Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 13

Chapter 13

Abinda Ake Gudu Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

amma ana dawowa kan Asmau sai kuka. Jafar yace Ummansu tace a zaneta idan bata yi karatu ba. Tunda ta fara kukan farko Abubakar yake kallonta. Dariya abin ya bashi sai da yaga taki denawa ta soma bashi tausayi. Malam Hadi yayi har ya gaji taki karatu sai kuka da rawar murya. Yace kowa ya fita banda manyan yayye. Suna tafiya ya nuna mata Abdulhalim da Abubakar "Waye a cikinsu kika yarda zakiyi karatun a gabansa tunda kin kasa a wurina." Tana daga kai suka hada ido da Abdulhalim ya hade rai. Da shine malamin zaneta zaiyi fes baya daukar rainin hankali. Da sauri ta nuna Abubakar. Malam Hadi yace "to Sadiq ka kwatanta gaskiya ka ji karatun. Ke kuma gobe ki tabbatar zakiyi a gabana ko na samo bulala". Da haka suka fita saura ita da Abubakar. Fuskarsa a sake ya fara tambayarta "shekarunki nawa Asmau?" "Shahudu" "Ashe ma kin girmeni da shekara takwas" Ta dan saki fuska amma muryarta bata dena rawa ba "so kake kace ka girmeni da shekara takwas dai" Yayi murmushi dama so yake ta saki jikinta "Haka ne, ni yanzu ina level two a BUK ina karanta computer science. Ke fa?" "SS1 nake a science class. Likita nake son zama" yadda take maganar yasan ba karamin son hakan take ba. "Very good, sai dai bakiyi kama da likita ba saboda tsoro yayi miki yawa. Likitoci kuma basu da tsoro". Yana kallon bata ji dadin maganarsa ba ya sake yin murmushi. "Kada ki damu akwai maganin tsoro. Shine ki daure ki rinka magana a cikin mutane. Babu mai yanka ki. Iyaka idan kinyi kuskure a gyara miki. Karatun Qur'ani karfin zuciya yake sawa ba ragwanta ba." Shiru tayi tana sauraronsa yana ta janta da zance. Sai karshe yace ta biya masa yaji. Da kyar ta daure hawaye wani na bin wani ta karanta. Kafin tayi rabi kukan ya dauke sai karatun ake ji. Tana kaiwa karshen surar yayi kabbara sannan ya sake karfafa mata gwiwa wurin bude baki a gaban jamaa. Da murmushi ta fito suka tafi gida ran Shema'u a bace saboda tasa sun dade. Tun daga wannan lokacin ko ta fara kukan idan Abubakar yana masallacin sai ta daure. Karshe dai sunanta ya koma Idon kuka saboda kullum sai tayi. Gashi ta tsani sunan. Haka rayuwa ta cigabar musu har lokacin bikin Nasiba. Gidajen biyu suna ta shiri duk da su Umma basu fi shekara daya a unguwar ba. Haka suka yi bikinsu lafiya kalau kamar dangin juna. Su Asmau an kara zama 'yan mata. Yanzu tana dan sakewa har ayi hira da ita. Wani lokaci da Umma zata Wushishi gashi basu yi hutu ba a nan gidan Mama Yalwa ta barsu. Abdulhalim ya tafi bautar kasa Jos yanzu Abubakar ne babba a gidan. Duk da yanayin karatunsa bai hana shi cigaba da zama daukar karatu a wurin malam Hadi ba. Duk cikinsu yafi kowa mayar da hankali akan karatun addini shiyasa Baba yake matukar ji dashi. Watarana an gama karatu kowa ya fita daga masallacin sai Asmau dake zaune tana kokarin kammala aikin da malam ya bata na fitar da hukuncin (NUUN saakina) a thumunin da ya biya mata ranar saboda washegari test gareta a makaranta karatu take son yi. Abubakar yana can wurin zaman liman yana tilawa aka soma iska mai karfi alamun ruwa zai iya sakkowa a kowane lokaci. Da dan gudunta ta tashi zata rufe tagogi kafin ta fita saboda kurar dake shigowa. Har ta gama rufewa Abubakar baiyi yunkurin tashi ba. A take kuma aka