Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 27

Chapter 27

Abinda Ake Gudu Book 1 Complete Hausa Novel 1,198 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

na uku ta zauna kusa dashi cikin damuwa. "Baban Abba me ya faru ne? Allah Yasa ba laifi nayi ba." Dan murmushi Sada yayi yana kallon abar kaunarsa. "Ko kadan Maman Abba. Bari nayi wankan dai." Sai da ya gama cin tuwo sannan ya bata labarin Asmau mai zuwa kofar shagonsa. "Ni bansan daga ina take ba sai dai ta bani tausayi. Muna ganin kanmu kamar marasa arziki amma wallahi cikin rufin asiri muke akan wasu. Tsorona daya kada taje wurin wani mara imanin ya bata maganin." Rashida tace "to ai dama kaine kullum kake ganin kamar shagonka kadai baya wadata mu. Amma gashi yara hudu duk suna makaranta kuma bama rasa abinci. Idan bazaka damu ba gobe sai na kawo maka abincin da kaina na ganta. Kila idan na bata shawara ta hakura da zubar da cikin ta koma gida". ***** Asmau ta dauko robar da Uwargida ta bata. Tana son sha kuma har ranta bata son zubar da cikin. Dama gudun zubarwar yasa ta fito daga gida. Dan motsin nan da taji ya sa ta kara son abinta. Robar ta dauka ta zubar da kadan a bakin rariya sannan ta mayarwa Uwargida. Bakin Uwargida a washe tace " nan da wayewar gari ma yana iya zubewa. Kinyi kyan kai 'Yar Da6as." Yau ma ta riga Sada zuwa shagonsa. Ita kanta bata san me ya dawo da ita ba. Da yazo har kasa ta durkusa ta gaida shi. Ya amsa mata fuskarsa babu yabo babu fallasa. Yayi mamaki da ko sau daya bata sake batun maganin ba. Tana dai zaune ne kawai a gefe guda. Wuraren shabiyu wata mace ta sha katon mayafi ta iso kafar shagon da flask din abinci. Matar tayi mata murmushi Asmau ta gaisheta. Sada ya fito daga cikin shagon yace "wannan ce yarinyar". Rashida taji tausayin Asmau ba don komai ba sai don yanayin da ta ganta. Har wani wari take yi saboda rashin wanka. Sada yace su shigo ciki ya dan kara kofar alamun ko anzo kada a shiga. Asmau na zaune a kasa a gabansu Rashida tace ta fada musu daga ina take kuma ina uban dan dake cikinta. "Kada kiyi mana karya domin kuwa Allah Yana kallonmu". Karo na biyu kenan tana bada labarinta. Kafin ta gama Rashida tayi ya6e ya6e da hawaye don tausayi. Mata da yawa idan an tambayesu game da ciki a irin wannan yanayin sai suce fin karfi aka yi musu. Amma wannan yarinyar ta zabi ta fada musu abinda suka fi tunanin gaskiya ne. Wato biyewa rudin shaidan da son farantawa masoyi. Shi kansa Sada yaji tausayinta matuka. Lokaci guda tarbiyarta ta wargaje a dalilin kawa da kafafen sada zumunta. Waje suka ce ta fita ta jira su. Muhawara sukayi inda yace su mayar da ita gida Rashida tace kada ta koma sai ta haihu ta yiwu iyayen su yafe mata idan suka ga dan a hannu. Duk da suna tsoron halin Dan Adam yanzu. Kayi masa rana yayi maka dare amma zukatansu sun amince da taimakonta musamman ma suna jin tsoron kada ta zubar da cikin ta fada sana'ar banza. Sada ya rufe shagon suka ce ta biyosu. Babu musu tabi bayansu tana adduar Allah Yasa alkhairi ne a tattare da mutanen. ABINDA AKE GUDU🙆🏽22 Batul Mamman💖 Zahra 'yar Rabe ta biyu ke zaune tana waya da mahaifiyarta Laraba wadda Raben ya dade da saki. A hirarsu ne take fadawa Laraban zancen haihuwar Shema'u wadda akayi kwanaki goma da suka wuce. Tun ranar da akayi haihuwar Yassar yazo ya sanar sai