Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 4

Chapter 4

Gidan Aro Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

dan tun tana k’arama ake mata lak’abi da Sady pretty a layinsu.. Tinda ta soma zama budurwa Uwani mahafiyarta da suke kira da Umma ta maida ita hanyar samun kud’inta.. Tuni Umma ta hure ma Sadiya kunne cewa ta dinga karb’o masu kud’i hannun samaruka, hakan yasa Sadiya bata raina samari hardai zata samu ta tatsesa ta rariki rabonta.. Kowa a unguwar yayi shaida ma Sady pretty da Ummarta indai akan tara samari barkatai ne da amsan abin hannunsu.. Babu yanda Malam Ibrahim mahaifin Sadiya da suke kirada Abba baiyi ba wajen ganin ya karkatar da Uwani da kuma mummunan d’abi’ar data d’aura d’iyarsu amma abu yaci tura.. Tsaf Uwani take tsefe masa ruwan bala’i tace bazata zauna tanaji tana gani d’iyarta ta k’are a auren matsiyaci ba kaman yanda ita ta k’are.. A haka har Sadiya ta sami gurbin karatu a Jami’ar babban birnin Tarayya.. Idanun Sadiya sun kuma bud’ewa yanda Ta soma gogayya da manyan ‘yanmata masu ji da kansu da kuma yaran masu hannu da shuni.. Tuni Sadiya Ta kumaji Lallai batada miji sai mai Kud’i ko d’an mai kud’i musamman ganin yanda daga shigarta samaruka sukai mata chaa sabida kyaun halitta da Allah yayi mata.. Idan tayi wanka ta shiga makaranta sai ka rantse d’iyar wani hamshak’i ne, daga nan duk wasu situru da abubuwan more rayuwa da take amfani dasu maza Ke bata su.. Daidai da registration da kud’in samari tayi.. Hoto kuwa idan zatayi posting a social media saidai ta tafi can layin bayansu gidan su wata k’awarta Sabeera a nan take hoto dashike mahaifin Sabeera yanada d’an rufin asiri dan babban d’an canji ne cikin Abuja amma gidansa na nan Suleja.. Gida mai d’an karan kyau ya cancad’a.. Kullum Sady pretty tana gidansu Sabeera dan dama tare suka sami gurbin karatu a nan Jami’ar Abuja, course d’aya suke tare suke tafiya tare suke dawowa, a motar gidansu Sabeera ake kaisu a d’auko su wasu sunyi zaton ma ‘yan gida d’aya ne wasu kuma sukanyi zaton Sady ce d’iyar mai Kud’i Sabeera ce ‘yar k’wak’warta.. Bugu da k’ari Sabeera irin ‘yanmatan nan ne da abun hannun iyayensu bai rufe masu ido ba, Sam abun duniya bai d’ad’areta ba kaman k’awarta Sady pretty.. Sady sam bata bari k’awaye suzo gidansu saidai Su had’e a gidansu Sabeera.. A haka Sabeera Ta zamto Aminiyar Sady, sau tari Sabeera takanyi nasiha ma Sady kan irin rayuwar data d’aukar ma kanta amma ko a jikinta takan ce lokacinta gwara taci duniyarta da tsinke.. Bazata bari kyaun da Allah yayi mata ya zamto a wofi ba tinda basu da kud’i zata iya amfani da kyaun da Allah ya bata ta sama masu rayuwa mai inganci itada iyayenta.. Duk wasu kayan more rayuwa da Sady zata kawo gidan Abba baya amfani dasu bai kuma fasa masu nasiha ba musamman ga Uwani mahaifiyar Sadiya.. Ita kam Sadiya ya mata nasihar ya mata fad’an har duka yasha mata amma babu abinda ya canza dan Tuni mahaifiyarta ta hure mata kunne.. K’arshe Umma ce masa tai idan dai bazai bar mata d’iya ta sakata ta wala ba toh wllhi zata kwashe yaran ta tafi taredasu kuma bazai sake ganinsu ba Eritrea zasu koma da shike dama Mahaifiyar Sady ‘yar asalin k’asar Eritrea ce, haka nan take kyakkyawa kaman mutanen k’asar Eritrea masu kusanci da Ethiopia dan a wajenta Sady ta samo tsantsan kyaun halitta da Allah yayi mata, saidai Ita Sady har ta d’ara mahaifiyar tata. Sosai Malam Ibrahim ya samu matsala da Umma akan Barin Sadiya da tai sakaka tana Yawo dan har Dattijan unguwa sun gaji sun soma masa magana, yayi dik yanda zaiyi ya hana hakan abu yaci tura..K’arshe dai shine yace saidai Sady ta fiddo da miji a mata aure kafin ta k’arasa shekararta ta farko a jami’a.. Ana haka ta had’u da wani saurayi mai suna Sagir a Yanargizo.. Nan da nan Sagir ya samu gurbi mai girma a zuciyar Sady dan sosai yake mata b’arin kud’i kuma yace da aure yake nemanta.. Sady ta gama sakankacewa ta yarda ta amince Sagir masoyinta ne Tuni tace masa ya turo ayi maganar aurensu dan Dama Abbanta ya saka mata takunkumi.. Nan Sagir yake sanar da ita cewa iyayensa US suke basa zama a Nigeria.. Shima abinda ya kawosa zuwa yayi dan ya nemi mata ‘yar k’asar Nigeria ya aura ya d’auketa su koma can US suci gaba da zama.. Haba nan fah Sady da Umma suka kuma susucewa akan Sagir.. Ya turo masu wani mutumi guda d’aya a matsayin Uncle d’insa akai maganar aure.. Sagir yace kar suji komai shi zaiyi komai na aure, nan suka kuma jin dad’i.. Nan da nan zance ya d’auka Sady zata auri d’an gidan k’usa bama cikin Abuja suke zama ba cen k’asar Amurka suke da zama shida iyayensa neman macen aure ya dawo dashi gida Nigeria, iyayensa zasu Zo da zaran ya samu mata an soma shagulgulan biki.. Hakan yasa Uwani cin alwashin yin Bikin kece raini ga Sadiyarta, Ta shiga ciwo bashi dan tayi Bikin kece raini, Bikin yaran masu hannu da shuni Bikin nunuwa a shafukan sada zumunta na yanar gizo.. Ana biki kwatsam aka nemi ango aka rasa har rana mai kaman Ta yau basu san abinda ya faru da ango ba.. Ga wayar salulansa ta dena shiga.. Tun Sady na damuwa har dai Umma tace ta daina damuwa k’ila America ya koma dan ya taho da iyayensa tinda an soma shagulgulan biki.. Sabeera ma cewa tayi k’ila US d’in ya tafi kuma ba lallai wayarsa Ta shiga ba.. Hankalin Sady sosai ya tashi, taci kuka tana fad’in Maiyasa bazai kirata ba da zaran ya saka layinsa na k’asar Amurka, Sabeera tace k’ila surprise yake son mata.. Abu kaman wasa babu Sagir babu dalilinsa har zuwa ranan d’aurin aure da aka rasa ango aka rasa mai karb’awa ango aure.. Toh daga nan ne fah Umma da Sadiya suka fara shakku da yinin wane irin mutumi suka jajib’o... Umma Ta nusa tana duban Abba da har ya ida alwalansa yana d’auraye slippers d’insa da sauran ruwan butar har lokacin karan goge bakinsa na cikin bakinsa.. “Abban Sadiya yanzu bazakace komai ba.. Kana jin yanda ake shigo gidan nan sahu sahu ana d’aga min hankali sai na fidda kud’ad’en dana ciwo bashi..” Sai sann ya d’ago ya dubeta “Toh ki biyasu kud’insu mana sai su daina miki sintiri a gida..” Ya fad’i yana k’ok’arin mik’ewa. Ta k’walalo idanu waje “Ina zan iya kashin tulin kud’ad’en nan Abban Sadiya..?” “Aw dama Kinsan Bakida hanyar samu Kika ciwosu.. Kan wane dalili.? Dan ki birge mutane..? Ai sai ki jira mak’aryacin da ya yaudareku d’in yazo ya biya miki bashin dan nikam Kinsan Ko kud’in haya na shekara da nake biya idan an had’a bazasu isa ba..” Umma ta dafe fuskarta da hannu tana salallami tana furta “Oh ni Uwani na shiga uku, Sadiya kin d’ebo mana ruwan dafa kanmu..” Tana jiyo muryar mijinta na kiran Ashiru da Habib suzo su shige masallaci... Umma ta nufi d’aki yanda Sadiya Ke kwance tana aikin abu guda.. “Ki tashi ki daina wannan koke koken mu soma tunanin yanda zamu samo mafita.” Umma Ta fad’i tana mai zama gefen katifar da Sadiya Ke duk’unk’une tana zuban hawaye, sautin

