Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 231

Chapter 231

Gidan Aro Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Aleeyou...✍🏽* A haka mutumin yake k’arasowa cikin parlorn Sallama saman bakinsa. Muryar mutumin Baida banbanci dana mahaifinsu musamman kafin girma ya riski mahaifinsu. Uncle Salman ne ya iya samun zarafin k’arasawa ya mik’a masa hannu sukai masabaha Daddy kam mamaki ya kasa sakinsa ganin fuskar Mahaifinsa tsaye gabansa. Take mutumin ya soma gaida mutanen dake wajen, Mu’azzam ya k’araso Shima sukai masabaha yana hango kamannin Kakansa a tareda mutumin. “Jauro..!” Inne ta furta tana dubansa lokaci guda tana nunasa da hannunta dake matuk’ar rawa. Mutumin ya dubeta Sai yai murmushi ya girgiza kai “Sunana Ramadan ba Jauro ba..” Ya d’anyi fasali kafin yaci gaba da fad’in “Allah yasa nan ne gidan Alhaji Marwan Gamji..?” Sai sann Daddy ya samu zarafin jinjina masa kai yana mai nuna masa wajen zama “Bismillah.. Ga wajen zama.. zauna ni ne Marwan Gamji..” Kafin ya kaiga zama sai ganin Inne sukai ta duk’o gaban mutumin tana kuka tana fad’in “Ka yafeni.. Ka yafeni.. Wllhi kai jikinshi ne.. Wllhi kai d’ansa ne.. Fuskar nan tasa ce.. Dan Allah ka yafeni Bawan Allah ni ce na rabaka da mahaifinka.. Na tabbata kaine d’an Harira da Ta fice Ta tafi da cikinka..” Gaba d’aya jikkunansu sukai sanyi ganin abinda Ke faruwa. Cikin tsananin sanyin jiki mutumin ya kamo Inne yana fad’in “Dan Allah ki daina.. Kar ki duk’a gabana.. Nida mahaifiyata mun yafeki..” Yai fasali sanda shima ya duk’a gabanta. Lokaci guda ya d’ago yana dubansu “Tabbas ni d’in d’aya ne daga cikinku amma banzo nan domin na amsa sunan ahalinku ba.. Nazo nan ne domin na tafi da d’iyata wacce aka tabbatar min tana nan a nan..” Da tsananin mamaki suke dubansa. Daddy ya girgiza kai yace “D’iyarka kuma..? A nan gidan..?” Mutumin ya jinjina kai yace “K’warai d’iyata Jiddah..!” Ganin basu gane ba sai kallon kallo suke ya sanyasa sakin murmushi kafin yace “D’iyata Ajidde wacce Kyallu ta rabani da ita..” Sai snn Aunty Nuratu ta girgiza kai tace “Ajidde.. Ta ya ka zamto mahaifin Ajidde..?!” Ya jinjina kansa kafin ya soma fad’in “K’warai Ajidde d’iyata ce wacce Kyallu ta rabani da ita da kuma mahaifiyarta..” Mamaki ya cika illahirin mutanen dake parlorn. Ciki harda Mommy dake duk’e nan wajen wacce ake shirin tafiya da ita station. Mu’azzam ya shiga nanata sunan Ajidde cikin kansa dan yama rasa wacece ma Ajidden.. Kai wann wani irin Al’amari ne daga wann sai wancan. Abubuwan al’ajabi dai bai k’arewa a wann ahali nasu. Wajen zama Daddy ya nuna masa kafin ya mik’e ya zauna. Kowa ya zuba masa idanu alamun ana jira aji yanda al’amarin ya kasance. Saida yai gyaran murya wajen ya kuma yin tsit kafin ya soma fad’in “Da farko dai sunana Ramadan.. Mahaifiyata mai suna Harira ta haifeni a wani gari dake can gabacin jihar Kaduna. Tinda ta haifeni sai ta tafi ta barni tareda mutanen da Ta zauna wajensu na d’an lokaci. Akai sa’a mutanen masu dattako ne da sanin ya kamata.. Koda aka wayi gari mahaifiyata ta tafi ta barni sai suka kula dani suka rik’eni amana har na kawo girma.. Tinda na taso sai kowa ya hanani aure a garin sabida a cewarsu babu wanda yasan asali na.. Mahaifiyata yada zango kawai tai ta haifeni ta k’ara gaba. Hakan yasa Iyayen rik’ona suka bani auren d’iyarsu wacce Ita kad’aice d’iyarsu mace sauran maza ne. Bayan na auri Hauwa muna zaune Ina tab’a kasuwanci na dan dama tinda na