Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 99

Chapter 99

Abinda Ake Gudu Book 1 Complete Hausa Novel 1,196 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kwara a dakin" Babanta ya dafe kirji "ince ko ba ke kike gyara wurin ba idan yayi amai" Tayi kwalkwal da idanu "waye zai gyara idan banyi ba. Yanzu ma itace nake so ya siyo min wani saboda wannan yayi danshi yau da marmarin kunu na tashi. Amma yaki fitowa" Zinaru sai bude baki take amma ta ma kasa magana don mamakin karyar da Amarya ke gillawa. Ran Garbebe ya baci sosai. Yadda yake son yarsa shiyasa tana cewa Gidado take so ya amince. Yanzu ga ciki burinsa ta haihu ya sami jika. Ya dallawa Zinaru harara sannan ya fara kwalawa Gidado kira. Mutumin banza haka ya fito daga shi sai wani kodadden wando duk jirwaye. Garbebe yace "na gaji da wannan rashin kirkin naku. Kaje ka kwashe gwanjonka daga shagona. Ke kuma Zinaru idan jikan ne baki so ki fada ba sai kunyi mata horon yunwa ba. Daga yau bazata kara aikin amai ba don ba baiwarku bace" Gidado yace "uwar tawa kake fadawa magana haka?" Zinaru ta kwabe shi cikin harshen fulatanci "kyaleni dasu ka koma daki. Takarda aka kawo daga wurin uwar yaranka nasan bazasu yarda ta kuma zama da kai ba. Amma na sami dillali zan biya shi ya taimaka mu sayar da gidannan ko babu takardu. Ita kuma wannan kazar matsiyatan ka bari mu karbi kudin gidan sai ka saketa itama su karata ita da uban nata. Har yanzu da kyaunka Gidado baza mu rasa 'yar masu kudin da zaka iya aura ba" Shiru Gidado yayi da yaji zancen saki tsakaninsa da Zulaiha. Yara har shida tsakaninsu dole yaji yana sonta duk irin halinsa kuwa. Garbebe ya ja hannun Amarya suka yi wajen kofar gidan yace "shegun nan basu san mu fulani bane hala" Amarya tace "basa yin yaren a gidan shiyasa bana yi musu. Basu san na iya ba" Garbebe ya tafa hannuwa "karen bana ke maganin zomon bana. Kyaleni dasu ki koma amma ki fara shiri gaskiya aurenku ya kare. Ya ma kika ce sunan baban matarsa ta fari?" Amarya ta fada masa ya kwashi kafa sai gidan su Zulaiha. ***** Qasim da Ma'u ke hira a bangaren da ake ajiye motoci tana cewa ya shigo ciki yaci abinci saboda ya kwaso hanya. Innarsu ce tace ta kirashi ma amma yaki amincewa wai gara ta kawo masa nan. "Kai har ka fini kunya ma" Qasim yace "haka kike gani ko, nan da wata uku ne zaki gane waye Qasim" Ma'u tayi dariya "har kasa mana ranar ne?" "Nan da sati biyu za'a kawo kudi da sa rana. ni dai nace wata biyu za'a saka daga nan sai ki fara shirin komawa Zamfara" Tayi murmushi "Allah Ya tabbatar mana da alkhairi" Hayaniya suka ji daga bakin gate karshe dai maigadi yazo ya fada mata wani ke neman Alhaji tace baya nan bari taje ta gani. Qasim ya daure fuska "ina zaune zaki je bakin gate ganin wanda ba'a sani ba. Muje tare dai just incase na gida ne." Ma'u ta mike suka tafi. Mutumin dai basu sanshi ba amma sun fahimci labarin da ya kawo musu na cewa Zinaru zata sayar da gidan Zulaiha. Ma'u tace bari ta fada a cikin gida. Tare da Zulaihan suka fito. Tana ganinsa ta gane shi, lokacin da take tare da Gidado har dashi ake mata wulakanci kala kala wai shi mai 'ya. Yanzu kuwa russunawa yayi yana diban gaisuwa kafin ya sake mata bayanin abinda ya kawo shi. Zulaiha tayi masa godiya tace babu komai hukuma zata shiga zancen tana nuna Qasim. Garbebe ya dan tsaya yana jiran ihsani ladan