dauke wuta saboda wata tsawa da akayi mai karfi. A dan tsorace tace "Yaya Abubakar kazo mu fita kafin ruwan nan ya sauko" Shiru taji sai numfashinsa da ya kara karfi. Gabansa ta karasa sai dai duhu yasa bata ganinsa sosai. Wayarsa da ta taka ta dauka ta haska shi. Kwance yake numfashinsa yana sama-sama da kyar yake fita. Hannunsa daya kuma yana nuna mata aljihun wandonsa. Asmau duk ta rikice ta kuma fahimci abu yake so ta miko masa daga aljihunsa. To kuma Umma tayi musu gargadi sosai akan taba maza wannan yasa ta kasa tabashi ta fita da gudu a cikin ruwan ta shiga gidansu ta fadawa Mama Yalwa. Tare suka dawo har da Suwaiba dauke da irin filtilar nan mai batir. A kwancen dai suka same shi ya hada gumi idanunsa harda hawaye. Mama ta daga kansa ta dora a cinyarta a rude tace "ina inhaler dinka?" Aljihunsa yayi kokarin nuna mata. Tasa hannu ta dauko ta shaka masa. Asmau da Suwaiba suna tsaye suna yi masa sannu. Duk da haka numfashin bai dawo daidai ba. Mama tace a fadawa dreba yazo su tafi asibiti. Bayan fitarsu Asmau ta tafi gida ta sanar da Umma abinda ya faru. ABINDA AKE GUDU🙆🏽11 Batul Mamman💖 Rabe ne ya fito yasha sabuwar shadda sai kyalli take yi. Idonsa a kan Bara'atu da yanayin da ta shiga yayi dariyar mugunta. Don tsabar wulakanci yace "A'a bazawara kune a garin? Ya hanya?" Hawaye take yi wani na bin wani ta durkusa a gaban Hajjo "Nasan har mijina ya rasu baku taba kaunata ba amma Hajjo wallahi cin dukiyar marayu haramun ne. Gidan nan baku da hakki a kansa to a wane dalili zaku zo ku tare batare da izini ba". "Eh, lallai wuyanki ya isa yanka Bara'atu. Ni da gidan dana kike gaya min maganar banza." Hajjo ta amsa itama rai a bace. "Ko kinki ko kinso zama dole muyi a gidan nan. Idan bazaki iya zama damu ba sai ki bar min yaran ki kama gabanki." Yusuf mijin Anti Bintu yace "Anti kada ki sake cewa komai. Ai basu fi karfin hukuma ba. Kuma rabon gado ba hauka bane. Ki bari mu kwana yau gobe sai mu san abinyi." Mikewa tayi cikin zafin nama tana kallonsu daidai. Garzali banda taba babu abinda yake busawa. Rabe da amaryarsa suna tsaye suna mata kallon banza. Hannu tasa ta share hawayenta "Dama can saboda marigayi nake raga muku to amma wallahi yanzu an wuce wurin. Mu zuba ni daku shege ka fasa." Yaranta ta dakawa tsawa duk suka tashi daga gaban Hajjo suka bita cikin gidan. Hajjo da su Rabe kowa yayi tsit suna mamakin wai yau Bara'atu ke mayar musu da martani haka. ***** A cikin gidan dakuna biyu ta samu a bude ita da Yusuf da su Shemau suka rinka shiga da kayansu. Sai cikin dare tana zaune tana kallon 'ya'yanta na bacci ta rinka kuka. Washegari ko karyawa batayi ba suka fito ita da yaran suka hadu da Yusuf zasu tafi ofishin 'yan sanda. Rabe yana tsaye a waje yace " kinga basai kun wahala ba a bayan layin nan akwai gidan wani babban dan sanda. Maza ku tafi ku kai kara kada kuda ya rigaku." Basu kula shi ba suka wuce. Duk wani bayani sun gabatarwa 'yan sandan. Mutum hudu aka hado su dasu suka zo aka bukaci su Rabe su fita. Wannan muguwar dariyar yake yi ya dauko takardun gida sai gashi sunansa ne dana Shu'aibu a jiki a matsayin tare suka gina. Kuka sosai Bara'atu take yi tana karyata shi. Sai dai kuma bata da shaida. Bata san yadda akayi ya sami takardun gidan ba wanda a hannunta suke har akayi

Table of Contents

Chapters

103 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});