taso nakeda zafin nema da buga can buga nan.. Muna nan a haka muna zaune da Hauwa Allah bai bamu haihuwa ba tsawon shekaru.. A haka dai har na d’auki Hauwa tare dani muka taho cirani yanda muka yada zango a wani gari mai Sunana Fufore can jihar Adamawa. Tinda nazo garin naji hankalina ya kwanta a garin.. Naji Ina matuk’ar k’aunar zaman garin ba tareda nasan cewa wann garin shine Tushena da asalina ba. Muka had’u da wata mata a kasuwa mai tallan magani mai suna Kyallu.. Kyallu sai ta bani masauk’i Nida iyalina.. Ashe tinda Kyallu ta k’yalla idanu akaina sai ta apka soyayya na.. wann dalili ma yasa ta bamu masauk’i.. Muna zaune nida matata Hauwa a nan gidan Kyallu mai warka warka tamkar dai muna a GIDAN ARO. Kyallu tace zata bawa Hauwa maganin haihuwa tinda ta fuskanci bata haihuwa, sai muka nuna rashin amincewarmu daga ni har Hauwa tinda munsan haihuwa abu ne wanda Allah Ke baiwa wanda yaso a lokacin da yaso. Kyallu dai bata janye kudirinta na cewa zata bamu magani ba, dan muna ganin masu amsar magani suna shiga da fice a gidan Kyallu.. A haka ta dinga hure wa Hauwa kunne ba tareda munsan cewa Hauwa na d’auke da juna biyu ba ma ashe.. Hauwa ta soma amsar tayin maganin kyallu a b’oye ba tareda tasan cewa tuni tanada juna biyun ba.. Koda na fahimci tana amsar maganin Kyallu raina Sai ya b’aci nace da ita zamu tattara mu tafi.. Kyallu taita magiya tace na tsaya na gani idan maganinta baiyi aiki ba Ta yarda na d’auki matata na tafi.. Hauwa ma ta nuna damuwarta na cewa saidai mu tsaya.. Nan kuwa Rahmatu ta fara nuna alamomin masu juna biyu.. Kyallu tace maganinta ne ya soma aiki.. Nace atafau ba maganinta bane domin kuwa ita bata isa ta saka ko ta hana ba.. Iko ne na Allah. Sann idan ma maganin nata yayi aiki ta sani ba yinta bane Allah zai iya nuna k’udararsa da isarsa ya sanya maganin nata yayi aiki domin yaga zatai imani ko zata tab’e. A haka na dinga k’ok’arin nusar da Kyallu tauhidi amma sai tai k’ememe tak’i d’aukan wa’azin da nake mata. Ni kuma na kasa barin garin na kasa d’auke matata mu tafi ba tareda nasan dalili ba.. Sai na alak’anta hakan da cewa Watak’ila Allah ya nufi nazo garin ne domin na had’u da wann mushirikar matar mai suna Kyallu nai mata wa’azi ko zata wa’aztu.. Tafiya yayi tafiya har lokacin haihuwar Hauwa yai wanda zai kuma tabbatarwa Rahamatu tanada juna biyu muka taho garin ba maganin Kyallu bane yai aiki, domin kuwa bamu cika watanni tara a garin ba Ta soma nak’uda.. Kyallu ita ta amshi haihuwar Hauwa yanda muka rasa Hauwa a wajen haihuwa. Ta haifo d’iyarta mai kama da ita na maida mata sunan Hauwa (Jiddah).. Nayi kukan rashin Hauwa dan bansan mai zanje na sanar da iyayen Hauwa ba.. Na yanke shawarin d’aukan d’iyata Jidda na tafi da ita, amma sai Kyallu ta dage saidai na zauna na aureta mu raini jidda tare.. Ni kuma Sai nak’i aminta da hakan.. Kyallu sai ta rik’e Jidda tace bazata bani ba.. A ranan taita min kururuwa ta had’a mun mutane tace ni b’arawo ne zan sace mata d’iya.. Inaji ina gani Kyallu tasa aka mun korar wulak’anci a garin Ta kuma goye d’iyata a bayanta Ta hanani d’iyata ta bini da sharri cewa d’iyarta ce nida ita munyi aure zan d’auketa ne na gudu na shiga duniya da ita. Kuma wani ikon Allah ban iya aiwatar da komai akai ba bansan wani k’ullin Kyallu tai akaina da d’iyata ba. Koda na dawo gida na sanar da iyayen Hauwa cewa mun rasa Hauwa sai sukai tawakkali amma na kasa sanar dasu abinda ya samu d’iyarmu da Hauwa