kawo gulma yaga babu wanda yayi motsi cikinsu sai ya tafi kawai. Ko ba komai ya tarewa Zinaru hanyar samu. Yana fita wata mota hadaddiya ta shigo gidan. Wani mutum ne a bayan motar dreba na jansa. Maigadi yana ta daga hannu saboda Alh Najib akwai kyauta. Kusa da inda Qasim, Ma'u da Zulaiha ke tsaye suna zancen hali irin na Gidado da Zinaru akayi parking motar ya fito. Da fara'asa ya mikawa Qasim hannu suka gaisa sannan ya gaisa da Ma'u da Zulaiha wadda ta kasa kallonsa ma. Ciki ya shiga yace Alhaji na hanya zai jira shi ne. Bayan ya wuce Zulaiha ta tafi jikinta babu kwari. Ma'u tace "wannan Alhaji yaso aura mata fa taki yarda tun farko. Anti Zulaiha tayi masa wulakanci sosai gashi yanzu tana kunyarsa." Qasim yace "rabon haihuwa yasa ta auri wancan. Kuma gara haka akan ta haifesu a titi. Tunda ba yau zan tafi ba sai ki fadawa Alhaji in shiga case din Gidadon nan" "Ai kuwa zaiyi murna. Bari ya dawo anjima sai na fada masa". ***** Cikin kwanaki biyu Zinaru da Gidado sun tattara komai nasu zasu bar gidan sannan yayi mata saki daya. Tayi ta rokon Zulaiha wai ko albarkacin yara ta yafe musu a mayar da auren. Ko kallon kirki basu samu ba daga gareta balle yan uwanta. Da kwanan titi gara na kauye a dole tayi shirin komaa garinsu wane kauye a cikin Taraba state. Bats sani ba mijinta da ta baro yana da rai ko ya mutu. Alhajin su Zulaiha yace lallai wasu daga cikin yayyenta maza su bi bayansu aga tushensu albarkacin yara. Zinaru an sha kuka ga Amarya ma Garbebe ya karbar mata takardar saki. Su Humaira ko a jikinsu saboda irin mugun zaman da suka yi a hannun kakarsu da Babansu wanda bai san kowa ba sai kansa. Ganin idon Qasim ne ma yasa yabi Zinaru a son ransa ko a karkashin gada ya kwana indai zai sami ganyensa ya busa. Alh Najib kuwa tunda yaji anyi saki ya sanar da Alhaji idan Zulaiha ta gama idda a fada mata har yanzu yana sonta. Yana da mata dai da yara hudu. Banda auren wuri shekarunta goma sha shida ta auri Gidado ko secondary bata gama ba. ***** Sati biyu a tsakani aka taho nemawa Qasim auren Ma'u harda Col. Ishaq Jikamshi cikin tawagar su Alh Adamu. Wannan abu yayi dadi domin rashin auren Asmau bai sa sun kullaci juna ba. Daga zuwa kawo kudi Alhaji yace indai sun amince a kawo sadaki kawai a daura aure kada ayi ta wahalar da mutane. Haka kuwa akayi aka saka biki da tariya wata guda. Col. Ishaq ne ya kira Qasim da wannan albishir. Yayi murna sosai shikenan shima ya shiga sahun magidanta. Innarsa kuwa kamar tayi me don dadi. Allah Ya taumaketa danta yayi aure kuma ya auro yar mutumci irin wadda take so. ***** Zuwa yanzu kowa yasan da cikin Asmau a cikin 'yan uwanta da nasa. Kulawa take samu ta kowane bangare kada Mami taji labari. Sosai take kaunarta yanzu. Saura sati biyu bikin Qasim tana ta shirin zuwa Jos yana kallonta kawai. Ciki wata hudu ga laulayin da take fama amma ta dage da roko har da addua akan ya barta taje ko don Zulaiha. Sun gama rigimarsu yana ta shan kunu Amatullah tace masa tayi masa tuni zai kaita siyan takalmin makaranta na gudu. Da kyar ya yarda suka tafi da Asmau. A hanya aka shirya dama basa dogon fushi da juna. Sun gama siyayyarsu suna fitowa daidai inda suka ajiye mota suka hadu da wasu maza su biyu cikin shiga ta kamala kayansu ma iri daya. Daya

Table of Contents

Chapters

103 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});