Chapter 218
Chapter 218
D’an mahaifina.. Mahaifina ya rasu bai sani ba ko ta haihu ko bata haihu ba.. Inne kan wane dalili.. Dukiya.? Wann gadon da mahaifina zai bari.. Kan haka ne kika cutar da wata kika hanata zaman gidanki..?!” Kuka yaci k’arfin Sa yayinda Inne ma ke kuka.. Kuka take tana girgiza masa kai tana fad’in “Sharrin zuciya ne.. Ka yafe mun D’ana wllhi nayi nadama kuma nayi danasani mai tarin yawa.. Kuma nayi alk’awarin sadaukar da sauran rayuwana ga tuba da bautan Allah had’ida hidimta ma Al’umma... Bansan yanda zan samu Harira ba wllhi da na bita na rok’i yafiyarta..” Girgiza kai yake yana duban Inne hawaye na gangaro masa “Kin aikata mugun abu Inne.. Idan akan dukiyar mahaifina kika aikata haka ki sani bana buk’atar wann dukiyar.. Zanyi sadaukarwa da wann dukiyar... Sann zan d’auki iyalaina muyi nesa da nan Inne.. Bazan iya ba.. Bazan iya ci gaba da zama a nan ba..!” Yana maganan hawaye na gangaro masa yana girgiza kai. Inne na hawaye Ta kamo hannayensa “Kai hak’uri d’ana kar ka tafi ka barni.. Dan Allah ka zauna.” Ya girgiza mata kai kad’an kafin yace “Na riga na tsara hakan Inne.. Zanyita rok’ar miki Ubangiji ya yafe miki.. Kinsan Maiyasa..? Sabida ke mahaifiyata ce.. Amma zan d’auke iyalaina daga nan zamu tafi da nisa.. Allah ya yafe miki Inne..!” Yana mik’ewa ya fice ya bar Inne wajen tana kuka had’ida nadaman abinda Ta aikata a baya. Zai wuce company ya had’uda Marwan, suka jera suna tattaunawa. Marwan ya kula da yanda jikin D’anuwan nasa yake a mace, kaman dai wani abu na damunsa. Ya tsaresa da tambayar meke damunsa. Abubakar ya murmusa kafin ya dafa kafad’an Marwan yace “D’anuwana nasan dik cikinmu ka fimu zuciya mai taushi.. Zanso na bar maka amanan ahalinmu a bayana.. Ka kular mana da ahalinmu kar ka bari ahalinmu ya rushe..” Marwan ya murmusa kad’an yana duban D’anuwan nasa kafin ya girgiza kai yace “Kana nan Hamma kuma zamu kula da bayan Baffah tare.. Ka tuna kullum wasiyan Baffah a garemu shine mu so junanmu mu zama tsintsiya mad’auri d’aya sann mu kula da kasuwancin Ahalinmu..” Abubakar ya murmusa yana hango Musaddiq takwaransa da kuma Mu’azzam da suketa shawagi suna wasan Cop and bad guys a cikin fad’in Gidan gonan.. Lokaci guda ya saki murmushi kafin yace “Mu’azzam D’ansanda yake mafarkin zama Ina fata Takwarana ya gaji mahaifinsa wajen aiki tuk’uru kaman dai yanda kake Marwan ya k’arashe yana duban Musaddiq murmushi saman fuskarsa. Lokaci guda ya k’arada “Allah ya masu albarka” Marwan ya murmusa kad’an kafin yace “Ameen Hamma..” Sai karantar D’anuwan nasa yake yana ganin kaman wani abu ke d’awainiya dashi. Abubakar ya d’an murmusa kafin yace “Zanje Factory yanzu.. Akwai abubuwa da dama da nake so mu tattauna Marwan.. Allah yasa lokaci ya ara mana kansa.” Marwan ya murmusa kafin ya jinjina masa kai kad’an yace “Allah ya kaimu Hamma.. A dawo lafiya..” Har Abubakar yasa kai zai tafi sai kuma ya juyo ya dubi Marwan yace “Idan baka komai anjima ka sameni a company sai mu tattauna..” Marwan ya jinjina kai kad’an yace “Ba matsala zan sameka anjima a company in sha Allah..” Suka sakar ma juna murmushi kafin Abubakar ya dawo da baya ya d’an rungumi D’anuwan nasa.. Su duka biyu suna duban juna cikeda k’auna. Abubuwan da Abubakar yake yanda kasan mai sallama da D’anuwan nasa. Koda yake yai k’udirin zai tattara iyalansa su tafi bayan abinda yaji Inne Ta aikata wa matan mahaifinsu. Bazai iya sanar da D’anuwansa ga abinda ya faru ba sann bazai iya sanar dashi kai tsaye cewa zai tafi da nisa ba sabida yasan irin k’aunan dake tsakaninsa da D’anuwansa. Salman dake tsaye daga can yana hangensu jinjina kai yai yana sakin huci.. Ya jima da sanin ‘Yanuwan basa wani sonsa, waresa suke kansu su biyu a had’e.. Yai k’wafa cikin zuciyarsa kafin ya shige Mota yabi bayan Abubakar da ya nufi Factory. Marwan ciki Gida ya nufa.. A hanyarsa na komawa cikin gida ya hangota.. Zuciyarsa yai wani irin tsinkewa.. Yai tsaye yana hangeta ba tareda yasan ya aikata hakan ba. Tana tsaye kusan wani saniya tana rik’e da d’iyarta Ikram tana shafasa hannun d’iyar nata jikin saniyar murmushi