Chapter 119
Chapter 119
Ajidde ta juyo tana duban Mama Hindu.. Sai kuma ta soma nuna mata hoton ba tareda tace komai ba..” Girgiza kai Mama Hindu tai tace “Toh Sarkin shiririta wanene bak’o cikinsu a wajenki. Inne ce baki sani ba ko kuwa Mu’azzam da Musaddiq ne baki sani ba..?” “Mana Hindu kika ce menene sunan wancan dake tsaye daga b’angaren hagu..?” Mama Hindu Ta girgiza kai tace “Wai duk zuwanki gidan nan baki sansa ba.. Kwanakin baya ya koma can Abuja gidan Babansa amma ya jima a nan ai shi Musaddiq d’in..” Ajidde tace “Kika ce sunansa Musaddiq.. Toh ai shine Kuran tashe.. Na rantse da Allah shine Kuran tashe.. Wllhi bazan tab’a mance kamanninsa ba.. Dama jikan Inne ne..?” Mama Hindu ta girgiza kai tace “Adana tambayoyinki har ku dawo Inne na jiranki yanzu tintini Malam Sadi ya tada mota ke ake jira..” Ta k’arashe tana janyo Ajidden daketa faman waigowa tana kuma duban hoton Musaddiq daketa sakin murmushi. Mamaki fal Zuciyar Ajidde Wai jikan gidan ne.. Shine yace mata shi ba d’an gidan bane babu abinda ya had’asu Sai abota da yake da d’an gidan.. Wato k’arya ya mata kenan.. Toh Maiyasa ya mata k’arya.. Maiyasa ya b’oye mata asalinsa.. Duk sai taji babu dad’i.. Jikinta gaba d’aya sai taji kaman an zare mata laka.. Duk da wauta da shahshashanci irin nata sosai taji zafin abinda Kuran tashe yai mata na b’oye mata kansa da yai, sannan tana son sanin Maiyasa ya mata hakan. Ranan haka Ajidde har Ta koma gida tunanin da take kenan b’oye mata kansa da Musaddiq yai.. Sunansa kuwa ranan kaman biya karatu haka taita nanatawa.. Yanzu Kyallu batada lokacinta sosai dan tana samun majinyata da take kwantar dasu a nan gidanta akai akai.. Idan ta baiwa Ajidde maganin Gidan Gona bata kuma bi takanta.. Hakan sai yafi ma Ajidde dad’i da bata yini a gidan balle taga yanda ake shirka ma Ubangiji da sunan magani. Ko safiyan Washe gari ma da zata fice taga wata mata an kawota bata cikin hayyacinta Kyallu tace a kawo Bak’in zakara da budurwa Baru a masu barbara sannan aka buga kan bak’in zakaran da dutse wanda saida ya mutu jini ya soma zuba Kyallu tace Jinin za’a baiwa matar sannan a shafe jikinta da sauran shine maganin ciwonta.. Ajidde Ta girgiza kai kurum kafin ta fice ta nufi gidan Malama Hafsah. Daga yanda Malama ta ganta Jiki a sanyaye ta fahimci wani abu na damunta. Malama ta tambayeta meke faruwa.? Ajidde tai shiru tana duban Malama bata sanar da ita abinda Musaddiq yai mata ba Sai ta soma sanar da ita abinda taga Kyallu tayi. Malama Ta nusa kad’an tace “Da yawan irin wad’ann bokayen sun ari sunayen masu magani na gargajiya suna fakewa suna yin bokancinsu Ajidde.. Tabbas akwai masu magani na gaskiya na gargajiya wanda ubangiji ya huwace masu ilimin sanin magunguna.. Sannan akwai Malamai masu magani da ayoyin Ubangiji bisa tsari da shari’a.. Sannan akwai wad’anda suke fakewa suke bokanci suna yanka dabbobi bada sunan Allah ba suna bawa mushirikan Aljanu jini.. Sai kiji ana cewa a kawo bak’in jaki za’ayi magani, a’a a kawo faran tinkiya za’ayi magani.. Irin wad’ann masu maganin Ajidde duk sun b’adda kama suna shiga cikin na gari suna bokanci da tsafi.. Suna shirka ma Ubangiji da sunan magani.. Akwai majinyata da ciwo zaik’i ci yak’i cinyewa.. Aita kawo masa sunayen masu magani gari wa gari.. Idan ba’ayi sa’a ba har a fad’a hannun irin wad’ann masu maganin wad’anda bokaye ne masu shirka ma Ubangiji ba wai maganin sukeyi ba wasu ma kawai sai su had’a ‘yanuwa gaba suce wane ne yai maka jifa alhali k’arya ce kawai bokanci ne da tsafi... Abu na farko da majinyaci zai saka a ransa shine jinyar nan Bautan Ubangiji yake.. Kuma jarabawa ce da Allah ya jarabcesa da ita domin yaga zaiyi hak’uri yaci jarabawa kokuwa zai kauce wa rahamarsa.. Duk zafin jinya zunubi ake kankare wa majinyaci.. Sannan suma masu jinyar wann majinyacin jarabawa ce da Allah ya jarabcesu da ita kuma duk d’awainiyar da sukai wa mai jinya lada suke samu wanda Allah shi zai biyasu wanan ladan na hak’uri da kuma d’awainiyarsu.. Hadisi yazo