Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 30

Chapter 30

Gidan Aro Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ba bata gani ba. Yo wani irin aiki ne ma zatayi ta samo mata kud’ad’enta idan ba Sana’ar bin maza data d’aura ‘yarta akai zasuyi Su biyata kud’ad’enta ba.. Wanann magana na Tabawa sosai ya tab’a Zuciyar Umman Sadiya.. Abinda batayi tin k’uruciya ba shine Tabawa take jifanta da munanan kalamai irin haka.. Ya zama dole Ta nemo wa Tabawa kud’ad’enta dan abin ya zama akwai tab’a mutunci da tozarci bazata bari Ta kuma traumatizing yaranta ba bayan tashin hankalin rashin mahaifinsu da suke ciki already.. Hakan yasa Umma yanke shawarin tink’aran Committee na masallacin unguwa ko da akwai irin taimakon da zasu masu su rabu da Tabawa.. Malam Liman ya gyara zama had’ida nusawa kad’an yace “Da farko nasiha zan fara maki da ita.. Ita wannan rayuwar da kuke gani duka ba yawa bace da ita, sannan dik halinda bawa zai tsinci kansa ciki jarabawa ake masa.. Bazai yuwu ace koda Yaushe mun samu abinda muke so ba.. Sannan Ko yatsunmu muka duba ba daidai bane wani yafi wani toh haka Ubangiji ya tsara mana rayuwarmu.. Wani yafika kaima kafi wani.. Kai wani arzikin lafiya ma kawai yake nema dikda d’imbin tarin dukiyar da yake dashi wanda zai iya kashe ko nawa ne domin ya samu wannan lafiyar amma bai samu ba.. Ga dukiyar Allah ya basa amma babu lafiya da zaiji dad’in dukiyar.. Kaikuma idan ka dubi kanka kaga Allah ya huwace maka wannan lafiyan sai kayi tunanin ya gama baka babban arziki.. Har kullum idan zamuke duba rayuwar na sama damu toh fah bazamu tab’a gode ma Allah da tarin ni’imomin da ya mana ba.. Amma idan muka dubi na k’asa damu sai muyi masa godiya da ni’imominsa garemu.. Shi kuma Sai ya k’ara mana domin fad’insa da yace _’Idan kuka gode Mun Ni kuma Zan k’ara maku_.’ “ Umma na matsan k’walla cikin hijabinta take jinjina kai “Haka ne Malam.. Kuma in sha Allahu mun d’auki darasi.. Ina kuma fatan masu halin kwad’ayi irin nawa abinda ya faru dani da d’iyata ya zamto izna garesu..” Kuka ya hanata ci gaba da magana Malam Liman yace “Ki daina kuka in sha Allah Committee na masallaci zatayi iya k’ok’arinta ta had’o abinda za’a iya samu a baku ku rage bashin.. Ubangiji ya dafa mana gaba d’aya..”Ya k’arashe yana mai mik’ewa ya kuma yima Umma ta’aziya kafin ya fice. Sadiya tai tagumi tana duban mahaifiyarta, ga k’annenta dake gefe har lokacin kuka suke. Hawaye suka kuma gangaro mata tana tina mahaifinta da k’alubale na rayuwa da suka fuskanta.. Inama mahaifinta zai dawo gareta da ta kasance irin d’iyar da yake so ta zama.. Amma saidai shi lokaci baya jira, idan ya wuce ya wuce kenan har abada.. Koda Malam Liman yaje ma Committee na masallaci da wannan batu suma sun tausaya ma Sadiya da mahaifiyarta dukda a baya basa k’aunar kasancewarsu a Layin.. Amma saidai kaf kud’ad’en dake asusun masallaci bai kai ko kwatan kud’ad’en da ake bin Umma da Sadiya ba.. Bazasu isa ba balle a biya masu dashi Sabida falalar dake cikin biyan bashi ga musulmi.. Haka Liman ya tara jama’a ya masu wa’azi kan falala da ladar da mutum zai samu idan har ya cire d’anuwansa musulmi daga k’unci na bashin da ake binsa ya biya masa wannan bashi.. Saidai ba’a samu wanda yace zai iya biyan bashin ba.. Ana haka saiga Alhaji Isyaku Dancanji mahaifin Sabeera Aminiyar Sadiya ya shigo, ya nemi ganawa da Malam Liman.. Bayan sun keb’e ne ya dubi Malam Liman yace “Malam naji sanarwan da kake na neman kud’i da yarinyar nan Sadiya