Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 129

Chapter 129

Gidan Aro Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

tana mai son Ganin k’wayar idanunsa. “Kace Itace sanadiyar had’uwarmu.?” Sadiya ta tambaya tana dubansa dikda cewa shid’in ba cikin idanunta yake duba ba fuskarta yanda yatsun hannunsa ke sauk’a yana goge mata hawayen nan yake duba. A hankali ya jinjina mata kai kafin yace “Nayi alk’awari wa Mamy cewa matuk’a Ina aikin D’ansanda zan zak’ulo wanda duk ya kashe mata d’iyarta Ikram da izinin Allah.. A ta dalilin binciken mutuwar Ikram na had’u dake har ta kaimu ga aure.. Kinga Mamy tana cikin sanadi.” Ya k’arashe yana mai sauk’e k’wayar idanunsa cikin nata. Ta janye nata idanunta daga barin duban nasa tana mai sakin murmushi a hankal. Murmushin shima yasaki kafin ya maido da dubansa ga mahaifiyarsa. Ya kuma rik’e hannun mahaifiyar tasa dake bacci cikin nasa kafin ya soma fad’in “Mamy.. Ga d’iyarki na kawo miki ku gaisa..” Sai ya d’anyi fasali ya karkato yana duban Sadiya. Lokaci guda yaci gaba da furta “Although She’s the most stubborn person I’ve ever met.. Ko cikin mutanen da nake gwagwarmaya dasu a interrogation room, ban tab’a cin karo da stubborn person irinta ba..” Ji yai ta mintsili hannunsa dake cikin nata. Ya d’an saki k’ara yana dubanta yanda ta firfito da idanu waje. Lokaci guda take girgiza masa kai kafin tace “That’s not true..” Ta fad’i kaman zatai kuka. “Ok nayi shiru kar na fad’a..? Baki so Mamy taji halin ‘yar nata ne..?” Tai narai narai da idanu had’ida mak’e masa kafad’a alamun a’a. Yai intertwining yatsun hannayensu kafin yace “Bribe me idan baki so na fad’a mata..” Ta zaro ido waje tace “D’an sanda da karb’an cin hanci da rashawa..?” Tai maganar a hankali kaman mai tsoron kar Mamayn ta jita. Ya kashe murya kad’an shima kafin yace “Believe me this one is allowed..” Ya fad’i yana kashe mata ido guda. Hakan yayi daidai da shigowar Inne sallama saman bakinta. Suka amsa mata sallamar Sadiya na cire hannunta daga nasa. Ta gyara zamanta sosai daga nan yanda take zaune gaban gadon Mamy. Inne ta k’araso tana tambayarsu ko Mamyn tayi bacci. Mu’azzam ya bata amsa da fad’in tayi bacci ai. Inne ta jinjina kai kafin ta dubi Sadiya da ta sadda kanta k’asa lullub’e da mayafi sai kuma ta dubi Mu’azzam tace “Zata kwana wajena gobe idan Allah ya kaimu da yammaci a kaita d’akinta kaman yanda aka saba a al’ada.. Ba wani taro za’ai ba duba da yanayin jikin Nuratu.. ‘Yan uwa k’alilan ne zasu mata rakiya zuwa d’akinta kaji koh..” A hankali ya furta “Toh Inne..” Kana jin yanda ya amsa kasan a dole ya amsa hakan. Inne ta dubi Sadiya tace “Tashi maza kije koh.. Idan kina son wani abin ki fad’awa Hindu kinji koh.. Ki saki jikinki nan gida ne kinji koh..” Sadiya ta sadda kanta tana mai amsawa da “Toh Inne..” Tana tafe yana binta da Kallo har ta b’acewa ganinsa. Inne na hankalce dashi. Ganin Inne shi take duba ya d’an sanyashi sosa kai kad’an. “Mu’azzam..” “Na’am Inne..” Ya amsa yana dubanta dan tinda yaji batace Modibbo ba ta kirasa da sunansa kai tsaye yasan magana ce mai girma zata masa. Inne ta juya ta nufi parlor tana fad’in “Biyo ni muyi magana.” Babu musu ya mik’e yabi bayanta. A nan parlorn Aunty Nuratun suka zauna, Inne ta tsaresa da idanu. Ya d’an sadda kansa kad’an ba tareda yace komai ba. “Magana nake so muyi kan Safeenah..” Yanajin ta ambaci Safeenah a ransa yace anzo wajen. Inne taci gaba da fad’in “Safeenah ta kirani tana kuka.. Kasan bana d’aukan shashashancin Safeenah amma abinda ta sanar dani cikin waya ya matuk’ar d’aga mun hankali had’ida bani mamaki.. Mu’azzam kana cikin hankalinka zaka furta kalmar saki wa matarka kuma ‘yaruwarka a cikin gidan Mahaifinta.. Gaban mahaifiyarta da kowa nata dan kawai kayi sabon aure..? Babu wanda zai hanaka aure kuma babu wanda zai hanaka d’aukar matarka ka tafi da Ita yanda kake so.. Amma Safeenah tace mun kan kawai tace itama sai ta biyoka shine ka furta cewa ka saketa saikace wata ‘yar tsana.. Haba Mu’azzam saki fah ba k’aramin abu bane.. Ba’a wasa da saki.. Cikin gidan nan kaf wa kaga ya taso yana haka.. Mu ba’a mana wannan shaida ba. Mata hak’uri ake dasu, sabida Kai namiji ne tinanin ka da nasu ba zaizo d’aya ba. Sannan koda mace ta buk’aci saki bazaka biye mata ba.. Dan idan aka biye na mata sai a sakesu sau d’ari musamman idan akan kishiya ce.. Modibbo kishi nada matuk’ar zafi wanda ba Don Allah ne ya hukunta hakan ba kanajin akwai macen da zata amince mijinta ya zauna da wata ce.. A al’amari irin na aure dole a kula da irin haka musamman duba da yanda Kayowa Safeenar wata mata a tsakanin k’ank’anin lokaci.. Banji dad’in abinda ka aikata ba kuma ban amince ka aikata hakan ba saida nasa Safeenah ta bani Hajara a waya ta sanar dani K’warai anyi haka dan kasan bana yarda da wautan Safeenah..” Ta k’arashe cikin b’acin rai. Tinda ta fara magana kansa ke a k’asa. Saida ya bari ta ida kafin ya d’ago yace “Inne kiyi hak’uri.. Nasan bakiji dad’i ba kuma banso Labarin ya riskeki a irin haka ba.. kiyi hak’uri Inne..” Ya k’arashe cikin kwantar da murya. Lokaci guda yaci gaba da fad’in “Inne basu sanar dake gaskiyar abinda ya faru ba.. Quite alright na saki Safeenah amma basu sanar dake yanda al’amarin ya kasance ba..” Inne ta dubesa a d’an karkace kafin tace “Watau dai da gaske dai kayi sakin..” Mu’azzam ya jinjina kai a hankali kafin yace “Nayi amma ba wancan dalilin da Safeenah ta sanar dake bane ya sanyani yin sakin.. Inne ban saki Safeenah dan nayi wani aure ba sann ban saketa dan zan d’auko Sadiya na taho da ita nan ba..” Inne ta katsesa da fad’in “Kana nufin k’arya sukai maka kenan..?” “Kusan haka Inne..” Inne ta girgiza kai tace “Wai meke faruwa ne Modibbo..?” Mu’azzam ya gyara zamansa kad’an yana fad’in “Ni banso kiji wann labarin ba.. Dan nasan zai tada miki hankali ne kawai.. Amma tinda ita Safeenar ita ta kiraki ta sanar dake, kuma hakan na nufin ita ta zab’i kiji, zan sanar dake duk abinda ya faru Inne..” Inne ta gyara zama tana saurarensa. Tiryan tiryan Mu’azzam ke karanto mata dik abinda ya faru.. Tin daga kulle masa k’ofa da Safeenah tai wanda hakan ya hanasa shiga ya sanar mata tafiyar nasa balle yai mata sallama, har d’auko bindigarsa da tai taima Sadiya barazana da rayuwarta harde da munanan kalaman da ta dinga ambatonsa dashi har dai zuwa harba bindigar jikin garu da Safeenah tai zuwa zab’i data basa tsakaninta da Sadiya.. Ko abu guda bai b’oyewa Inne ba sai zuwan Mommy gidansa da tai tace sai ya saki Safeenah shine kawai bai sanar da Inne ba dan har wannan lokaci Kallon Uwa yakewa Mommy dan yasan ko mai Mommy zata masa bazai tab’a biyan d’awainiyar da sukai masu ba daga ita har Daddy musamman akan mahaifiyarsa. Sam baijin zai iya tozarta Mommy koda mai zata masa. Inne da take jin abun, shaye da mamaki take dubansa “Safeenah tace da bindiga zata harbi mutum..?” Mu’azzam yai shiru baici komai ba dan dama ba’a sanar da Innen ba lokacin da

