Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 40

Chapter 40

Gidan Aro Book 1 Complete Hausa Novel 1,198 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

neman alfarma Gimbiyata, abinda kike so kawai zaki fad’a ayi.” Sadiya tace “Kar ka biya Tabawa har sai randa akazo d’aura aurenmu domin akwai rayuwa akwai mutuwa bamu San mai zai faru kafin ranan ba..” Ya murmusa yace “Idan dan wannan ne banida matsala. Yanda kikace haka za’ayi Amaryata.. Wllhi na k’agu ki zamto tawa..” Katsesa tai da fad’in “Ni zan shige gida..” “A’a tsaya mana..” Yai maganar yana zaro kud’ad’e cikin aljihunsa. Saurin girgiza kai Sadiya tai tace “Bazan karb’i komai daga hannunka ba.. Na gode..” Bata tsaya sauraron sa ba tasa kai ta shige cikin gida. Yabi bayanta da kallo zuciyarsa fari k’al, kad’a Kai yai yace a fili “Bari dai naita lallab’a ki har ki shigo...” Yana ida fad’in haka ya gyad’a Kai yana mai kuma Washe baki ya shige. ** Washe gari sassafe Tabawa tai kiran Asabe mai kayan Koli. Tabawa ta k’irgo kud’ad’e cikin wanda Alhaji Isyaku ya bata, Ta mik’awa Asabe Mai kayan Koli tace “Kina jina dik abinda na sanar dake haka zaki sanar da matarsa.. Asabe koda wasa kar ki ce ni na sanar dake..” Asabe Ta jinjina kai tana tura kud’in cikin posar ta. “Haba Hajiya Tabai, indai dan wannan ne ai bakida matsala, da Asabe fah kike zancen..” Tabawa ta murmusa cikeda jin dad’i tace “Yauwa tawan.. Idan har hak’ata ta cimma ruwa zan k’ara miki wani abu..” Asabe Ta Washe baki cikeda farin ciki.. Tuni ta aza kayanta na Koli aka ta nufi layin gidan Alhaji Isyaku. Tabawa tabi bayanta da kallo zuciyarta fari k’al. A fili take furta “Alhaji Isyaku kenan ai wllhi bazan bari ka auri yarinyar nan ba, auren nan saidai ayi dani Koda zaka biya masu bashin amma bakada mata sai ni Tabawa. Zan d’aga masu hankali dan ka biya masu bashi sannan zan sa matarka da d’iyarka su d’aga masu hankali suk’i amincewa da buk’atarka bayan ka biya masu bashin..” Tana ida fad’in haka ta bushe da muguwar dariya kafin ta shige gida. ** Maman Sabeera na zaune parlor tana kallon shirin good morning Nigeria da ake nunawa da sanyin safiya a tashar NTA Asabe mai kayan Koli tai sallama. Iyatu mai masu aikatau ce ta amsa mata sallamar tace ta jira ta shiga ta tambayi Hajiya idan zata sayi wani abin. Asabe tace “Dakata ba saye da sayarwa ya kawoni na ba.. Alhaji na gida Ko ya fice..?” Iyatu tai jim kafin tace “Ai Jiya Alhaji bai dawo gida ba inaga wajen aiki ya kwana..” Asabe ta zaro ido waje tace “Bai kwana gida ba..? Ikon Allah Toh ki shiga kice mata magana nazo mata dashi mahimmiya kan maigidanta.” Iyatu ta dubeta da mamaki amma sai ta jinjina kai tace “Shikenan.” Lokaci guda ta shige ta nufo parlor ta tadda Maman Sabeera ta sanar da ita abinda Asabe mai Kayan Koli ta fad’a mata. Mamaki ya cika Maman Sabeera jin Wai magana Asabe tazo mata dashi kan mijinta. Ta nusa tana tinani kafin taceda Iyatu “Kice mata Ta shigo.” Iyatu ta jinjina kai kafin ta fice yin iso ma Asabe. Jim kad’an Asabe ta shigo d’aikeda kayan Kolinta, ta nemi waje daga k’asa ta zauna tana gaida Maman Sabeera. Maman Sabeera Ta dubeta da mamaki tace “Asabe kikace yau ba talla kikazo ba.. Toh wani magana ne ya kawo ki kan maigidana.?” Asabe Ta d’an Tab’e baki tana ‘yan waige waige tace “Hmm ai Hajiya abinda nazo dashi yau yafi k’arfin talla.. Amma Hajiya jiya Kinsan yanda mijinki ya kwana..?” Da tsananin mamaki Maman Sabeera ke dubanta ganin basu saba