da mahaifiyarta suke.. Zan biya masu bashin amma fah da sharad’i.. Liman ya fad’ad’a murmushi yana fad’in “Alhamdulillah.. Masha Allah.. Allah dai ya biyaka da gidan Aljannah Alhaji.. Taimakon da kake a layin nan Allah ya dad’a bud’e maka k’ofofin arziki.. Inaji mecece sharad’in naka..?” Alhaji Isyaku yace “Zan biya masu bashin da ake binsu amma fah saidai idan za’a bani auren ita yarinyar Sadiya..” Liman yai shiru yana dubansa “Alhaji kana nufi Sai za’a baka auren yarinyar ka biya masu bashin..?” “K’warai kuwa Malam Liman yanda dai kaji haka ne.. Ai dama bashin na shagulgulan Bikin yarinyar ne.. Kaga Shagali bai tashi a banza ba Malam Liman shikenan sai a d’aura aure dani..” SameenaAleeyou📚 *GIDAN ARO* *14* *©️Sameena Aleeyou...✍🏽* Da tsananin mamaki Umma take duban Malam Liman “Malam Alhaji Isyaku fah kace.. Shine yace zai biya bashin idan za’a basa auren Sadiya.? Malam Sadiya fah k’awar d’iyarsa ce Aminiyarta ce Wanda sam baya k’aunar tarayyarsu shine zai zago yace yana sonta da aure.. Allah mai iko..” Malam ya nusa kad’an yace “Ni kaina banji dad’in cewa da yayi har sai idan za’a basa auren Sadiya ne zai biya bashin, domin kuwa naso ya biya dan Allah Allah ya basa ladansa toh amma ya kawo sharad’i sharad’i kuma shine a basa auren Sadiya..” Umma ta katse Malam Liman da fad’in “A’a Malam wannan ma bazai tab’a yuwa ba, Ko lokacin da nake ganiyan son kud’ina da abin duniya bazan tab’a bari Sadiya ta auri mutumin nan ba balle yanzu da duniyar da abindake cikinta suka fita kaina.. Yajesa mun gode da niyyan taimako Allah zai kawo mana wani hanyar amma banda auren Alhaji Isyaku..” Liman ya nusa yace “Toh shikenan dama ni ga abinda na Fad’i idan na tuntub’eku zaiji ba’asi.. Allah Ubangiji ya huwace ya kawo wani hanyar..” Umma ta amsa da Ameen Malam Liman yai mata sallama... Ta rapka uban tagumi tana mamakin halin mutanen duniya.. Lallai kaga d’an mutum ka barsa, yanzu dik kushe Sadiya da hanata k’awance da mutumin nan keyi da d’iyarsa ashe idonsa nakan Sadiyar ce.. Ashe zai zago bayan ya rabata da d’iyarsa yace zai aureta.. Oh Lallai duniyar yau Ta zama abinda Ta zama.. Wai mutum bazaiyi taimako dan Allah ba sai idan zai sami wani abu in return.. Taimako dan Allah yayi k’arancin har sai idan kaima zaka sami wani abu. Ta yaya kuwa Allah Bazai barmu da halinmu ba idan har na sama bazai tallafi na k’asa ba.. Kai Allah ka kawo mana sauk’i a wannan duniyar tamu.. Ta k’arashe tinanin nata tana mai sauk’e nannauyan ajiyan zuciya. A d’aki ta iske Sadiya ta gama lallashin Habib yayi bacci dan yaron tinda yaga yanda aka kad’e mahaifinsa akan idonsa Sai ya dinga wani irin firgita idan yana bacci yaita surutai, har sai sunyita masa addu’o’i kafin su samu ya d’anyi baccin.. Umma ta k’ura ma yaran nata idanu cikeda tausayinsu da k’aunarsu, ta k’udiri niyyan da zaran ta gama iddarta zata nemi Sana’a domin ta rufa ma kanta da iyalanta asiri.. Har kullum hannun da yake bayawar yafi hannun da yake karb’a, tayi kuskuren fahimtar rayuwa a baya da tayi tinanin Lallai sai ta hanyar namiji mace zata sami kud’i, yau da ace tanada sana’arta da zai rufa mata asiri da ba sai ta tsaya hangen abin hannun namiji ba balle har taje ta jefa rayuwar d’iyarta a tsaka mai wuya.. Juyowan da Sadiya zatai suka had’a idanu.. Murmushi suka sakar ma juna kafin Sadiya ta gyara ma Habib abin rufuwarsa ta mik’e ta nufo bayan Umma. Yanayin da taga Umman ciki ya tabbatar abubuwa sunci gaba da tafiya babu dad’i, Ta taimaka ma Umman ta zauna da