Table of Contents

Chapters

243 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
  170. 170 Chapter 170
  171. 171 Chapter 171
  172. 172 Chapter 172
  173. 173 Chapter 173
  174. 174 Chapter 174
  175. 175 Chapter 175
  176. 176 Chapter 176
  177. 177 Chapter 177
  178. 178 Chapter 178
  179. 179 Chapter 179
  180. 180 Chapter 180
  181. 181 Chapter 181
  182. 182 Chapter 182
  183. 183 Chapter 183
  184. 184 Chapter 184
  185. 185 Chapter 185
  186. 186 Chapter 186
  187. 187 Chapter 187
  188. 188 Chapter 188
  189. 189 Chapter 189
  190. 190 Chapter 190
  191. 191 Chapter 191
  192. 192 Chapter 192
  193. 193 Chapter 193
  194. 194 Chapter 194
  195. 195 Chapter 195
  196. 196 Chapter 196
  197. 197 Chapter 197
  198. 198 Chapter 198
  199. 199 Chapter 199
  200. 200 Chapter 200
  201. 201 Chapter 201
  202. 202 Chapter 202
  203. 203 Chapter 203
  204. 204 Chapter 204
  205. 205 Chapter 205
  206. 206 Chapter 206
  207. 207 Chapter 207
  208. 208 Chapter 208
  209. 209 Chapter 209
  210. 210 Chapter 210
  211. 211 Chapter 211
  212. 212 Chapter 212
  213. 213 Chapter 213
  214. 214 Chapter 214
  215. 215 Chapter 215
  216. 216 Chapter 216
  217. 217 Chapter 217
  218. 218 Chapter 218
  219. 219 Chapter 219
  220. 220 Chapter 220
  221. 221 Chapter 221
  222. 222 Chapter 222
  223. 223 Chapter 223
  224. 224 Chapter 224
  225. 225 Chapter 225
  226. 226 Chapter 226
  227. 227 Chapter 227
  228. 228 Chapter 228
  229. 229 Chapter 229
  230. 230 Chapter 230
  231. 231 Chapter 231
  232. 232 Chapter 232
  233. 233 Chapter 233
  234. 234 Chapter 234
  235. 235 Chapter 235
  236. 236 Chapter 236
  237. 237 Chapter 237
  238. 238 Chapter 238
  239. 239 Chapter 239
  240. 240 Chapter 240
  241. 241 Chapter 241
  242. 242 Chapter 242
  243. 243 Chapter 243
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});