irin wannan batu ba, iyakaci ta shigo da kayan kolinta ta tallata ta fice. Amma yau Asabe tazo mata da batu mai girma. Girgiza kai kad’an Maman Sabeera tai “Ban.. Fahimceki ba Asabe.. Mai kike nufi..?” Asabe ta kuma gyara zama tana duban Maman Sabeera “Hajiya wllhi wllhi abinda zan fad’a miki Sai ya firgitaki.. Idan dai har bakisan yanda mijinki ya kwana jiya ba kuma bakisan da wa ya kwana ba ni zan sanar dake dan na sani..” Zuciyar Maman Sabeera yaci gaba da bugawa cikin sauri, mijinta ya saba kwana cikin Abuja idan dare ya masa sabida tsananin holdup da cinkoson Abuja yakan sa wataran ya kwana ga yanda k’asar Ta koma babu tsaro, wataran yakan ce aiki ya rik’esa zai kwana cikin Abuja da safe ya dawo. Amma koda wasa bata tab’a saka ma ranta cewa mijinta na ha’intarta ba tuni ta kyautata masa zato tinda ma kafin ya kwana cikin Abujan Sai ya kirata ya sanar da Ita cewa zai kwana aiki ya rik’esa gudun Karma zargi ko abu mai kama da haka ya shiga tsakaninsu. Cikin rashin yarda da batun Asabe Ta mik’e tana nuna ma Asabe k’ofa “Kinga Asabe tashi kawai ki fice.. Kafin ranmu gaba d’aya ya b’aci.. Tashi ki fice min a gida ni bana shiga gulma da gutsiri tsomen unguwar nan.. Tashi ki fice min a gida kuma kar ki sake dawowa idan da irin batun nan zaki Zo..” Asabe Ta murmusa tace “Hajiya wllhi Allah na rantse miki da Allah daren jiya mijinki na unguwar nan kuma nasan da wa yake tare.. Ni ganau ce ba jiyau ba, na gansa da yarinyar nan Sadiya kuma yau kusan kwanaki uku kenan yana zarya k’ofar gidansu.. Ina mai tabbatar miki d’aukanta yayi suka fice suka kwana tare.. Ai dai Kinsan wacece Sadiya a unguwar nan Sadiya Sady Pretty da tai k’aurin suna wajen rab’an maza masu abin duniya.. Toh ta fad’o kan mijinki zata k’wak’wale abin hannunsa.. Dan wllhi jiya tare na gansu kaman zai mata sijadda dan biyayya..” Bibbiyu Maman Sabeera ta soma gani, hazo hazo da wani irin duhuwa ne suka gifta k’wayar idanunta. A yayinda Sabeera da fitowarta kenan daga kitchen rik’eda mug dik taji tattaunawarsu a kunnuwanta.. Wani irin k’ara ta saki had’ida sake mug d’in dake hannunta ya watse saman tiles.. SameenaAleeyou📚 *GIDAN ARO* *18* *©️Sameena Aleeyou...✍🏽* Da kuka Sabeera ta k’araso gabansu tana fad’in “A’a badai Babana ba.. Badai k’awata Sadiya ba.. Mama kar ki yarda da maganar wannan matar I’m sure k’arya take.. Ki tashi.. Tashi ki fice mana daga gida..!” Tai maganar tana k’ok’arin finciko Asabe dake duk’e wajen ta zuba masu ta mujiya. Maman Sabeera kam tama kasa tantance abinda ke faruwa. Kaman daga wani duniyar take sinkayo kukan Sabeera da maganganunta. Asabe ta mik’e tana fad’in “Idan k’arya nake maku ku tare mutanen lungunsu ku tambayesu ko kuma kuje da kanku dan ance zuwa dakai yafi sak’o. Nidai na gama nawa tinda sanar daku.. Ya rage naku ku yarda ko kar ku yarda. Allah bamu alheri.” Tana ida fad’in haka ta mik’e ta aza bahon kayan Kolinta aka Ta nufo waje, tuni Ta cika ma rigarta iska aka bar Sabeera da Mamanta babu mai iya ba ma wani hak’uri. Cikin muryar kuka Sabeera ke duban mahaifiyarta tana fad’in “Mama k’arya take kar ki yarda da ita.. Wllhi nayi imani Sadiya bazata tab’a aikata haka ba.. Nasan Sadiya nasan halinta wllhi sharri ne kawai irinta mutanen unguwar nan.. Mama dan Allah Kema kice min baki yarda ba..!” Maman Sabeera bata iya furta koda kalma ba sai hawaye dake zarya saman k’uncinta. Cikin sauri ta mik’e ta nufi d’aki tana jin kukan da gaske na zuwa mata.