Table of Contents

Chapters

243 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
  170. 170 Chapter 170
  171. 171 Chapter 171
  172. 172 Chapter 172
  173. 173 Chapter 173
  174. 174 Chapter 174
  175. 175 Chapter 175
  176. 176 Chapter 176
  177. 177 Chapter 177
  178. 178 Chapter 178
  179. 179 Chapter 179
  180. 180 Chapter 180
  181. 181 Chapter 181
  182. 182 Chapter 182
  183. 183 Chapter 183
  184. 184 Chapter 184
  185. 185 Chapter 185
  186. 186 Chapter 186
  187. 187 Chapter 187
  188. 188 Chapter 188
  189. 189 Chapter 189
  190. 190 Chapter 190
  191. 191 Chapter 191
  192. 192 Chapter 192
  193. 193 Chapter 193
  194. 194 Chapter 194
  195. 195 Chapter 195
  196. 196 Chapter 196
  197. 197 Chapter 197
  198. 198 Chapter 198
  199. 199 Chapter 199
  200. 200 Chapter 200
  201. 201 Chapter 201
  202. 202 Chapter 202
  203. 203 Chapter 203
  204. 204 Chapter 204
  205. 205 Chapter 205
  206. 206 Chapter 206
  207. 207 Chapter 207
  208. 208 Chapter 208
  209. 209 Chapter 209
  210. 210 Chapter 210
  211. 211 Chapter 211
  212. 212 Chapter 212
  213. 213 Chapter 213
  214. 214 Chapter 214
  215. 215 Chapter 215
  216. 216 Chapter 216
  217. 217 Chapter 217
  218. 218 Chapter 218
  219. 219 Chapter 219
  220. 220 Chapter 220
  221. 221 Chapter 221
  222. 222 Chapter 222
  223. 223 Chapter 223
  224. 224 Chapter 224
  225. 225 Chapter 225
  226. 226 Chapter 226
  227. 227 Chapter 227
  228. 228 Chapter 228
  229. 229 Chapter 229
  230. 230 Chapter 230
  231. 231 Chapter 231
  232. 232 Chapter 232
  233. 233 Chapter 233
  234. 234 Chapter 234
  235. 235 Chapter 235
  236. 236 Chapter 236
  237. 237 Chapter 237
  238. 238 Chapter 238
  239. 239 Chapter 239
  240. 240 Chapter 240
  241. 241 Chapter 241
  242. 242 Chapter 242
  243. 243 Chapter 243
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});