Table of Contents

Chapters

243 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
  170. 170 Chapter 170
  171. 171 Chapter 171
  172. 172 Chapter 172
  173. 173 Chapter 173
  174. 174 Chapter 174
  175. 175 Chapter 175
  176. 176 Chapter 176
  177. 177 Chapter 177
  178. 178 Chapter 178
  179. 179 Chapter 179
  180. 180 Chapter 180
  181. 181 Chapter 181
  182. 182 Chapter 182
  183. 183 Chapter 183
  184. 184 Chapter 184
  185. 185 Chapter 185
  186. 186 Chapter 186
  187. 187 Chapter 187
  188. 188 Chapter 188
  189. 189 Chapter 189
  190. 190 Chapter 190
  191. 191 Chapter 191
  192. 192 Chapter 192
  193. 193 Chapter 193
  194. 194 Chapter 194
  195. 195 Chapter 195
  196. 196 Chapter 196
  197. 197 Chapter 197
  198. 198 Chapter 198
  199. 199 Chapter 199
  200. 200 Chapter 200
  201. 201 Chapter 201
  202. 202 Chapter 202
  203. 203 Chapter 203
  204. 204 Chapter 204
  205. 205 Chapter 205
  206. 206 Chapter 206
  207. 207 Chapter 207
  208. 208 Chapter 208
  209. 209 Chapter 209
  210. 210 Chapter 210
  211. 211 Chapter 211
  212. 212 Chapter 212
  213. 213 Chapter 213
  214. 214 Chapter 214
  215. 215 Chapter 215
  216. 216 Chapter 216
  217. 217 Chapter 217
  218. 218 Chapter 218
  219. 219 Chapter 219
  220. 220 Chapter 220
  221. 221 Chapter 221
  222. 222 Chapter 222
  223. 223 Chapter 223
  224. 224 Chapter 224
  225. 225 Chapter 225
  226. 226 Chapter 226
  227. 227 Chapter 227
  228. 228 Chapter 228
  229. 229 Chapter 229
  230. 230 Chapter 230
  231. 231 Chapter 231
  232. 232 Chapter 232
  233. 233 Chapter 233
  234. 234 Chapter 234
  235. 235 Chapter 235
  236. 236 Chapter 236
  237. 237 Chapter 237
  238. 238 Chapter 238
  239. 239 Chapter 239
  240. 240 Chapter 240
  241. 241 Chapter 241
  242. 242 Chapter 242
  243. 243 Chapter 243
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});