Table of Contents

Chapters

243 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
  170. 170 Chapter 170
  171. 171 Chapter 171
  172. 172 Chapter 172
  173. 173 Chapter 173
  174. 174 Chapter 174
  175. 175 Chapter 175
  176. 176 Chapter 176
  177. 177 Chapter 177
  178. 178 Chapter 178
  179. 179 Chapter 179
  180. 180 Chapter 180
  181. 181 Chapter 181
  182. 182 Chapter 182
  183. 183 Chapter 183
  184. 184 Chapter 184
  185. 185 Chapter 185
  186. 186 Chapter 186
  187. 187 Chapter 187
  188. 188 Chapter 188
  189. 189 Chapter 189
  190. 190 Chapter 190
  191. 191 Chapter 191
  192. 192 Chapter 192
  193. 193 Chapter 193
  194. 194 Chapter 194
  195. 195 Chapter 195
  196. 196 Chapter 196
  197. 197 Chapter 197
  198. 198 Chapter 198
  199. 199 Chapter 199
  200. 200 Chapter 200
  201. 201 Chapter 201
  202. 202 Chapter 202
  203. 203 Chapter 203
  204. 204 Chapter 204
  205. 205 Chapter 205
  206. 206 Chapter 206
  207. 207 Chapter 207
  208. 208 Chapter 208
  209. 209 Chapter 209
  210. 210 Chapter 210
  211. 211 Chapter 211
  212. 212 Chapter 212
  213. 213 Chapter 213
  214. 214 Chapter 214
  215. 215 Chapter 215
  216. 216 Chapter 216
  217. 217 Chapter 217
  218. 218 Chapter 218
  219. 219 Chapter 219
  220. 220 Chapter 220
  221. 221 Chapter 221
  222. 222 Chapter 222
  223. 223 Chapter 223
  224. 224 Chapter 224
  225. 225 Chapter 225
  226. 226 Chapter 226
  227. 227 Chapter 227
  228. 228 Chapter 228
  229. 229 Chapter 229
  230. 230 Chapter 230
  231. 231 Chapter 231
  232. 232 Chapter 232
  233. 233 Chapter 233
  234. 234 Chapter 234
  235. 235 Chapter 235
  236. 236 Chapter 236
  237. 237 Chapter 237
  238. 238 Chapter 238
  239. 239 Chapter 239
  240. 240 Chapter 240
  241. 241 Chapter 241
  242. 242 Chapter 242
  243. 243 Chapter 243
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});