Chapter 85
Chapter 85
a goshinta yayi mata wani kiss din ya tafi ya barta a tsaye tana numfashi da kyar. ABINDA AKE GUDU🙆🏽54 Batul Mamman💖 _Gaisuwa da fatan alkhairi gareki Maman Iman da Asim. Nagode Allah Ya saka da alkhairi._ Har motarsa ta fita daga gidan Asmau ta kasa motsi kamar an kafeta a wurin. Daga ciki taji kamar ana taba kofa tayi saurin bude kofar ta shiga da sanda ga takalma a hannu. Tayi sa'a masu kwanan falo wasu sunyi bacci. Na ido biyun kuma ba 'yan tsirku bane. Dakin Sabira ta lallaba ta shiga suma suna kwance. A ranta tace wai sun dade ne da Jikamshi a waje? Ita fa gani tayi kamar bai jima ba. Tana dukawa ta ajiye takalmanta taji ance "Sai yanzu" Ba karamin tsorata tayi ba harda dan tsalle. Ta juya suka hada ido da Zulaiha tana murmushi. "Meye haka kika firgice kamar an kama barawo. Kinga bakinki kuwa?" Asmau tayi saurin dora hannu akan lebenta tana rufewa don a tunaninta ana ganin abinda Jikamshi yayi mata a bakin. Ko kafin ta shigo ji take kamar a lokacin yayi. Ido a waje tace "me...me kika gani a bakin nawa?" Zulaiha sai dariya tace "amma dai kina da matsala. Kowa ya ganki sai yasan baki da gaskiya. Yanzu yanzu kin tonawa bawan Allah asiri har na gano abinda baki son na gane" "Da gaske ana gani? Na shiga uku. Shiyasa a falo suka bini da kallo ashe." sai kuma ta sake rufe baki da ta gane sake tonawa kanta asiri take ta shige toilet da gudu tana jin dariyar Zulaiha. Ita Zulaiha kwanciya ta gyara tana dariya tace "dama wannan angon naki ai banga alamar wasa ba tare dashi. Goben ma gara a kaiki da wuri kada muji dirar sojoji a gidan nan". ***** Wanka Asmau tayi ta dauro alwala ta fito. Dakin dai shiru Zulaiha ma ta gyangyada. Ta dafe kirjinta oh Allah Yasa sauran basu gane ba. Amma Jikamshi ya janyo mata jin kunya sosai. Ko mai bata shafa ba ta saka kayan bacci ta kwanta saboda gajiya. Ji tayi tana son kiransa taji ko yaje gida lafiya. Gashi har daya ta wuce idonta ya soye kamar ba wadda ta gaji ba. Tana ta tantamar kiran nasa taji wayarsa ta shigo. Saurin dauka tayi saboda kada ringing din ya tashi masu bacci. Zaune yake akan gado ya jingina da pillow. Shima tunda yayi wanka bacci ya kaurace masa. Matarsa yake tunani da yadda yaji dadin hirarsu ta dazu. Tana dauka yace "me ya hanaki bacci" Wannan murya ta Jikamshinta ita kadai tasan dadin da take mata. Sai taji kamar kada ya dena magana. Rufe ido tayi taki magana "Ni ne ko? Na biya miki sabon karatu na tafi na barki da bugun zuciya" Sake runtse ido tayi kamar yana gabanta tana jin kunyar kalamansa "ban ce ba fa" "Ai ni nace. Kada ki manta ban dade da jin bugun zuciyarki ba a kirjina, kinsan shi baya karya. Nasan dai nawa yafi naki. Tsoronki yasa baki nutsu ba kinji zuciyar da take bugu da kaunarki. Burina na farko ya cika. Na aureki, na biyun ma in sha Allah zai cika. Shine mu sami zaman lafiya da fahimtar juna" Tayi dan murmushi tace "Amin Jikamshina" Kwanciya ya gyara yace "Kinsan tun yaushe nake son daukar ki? Tun ranar da kare ya biyoki. Daga ranar kika tashi daga matsayin Ummin Safina a wurina kika koma Matar Jikamshi." "Wannan karen naka bai kyauta min ba" "Ni kuwa yayi min komai. Ya bude kofar zuciyar Asmaun Ishaq. Ya kamata ki kwanta haka kafin gobe" Hamma take yi amma