ingantacce Manzon Allah (S.A.W) yace babu wata cuta da Allah ya sauk’ar saida ya sauk’ar mata da maganinta. Ko wata iri ce kuwa... Neman magani ba haramun bane kuma godiyan Ubangiji shine ka saka dukiyanka ka nemi lafiya da Ita, amma saidai kar garin neman magani ka kai kanka ga halak’a.. Kar kaje wajen boka domin ya baka lafiya.. Babu mai warkarwa sai Allah.. Shi yake saka cuta kuma shi yake yayewa.. Idan yaso ko baka sha komai ba Sai ya baka lafiya dan shine mai bayarwan. Idan baiso ka sami lafiya ba ko zaka zaga duniyar nan Sai k’a k’arashi neman maganinka baka samu ba.. Tauhidi itace abu na farko da majinyaci yake buk’ata Ajidde.. Ita ce magani na farko da majinyaci zai sha.. Ya saka a ransa Allah shine mai yi kuma shine mai hanawa.. Idan ya tsira da tauhidinsa ko da Ubangiji ya k’addari wann jinya ba na tashi bane sai yayi fatan ya d’auki ransa yana mai imani ba yana mai kauce ma Ubangijinsa ba.. Sau tari zakiga anje wajen irin wad’ann masu maganin anyi bori anyi yanka ma aljanu sannan an halak’a daga k’arshe ba’a samu biyan buk’atan ba dan basu sukeyi ba Allah shine mai yi.. Ba’a samu biyan buk’ata ba Sannan an mutu ana kauce wa Ubangiji.. Allah ya shiryemu gaba d’aya ya kuma datar damu.. Ya ba ma marassa lafiyanmu lafiya, ya tsare mana imanin mu da tauhidinmu.. Ya d’auki rayuwarmu yana mai farin ciki damu..” A hankali Ajidde ta jinjina kai tana fad’in “Ameen Malama..” Malama Hafsah ta mik’o mata ruwa addu’a da take bata sannan ta had’a mata da garin Habbatussauda tace wannan hayak’insa zaki mata a cikin d’akin da take kwana.. Yana koran shaid’anu.. Sannan yanada kyau mutum ya dinga hayak’in habbatussauda a cikin gidansa lokaci zuwa lokaci domin yana kore shaid’anu daga gida.” Ajidde ta jinjina kai tace “Toh Malama Allah ya saka da alkhairi ni zan wuce..” Malama ta jinjina kai tace “Allah ya nufemu da dacewa ya kuma bawa Nuratu lafiya..” Ajidde ta amsa da Ameen kafin sukai sallama da Malama ta fice. ** ABUJA Yau kusan kwanaki uku kenan bata sanyasa a idanunta ba, tinda ya tafi ranan da dare bata kuma ganinsa ba, gashi harta waya ma bai mata ba.. Haka zatai ta kallon lambarsa taji kaman ta danna kira amma sai ta fasa dan batasan mai zata ce masa ba.. Kasancewar laraba tayi ya sanya take ta jin wani Farin ciki cikin zuciyarta dan tafiyarsu Alhamis ne kaman yanda yace. Harga Allah ba Farin cikin tafiyar take ba amma tasan tana Farin ciki ne sabida zata gansa.. Tai shiru tana tuhumar kanta Maiyasa take jin haka akansa..? A baya zata iya cewa bata tab’a jin irin hakan ga kowa ba harta kuwa Sagir da suka kusan aure.. Ko dan lokacin abin hannayensu take so ba Su d’in ba..? Toh Maiyasa yanzu da bata son abin hannun kowa take jin haka gameda Inspector..? Kar fah maganan Aunty Larai ya tabbata cewa son Inspector take.. Cikin sauri ta d’ago kai tana duban
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182
- 183 Chapter 183
- 184 Chapter 184
- 185 Chapter 185
- 186 Chapter 186
- 187 Chapter 187
- 188 Chapter 188
- 189 Chapter 189
- 190 Chapter 190
- 191 Chapter 191
- 192 Chapter 192
- 193 Chapter 193
- 194 Chapter 194
- 195 Chapter 195
- 196 Chapter 196
- 197 Chapter 197
- 198 Chapter 198
- 199 Chapter 199
- 200 Chapter 200
- 201 Chapter 201
- 202 Chapter 202
- 203 Chapter 203
- 204 Chapter 204
- 205 Chapter 205
- 206 Chapter 206
- 207 Chapter 207
- 208 Chapter 208
- 209 Chapter 209
- 210 Chapter 210
- 211 Chapter 211
- 212 Chapter 212
- 213 Chapter 213
- 214 Chapter 214
- 215 Chapter 215
- 216 Chapter 216
- 217 Chapter 217
- 218 Chapter 218
- 219 Chapter 219
- 220 Chapter 220
- 221 Chapter 221
- 222 Chapter 222
- 223 Chapter 223
- 224 Chapter 224
- 225 Chapter 225
- 226 Chapter 226
- 227 Chapter 227
- 228 Chapter 228
- 229 Chapter 229
- 230 Chapter 230
- 231 Chapter 231
- 232 Chapter 232
- 233 Chapter 233
- 234 Chapter 234
- 235 Chapter 235
- 236 Chapter 236
- 237 Chapter 237
- 238 Chapter 238
- 239 Chapter 239
- 240 Chapter 240
- 241 Chapter 241
- 242 Chapter 242
- 243 Chapter 243