Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 54

Chapter 54

Abinda Ake Gudu Book 1 Complete Hausa Novel 1,197 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

zuwa zai tura masu wakiltarsa a nemawa Qasim auren Asmau. Ya gaji da ganin dan nasa gwuaro. Da Qasim yace basu gama shawara sa Asmau ba, Mal Musa yace babu komai sunyi magana da Alh Adamu yace zaije ya sami Umma da Kawu Garzali a tsayar da magana ayi aure kowa ya huta. Murmushi Qasim yayi na jindadi don yasan Asmau bazata bijerewa iyayensu ba. ABINDA AKE GUDU🙆🏽40 Batul Mamman💖 Washegari su Asmau basu sami zaman gida ba. Sun hadu da Shemau, Sabira da su Nasiba an sake gyara gidan Ainau kamar masu shirin kai amarya. Da yamma Umar yaje ya daukota. Kana ganinsa kasan yau yana cikin farinciki. Kusan wata uku bata gida don tun kafin ta haihu aka bata bedrest shine Mama tace ya kaita gida zata fi hutawa. Ranar Jikamshi ya kirata yafi sau shida kuma sai anyi hira akalla ta rabin awa. Yana kira sai ya tambayeta ko Qasim ya kira kuma wayar minti nawa suka yi. Sai da ta gama dariya sannan ta zolaye shi tace "baya ajiye waya sai wata wayar ta shigo min." Shima dariyar yayi mata kawai yace "ba zan damu ba don nasan tawa hirar ce kawai take burgeki koda kuwa ta minti daya ce. Amma zancen gaskiya ki dena kashe masa murya yadda kike yi min. Kara sonki kawai zaiyi ni kuma ba hakura zanyi na bar masa ba" Tayi dariya sosai hakan ya sanya shi nishadi. "Haba Yaya Ishaq, kai fa Yayana ne kuma Yayan Qasim. Kaci girma kawai" Kamar tana gabanshi ya dan daure fuska cikin wasa "ki kiyaye ni fa matar Jikamshi. Ni ba yayanki bane na fada miki. Kina magana da baban Safina mijin Asmau in Sha Allah" Ta danyi shiru tana jin inama hakan ya tabbata. "Baki ce amin ba" "Amin" ta amsa ba don yana tunanin ganin ranar aurensu a gaba ba. Addua zata yi masa Allah Ya bashi mace ta gari. Amma tasan bazata je komai ba a bikin. Daga haka suka yi sallama kowannensu yana kara jin son dan uwansa. ***** Bayan sati daya kullum Col. Ishaq da Qasim sai sun kirata a waya kowanne yana kara jaddada mata irin son da yake mata. A wannan kwanakin da Jikamshi bai zo ba ita kanta abin ba karamin damunta yayi ba. Har mamaki take yi da take masa so irin wannan duk da tana kokarin dannewa. Ranar alhamis ta kira Zubaida ta sanar da ita zata zo yini washegari. Zubaida sai murna don tun dawowarta sau daya ta samu taje gidan, basu zauna sunyi hira yadda suke so ba. Ita kuma Zubaida saboda cikinta ya tsufa babu batun fita. Kafin shabiyun rana washegarin Asmau ta gama girkin rana tayiwa Amatullah wanka sannan itama ta shiga. Tana fitowa taga Umma ta dawo duk da ranar aiki ne. Har daki ta bita tana tambayar ko lafiya. "Babu komai yau dai na gaji ne. Kinsan kwana biyu bamu huta ba. Kema da kin hakura da zuwa gidan Zubaidan sai wani satin. Yarinyar nan kina ta yawo da ita 'yan kwanakin nan" "Umma Yaya Jafar yace zai kaini ba adaidaita zan hau ba." "To kiyi maza ki karasa shiri kinsan baya son jira." Asmau ta tashi ta koma daki ta karasa shiryawa sannan ta zauna jiran Jafar. Ko rabin awa ba ayi ba ya iso. Suna shirin fita taga Kawu Garzali shima ya shigo. Gaisawa suka yi yace mata Zubaida tun asuba take jiranta. Yanzu Kawun nasu kamar wani kaka haka yake musu wasa. Shima dai tayi mamakin ganinsa don ance mata Umma ce ta sama masa aiki