kuma bata so ya ajiye wayar. "Bana jin bacci. Gobe nayi idan an gama hidimar nan" Tashi yayi zaune yana kallon wayar da mamaki kamar ita ce Asmau sannan ya mayar kunnensa "ba dai a gidana ba ko?" Asmau tace "to a ina zanyi. Kasan nan yini za'ayi babu lokacin bacci" "Kinga Allah Ya bamu alkhairi, ki kwanta kawai ko babu baccin ki rufe idonki ki huta. Wai bacci! Matar Jikamshi anya kina sona kuwa, a ina kika taba jin anyi bacci ranar da aka kai amarya idan ba auren dole ba?" magana yake da gasken sa ya ma za'ayi ta fadi magana irin wannan. Sai da tayi dariya tace "To bazan tambayeka me ya kamata ayi ba nasan halinka. Yanzu sai kasa na gwammace banyi magana ba, ka fi karfina" "Muka fi karfin juna dai. Dama yaushe zaki tambaya bayan kin san abinda nake nufi." Dariyarta yaji sannan tace "uhmm bari naje falo neman pillow din kujera na dakin sun kare ni kuma bana jin dadin bacci haka." "Kice dai kawai kina so kiyi pillow da kirjin mijinki. Daga gobe ne fa Matar Jikamshi. Har kin fini....." Ya Salaam, bata kara magana ba ta kashe wayar ta fita neman pillow tana dariya. Haka ta dawo ta kwanta don bata samu ba. Shima dariyar kunyar da yasan taji ya gama ya gyara kwanciya yana tuno dan lokacinsu na dazu zuciyarsa na kara nutsuwa da zabin da Allah Yayi masa. ***** Da safe sai da suka yi breakfast kowa ya shirya aka fara komawa gidan Umma wurin yini. Yau atampa ta saka anyi mata dinkin half-gown da plain zani. Ta kashe dauri ta yafa mayafi irin na kayan. Da ta fito falo guda aka saka amarya da farinjini. Kujeru aka jera a waje da tabarmi da kafet. Sai ga Ado Gwanja ya iso da tawagarsa. Wannan aikin Sally ne 'yar Yaya Abu da Ab Kura kamar yadda suka saba kiran babbar 'yar Anti Lami. Sun dage sai sun gwangwaje suma a bikin nan. Tun kafin dawowar Asmau zumuncin 'yan uwan ya karu bayan tafiyar Kawu Rabe. 'Yan mata kuwa da su Shemau aka shiga filin rawa. Amarya dai sai janta akeyi amma ko da can bata iya sakin jiki tayi rawa balle yanzu da tun jiya Jikamshinta ya rada mata baya son rawar nan. Idan zatayi ta jira sai su kadai. Ana ciye ciye biki na ta tafiya aka kira Sabira a waya sai ta fita da gudu tana murna. Anti Bintu tace "ke lafiyarki kuwa" Sauri take ta karasa waje ta taro bakin tace "Anti Bintu 'ya'yan yayyen Mama ne daga Maiduguri. Mota ce tayi musu tsiya tun shekaranjiya suka so zuwa." Ta fita ta taro 'yan uwanta tazo ta gabatar dasu wurin amarya Asmau. "Wannan sunanta Fatima Goni ga kuma Amalus sai Halima Wasagu da Feey. Cousins dina da nace miki suna son zuwa biki" Asmau fuska a sake ta gaisa dasu tana godiya da suka sami damar zuwa. Daga nan aka cigaba da taro har yamma. Sai da magariba ta gabato aka sallami mai waka iyaye suka kira Asmau cikin dakin Hajjo. Jikinta ya gama sanyi ta shiga dakin suna zazzaune. Hajjo ce a tsakiya ga Mama Yalwa, Umma, Anti Bintu, Yaya Abu da Anti Lami don kara irin tasu harda Yaya Tagwai da Uwargida basu nuna mata kyama ba. Nasiha ce suke mata wadda tasa ta kuka kamar an bude famfo. Hakuri ne kowacce take mata nuni dashi domin shine jigo a zaman aure duk son da kuke yiwa juna da miji to sai an kai zuciya nesa. Zama ne ake fatan yi har karshen rayuwa. Suka dora mata da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103