Table of Contents

Chapters

243 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
  170. 170 Chapter 170
  171. 171 Chapter 171
  172. 172 Chapter 172
  173. 173 Chapter 173
  174. 174 Chapter 174
  175. 175 Chapter 175
  176. 176 Chapter 176
  177. 177 Chapter 177
  178. 178 Chapter 178
  179. 179 Chapter 179
  180. 180 Chapter 180
  181. 181 Chapter 181
  182. 182 Chapter 182
  183. 183 Chapter 183
  184. 184 Chapter 184
  185. 185 Chapter 185
  186. 186 Chapter 186
  187. 187 Chapter 187
  188. 188 Chapter 188
  189. 189 Chapter 189
  190. 190 Chapter 190
  191. 191 Chapter 191
  192. 192 Chapter 192
  193. 193 Chapter 193
  194. 194 Chapter 194
  195. 195 Chapter 195
  196. 196 Chapter 196
  197. 197 Chapter 197
  198. 198 Chapter 198
  199. 199 Chapter 199
  200. 200 Chapter 200
  201. 201 Chapter 201
  202. 202 Chapter 202
  203. 203 Chapter 203
  204. 204 Chapter 204
  205. 205 Chapter 205
  206. 206 Chapter 206
  207. 207 Chapter 207
  208. 208 Chapter 208
  209. 209 Chapter 209
  210. 210 Chapter 210
  211. 211 Chapter 211
  212. 212 Chapter 212
  213. 213 Chapter 213
  214. 214 Chapter 214
  215. 215 Chapter 215
  216. 216 Chapter 216
  217. 217 Chapter 217
  218. 218 Chapter 218
  219. 219 Chapter 219
  220. 220 Chapter 220
  221. 221 Chapter 221
  222. 222 Chapter 222
  223. 223 Chapter 223
  224. 224 Chapter 224
  225. 225 Chapter 225
  226. 226 Chapter 226
  227. 227 Chapter 227
  228. 228 Chapter 228
  229. 229 Chapter 229
  230. 230 Chapter 230
  231. 231 Chapter 231
  232. 232 Chapter 232
  233. 233 Chapter 233
  234. 234 Chapter 234
  235. 235 Chapter 235
  236. 236 Chapter 236
  237. 237 Chapter 237
  238. 238 Chapter 238
  239. 239 Chapter 239
  240. 240 Chapter 240
  241. 241 Chapter 241
  242. 242 Chapter 242
  243. 243 Chapter 243
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});