akayi rashin sa'a Rabe da Zahran ne kadai a falon. A wurin ya ci mutumcin Yassar sannan yace da Zahra kada ta fadawa Hajjo babu mai sake zuwa gidan Bara'atu. Laraba duk ta gama sauraren 'yarta tace mata su kara hakuri da babansu. Dama ita ta bata shawarar dagewa taje bikin Asmau. Tace idan ta shigo Kano zata zo tayiwa Umma jajen abinda ya sami Asmau da barkar Shema'u. Hajjo tana tsaye a bakin kofa ta fahimci duk hirar Zahra da Laraba. Ko kwanaki uku da suka wuce sai da ta cewa Rabe wai har yanzu Shema'u bata haihu bane yace wa ya sani ne. Bara'atu da bakin hali kuma. Ta rasa gane irin wannan tsana da yake nunawa iyalin dan uwansa. Dakinta ta koma jiki a sanyaye ta dauko mayafi ta fito. Karnukan Garzali ne suka yo kanta ba shiri ta koma ciki. Dakinsa ta je yana bacci ta daka masa duka a baya. Shi babu arabi babu boko sannan auren ma ya gagara. Sai dai yaje yawo ya dawo gida ya kwanta bacci. A zabure ya bude ido ganin wace ke kansa ya turo baki "haba Hajjo yau kuma me nayi zaki doke ni? Na rantse jiya ban sha komai ba. Sansana bakina kiji". Ta kau da fuska "Allah Ya tsareni na kai hancina bakinka. Ni tashi ka daure karnukan ka fita zanyi. Ka mayar mana da gida kamar dandalin 'yan daba. Motsi kadan sai haushin karnuka." Dariya yayi tare da zuro kafafunsa zai sauko daga kan gadon. Daga bayanta taji ance "ina zaki je?" Gabanta sai da ya fadi don firgici ta juya tana kallon Rabe wanda bata san ya dawo gida ba. Murmushin da bai kai zuci ba ta kakalo "Yaushe ka dawo Alhaji?" Ya basar da tambayar. "Naji kina cewa zaki fita". Kamar ba mahaifiyarsa ba duk ta kidime tace "uhmm dama gidan waccan mara kunyar zani. Ashe Shema'u ta haihu shine ko ta aiko mana. Ai bata isa ta rabamu da 'ya'yan Shuaibu ba ko?" Rabe ya soma jin tsoron yawan ambaton su Bara'atu da take a kwanakin nan sai ya dan dake. "Yanzu a kanta zaki fita cikin ranar nan? Ki kyaleta kawai da halinta. A ce har 'yar dan uwana ta haihu bamu ji ba kawai don bata daukemu a bakin komai ba. Ni daga yanzu na kafa doka babu mu babu su. Tunda haka ta zaba kowa yayi ta kansa." Hajjo ta jinjina kai tama mamakin yadda yake gilla mata karya haka. Ta tabbatar maganar da Zahra keyi a waya ba karya bane. Ta sake gwada sa'arta ta hanyar cewa "Wai dama nace muje ko tare da kai ne mu dan zagesu mu huce haushi" Juyawarsa yayi don kada ta sake jan zancen. " Koma daki kiyi kwanciyarki ki huta Hajjo". Tana kallo ya tafi itama ta juya zata koma dakinta. Hawaye ne ya sauko mata wanda bata san dalilinsa ba ta goge da habar zaninta sannan ta koma daki. Garzali da bai tanka musu ba yaji tausayin mahaifiyarsa ya ratsa shi. Ya rasa dalilin da yasa dukkansu har Yaya Abu da Yaya Lami basu da katabus sai abinda Rabe yace. Amma zaiyi kokari ko yaya ya kai Hajjo taga jikokinta tunda wulakancin da suke musu yasa suka dena zuwa gidan. A daki Rabe ya kasa sukuni. Sagira na masa magana ya daka mata tsawa. Dama ba wani matsayi gareta a wurinsa ba. A duniya babu matar da yake matukar so kamar Bara'atu duk da girma ya kamasu. Sai kuma batun Malamin tsibbunsa. Dama lokaci lokaci yake sake biya a toshe bakin Hajjo da 'yan uwansa. Yanzu idan asirin ya karya yasan Hajjo cewa zata yi su tashi daga gidan Bara'atu ta dawo. Matsalar idan

Table of Contents

Chapters

103 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});