a inda take wato MTN office. ***** Suna fita Umma tayi ajiyar zuciya ta tafi dakin Hajjo ta sanar da ita wayar da suka yi da Mama tun tana wurin aiki. Shine ma dalilin dawowarta gida da wuri da zuwan Kawu Garzali. Alh Adamu ne yake son ganinsu don yace gidan zai zo idan ta taso aiki. Kasa hakura tayi saboda Mama tace mata batun auren Asmau da Qasim ne zai kawo shi. Shiyasa ta fada Garzalin suka dawo gida kawai. A cikin satin da tayi magana da Asmau akan manemanta biyun ta nuna mata ita karatu kawai zatayi duk zata sallamesu batare da bacin rai ba. Sai dai kuma tuni Umma ta gano inda zuciyar 'yarta tafi karkata. Matsalar dai bai wuce abinda itama Asmau take jiyewa tsoro ba na dangane da gori ko rashin amincewa daga dangin mazan. Bayan ta gama bayaninta Hajjo tace "yaron nan da gaske yake da rike amanar amininsa. Allah Ya tabbatar da alkhairi." Ta danyi shiru kamar mai tunani sannan tace "Amma idan banyi kuskuren fahimta ba sai naga Ishaq shima kamar fa sonta yake yi. Kinsan mu idonmu idon soyayya. Muna ganinta muke ganewa" Umma tayi dariya sannan ta fada mata wayarsu da Anti Bintu da kuma yadda suka yi da Asmau "Bazamu zuba mata ido ba duk da muna jin tsoron surutun mutane auren shine rufin asirinmu. Duka su biyun ni bana kin kowa amma Hajjo kinga Qasim muka fi sani kuma gashi har maganarsa ta kai kunnen manya. Garzali ma ya shigo ina tsammanin a falo ya tsaya. Shine namiji dole ayi komai dashi " "Kinga wancan mutumin banzan shi ya kamata ace zaiyi komai akan lamarin yaran nan amma kafin a ganshi ma aiki ne" Umma ta fahimci da Kawu Rabe take. Murmushi kawai tayi "kada ki damu Hajjo, Garzalin ma ai babanta ne kuma na fadawa su Yaya Abu don su san me ake ciki. Saura kuma sai yazo munji" Kawu Garzali sallama zai shigo dakin yaji Hajjo tace "Kinsan Allah Bara'atu kada ku yarda kuce kun amince ba tare da munji ta bakin Asmau ba, bazan yarda kuyi mata auren dole ba. Idan bata so ya hakura kawai" Umma tace "Hajjo mu har mun isa muce bama so? Kada ki manta duk abinda ya faru da Asmau. Yanzu duk wanda yazo neman aurenta ai alfarma yayi mana" Hajjo ta danyi shiru tana tausayawa jikarta "kuma fa haka ne. Allah Ya rabamu da mummunar kaddara" Tashi Umma tayi "dama yanzun ma ina jin shawara ce dai yake son bamu a matsayinsa na uba gareta." Kawu Garzali ya gaishe da Hajjo sannan tace su fito falo Alh Adamu yazo. ***** Sun zazzauna an gaisa da Alh Adamu da Mama Yalwa da bata dade da shigowa ba itama. Yayi dan gyaran murya wanda ya janyo suka fuskance shi "Nasan Yalwa ta fara sanar dake dalilin zuwan nan. Mal Musa ya kirani a waya ya sanar dani yadda suka yi da Qasim akan auren Asmau. To shi a son ransa nan da lahadi su zo ayi magana ta iyaye a tsayar da lokaci. Shine ya bukaci lallai in fara sanar daku domin ayi shawara" Hajjo ce ta soma magana "hakika Alhaji kai uba ne ga dukkan 'ya'yan Bara'atu. Ka rikesu tsakani da Allah tun lokacin da mu da suke dolenmu muka wofantar dasu. Duk shawarar da ka yanke akan yarinyar nan muna da tabbacin bazata cutar da ita." "Duk da haka Hajjo me kuka gani? A basu dama su zo ko akwai wani tanadi da kuka yi mata". Kawu Garzali yayi saurin cewa "haba haba Alhaji akwai wani tanadi ne da ya wuce aure. Amma Haj Bara'atu me kika gani?"

Table of Contents

Chapters

103 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});