saman fuskarta sai wasa ma Ikram d’in take sunata murmushi gwanin ban sha’awa. Kasa janye idanunsa yai ga wane irin rauni da ya cika idanun nasa.. Ya dinga tina sanda suka tsinceta da yanda ya kwashe sauran kwanakinsa a makaranta yana lissafin yanda zai dawo ya gina soyayyarsa mai tsafta cikin zuciyarta. Tinawa da haramcin abinda yake aikatawa ya sanyasa saurin janye idanunsa ya janye jikinsa ya nufi cikin gida yana istigfar. Hajara dake lab’e akan idanunta komai ya faru.. Taga yanda mijinta yai tsaye yana kallon Nuratu sann ya shige cikin sauri kaman wanda ya tina wani abu.. Zuciyarta ya buga kardai Nuratu ce matar da Ta dasashe hasken Zuciyar mijinta.. Kar dai Itace wann Hasken da yace ta mutu tareda zuciyarsa.. Lallai kuwa idan haka ne ya zama dole Ta d’au mataki.. Ta wuce fuuu ta nufi cikin gida.. Saidai tana shiga ta hangi Marwan saman sallaya hannayensa biyu a sama yana rok’on Allah ya shiga al’amarinsa ya tsare masa zuciyarsa ya kareta daga sharrin shaid’an ya kuma basa ikon cin duk jarabawar da zai jarabcesa dashi.. A addu’o’insa na k’arshe ne Ta tabbata Nuratu dai itace wann matar da tasa Ta rayu da mijinta kaman hoto ko gunki.. Bata zaci matar da Ta kashe hasken fitilar Zuciyar mijinta tana raye ba.. Dama ta d’au alwashin gano wacece wann matar.. Lallai ya zama dole Ta taka ma hakan birki.. Meye abinyi..? Ta tambayi kanta..! Ta soma tinanin neman mafita. Tana ganinsa ya shirya tsaf, kaman ko yaushe babu wani walwala yake sanar da ita zaije Company ya sami D’anuwansa. Ta murmusa tace dashi a dawo lafiya. Sai girgiza k’afa take tana tinanin abin yi har ya fice.. Kafin hutunsu ya k’are a garin ya zama dole Ta fasa komai kowa yaji.. Kowa yasan Marwan son matar D’anuwansa ya hanasa samun natsuwa da nasa iyalin.. Tasan idan Abubakar yaji haka dole ya d’au tsartsauran mataki kan D’anuwan nasa.. Da wann tunanin ta yanke shawarin taje har Factory d’in Ta sanar da Abubakar a gaban Marwan d’in cewa K’aninsa na son matarsa. Allah Sa idan ta fad’I haka Abubakar ya d’auki matarsa suyi nesa yanda babu mai K’ara ganinsu cikinsu. ** A can Factory kuwa Salman ya tasa Abubakar gaba, Ta yanda yake shiga ba Ta nan yake fita ba.. “Ka handame mana dukiya ka hanani sukuni ka hanani girma cikin company..Toh mai kake nufi kenan..?” Tinda ya soma magana Abubakar kai tankasa ba, yanata rubutu cikin wata doguwar Takarda... Har ya gama ya saka hannu ya rufe envelope d’in ya rubuta BAT a saman takardan. Salman ya dubesa ya dubi doguwar takardan kafin yace “Meye kuma wann.. Wane kutungwilar zakai da dukiyar mahaifinmu.?” Murmushi Abubakar ya sakar masa kafin yace “Nawa kason ne a cikin nan..” Salman yace “Ban gane ba..” Murmusawa Abubakar ya kumayi kafin yace “Zan tafi da nisa.. Zan bar maka abinda kake mafarkin samu Wato shugabancin wann company... Ka kwantar da hankalinka Salman.. Kaga dukiyata dake cikin nan a rubuce bana son ko k’wandala.. Hasalima zanyi sadaukarwa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182
- 183 Chapter 183
- 184 Chapter 184
- 185 Chapter 185
- 186 Chapter 186
- 187 Chapter 187
- 188 Chapter 188
- 189 Chapter 189
- 190 Chapter 190
- 191 Chapter 191
- 192 Chapter 192
- 193 Chapter 193
- 194 Chapter 194
- 195 Chapter 195
- 196 Chapter 196
- 197 Chapter 197
- 198 Chapter 198
- 199 Chapter 199
- 200 Chapter 200
- 201 Chapter 201
- 202 Chapter 202
- 203 Chapter 203
- 204 Chapter 204
- 205 Chapter 205
- 206 Chapter 206
- 207 Chapter 207
- 208 Chapter 208
- 209 Chapter 209
- 210 Chapter 210
- 211 Chapter 211
- 212 Chapter 212
- 213 Chapter 213
- 214 Chapter 214
- 215 Chapter 215
- 216 Chapter 216
- 217 Chapter 217
- 218 Chapter 218
- 219 Chapter 219
- 220 Chapter 220
- 221 Chapter 221
- 222 Chapter 222
- 223 Chapter 223
- 224 Chapter 224
- 225 Chapter 225
- 226 Chapter 226
- 227 Chapter 227
- 228 Chapter 228
- 229 Chapter 229
- 230 Chapter 230
- 231 Chapter 231
- 232 Chapter 232
- 233 Chapter 233
- 234 Chapter 234
- 235 Chapter 235
- 236 Chapter 236
- 237 Chapter 237
- 238 Chapter 238
- 239 Chapter 239
- 240 Chapter 240
- 241 Chapter 241
- 242 Chapter 242
- 243 Chapter 243