy yana gidansa “No bana gida Daddy. Ai na fice..” Daddy ya jinjina kai yace “Toooh da kuwa gashi na taho da Safeenah ce zan had’aku gaba d’aya harda d’aya matar taka nai maku nasiha.” Jin abinda Daddy yace ya sanya Mu’azzam ware idanu babu shiri yana jin wani abu na neman toshe masa mak’oshi.. D’an girgiza kai yai kafin yace “Daddy you mean, ka kawo Safeenah yanzu haka..?” Daddy yace “K’warai kuwa Mu’azzam, na kawo maka matarka dan zaman nata a gida can baida wani alfanu.. Kyaun mace mai aure ta kasance a d’akinta shine cikan mutuncinta.. Sannan kaima shine cikan Kamalarka..” Mu’azzam ya jinjina kai a hankali kafin yace “Haka ne Daddy..Amma yanzu bana gida and.. Bazan dawo gida nan kusa ba..” Yai maganar cikeda jin nauyin Daddy. Daddy ya d’anyi jim kafin yace “Tooh lafiya dai koh..?” Mu’azzam ya jinjina kai kaman Daddy na ganinsa “Eh.. Eh wani aiki ne ya taso mun shisa zan d’an makara.” Daddy yace “Af Toh ai babu komai, nan gaba sai na had’aku na maku nasiha.. Ina ita matar taka take..?” Mu’azzam ya dubi Assad dan baisan mai zai sanar da Daddy ba.. Baisan ta yanda zai soma fad’a masa cewa Sadiya ta gudu daga gidan ba. Ya d’an shafi fuskarsa kad’an kafin yace “Bata gida inaga taje can wajen mahaifiyarta..” Daddy yace “Allah sarki toh shikenan.. Allah Ubangiji ya zaunar daku lafiya ya had’e maka kan iyalanka.. Allah shi maku albarka gaba d’ayanku..” Mu’azzam yanata amsa masa da Ameen kafin Daddy yai masa sallama yana mai sanar dashi ya bar Safeenah a gidan shi kuma ya koma gida. Suna ida wayar Mu’azzam ya dubi Assad yana mai kuma tura yatsun hannunsa cikin sumarsa. Assad ya d’an girgiza masa kai alamun meke faruwa. Mu’azzam ya d’aura duka hannayensa saman steering yana mai kuma fuzar da huci, idanunsa naga glass na gaban motar yake furta “Daddy yakai Safeenah gidana..” Assad ya murmusa yace “Kaga mai tagwayen mata.. Baka Farin ciki da hakan ne..?” Da wutsiyar idanu ya dubesa kafin yace “If she’s still my wife it’s because of Daddy..” Assad ya d’an girgiza kai kad’an yace “Mu’azzam, Safeenah batada wani laifi.. Kawai dai she got trapped ne.. Gashi Allah ya wanketa. Su Danger sunso saceta ne suka sace Ikram. At least ka godewa Allah da ya wanke Safeenah.. Ko Babu komai ‘yaruwarka ce kuma matarka ce Still da wutsiyar idanu

Table of Contents

Chapters

243 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
  170. 170 Chapter 170
  171. 171 Chapter 171
  172. 172 Chapter 172
  173. 173 Chapter 173
  174. 174 Chapter 174
  175. 175 Chapter 175
  176. 176 Chapter 176
  177. 177 Chapter 177
  178. 178 Chapter 178
  179. 179 Chapter 179
  180. 180 Chapter 180
  181. 181 Chapter 181
  182. 182 Chapter 182
  183. 183 Chapter 183
  184. 184 Chapter 184
  185. 185 Chapter 185
  186. 186 Chapter 186
  187. 187 Chapter 187
  188. 188 Chapter 188
  189. 189 Chapter 189
  190. 190 Chapter 190
  191. 191 Chapter 191
  192. 192 Chapter 192
  193. 193 Chapter 193
  194. 194 Chapter 194
  195. 195 Chapter 195
  196. 196 Chapter 196
  197. 197 Chapter 197
  198. 198 Chapter 198
  199. 199 Chapter 199
  200. 200 Chapter 200
  201. 201 Chapter 201
  202. 202 Chapter 202
  203. 203 Chapter 203
  204. 204 Chapter 204
  205. 205 Chapter 205
  206. 206 Chapter 206
  207. 207 Chapter 207
  208. 208 Chapter 208
  209. 209 Chapter 209
  210. 210 Chapter 210
  211. 211 Chapter 211
  212. 212 Chapter 212
  213. 213 Chapter 213
  214. 214 Chapter 214
  215. 215 Chapter 215
  216. 216 Chapter 216
  217. 217 Chapter 217
  218. 218 Chapter 218
  219. 219 Chapter 219
  220. 220 Chapter 220
  221. 221 Chapter 221
  222. 222 Chapter 222
  223. 223 Chapter 223
  224. 224 Chapter 224
  225. 225 Chapter 225
  226. 226 Chapter 226
  227. 227 Chapter 227
  228. 228 Chapter 228
  229. 229 Chapter 229
  230. 230 Chapter 230
  231. 231 Chapter 231
  232. 232 Chapter 232
  233. 233 Chapter 233
  234. 234 Chapter 234
  235. 235 Chapter 235
  236. 236 Chapter 236
  237. 237 Chapter 237
  238. 238 Chapter 238
  239. 239 Chapter 239
  240. 240 Chapter 240
  241. 241 Chapter 241
  242. 242 Chapter 242
  243. 243 Chapter 243
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});