Chapter 101
Chapter 101
su Umma na koma motarsu" "Wani abin ne ya faru kike son canja wurin zama?" Shiru tayi sai kuma ta soma hawaye. Nan da nan hankalin Asmau yayi mugun tashi. Shi kuwa Yassar hannunsa rawa ya soma yi ya sami gefen hanya yayi parking din motar. Asmau tana ta tambayar me akayi mata sai ji tayi Yassar yace "Bilkisu" Ta dago kai idanunta sun kumbura sunyi jawur. "Idan ba cewa zakayi kana sona ba ka rabu dani. Allah zai bani wani" Asmau ta hangame baki cike da mamaki. Rashin kunya a gaban masoyi ta yarda gadon gidansu Jikamshi ne. Anya Bilkisu bata manta tana bayan motar ba. Allah Yasa ma Amatullah tayi bacci. Yassar yace "kema kinsan ina sonki don Allah ki share hawayen kinga a hanya muke" Ta murguda masa baki "a haka ne kana sona tunda ka tafi ba waya ba text sai na gaji na nemeka. Kuma kaki fadawa kowa balle a fara shirin bikinmu sai iya zuwa bikin wasu" Asmau ta shiga tafa hannu a hankali tace "Bilkisu kwantar da hankalinki naji komai muna dawowa in sha Allah magana zata je gaba kinji ko. Kinsan Yassar din ne akwai tsoron mata" Dora hannu Bilkisu tayi a kanta tare da jan mayafi ta rufe fuska. Wallahi ta manta da Asmau a motar. Haushi Yassar dinta ya bata tun bikin su Asmau da ta samu yace yana sonta bai kara waiwayenta ba. A nasa bangaren shima wata matsananciyar kunya yaji. Ko Bilkisun ba don baya sonta yake kin nemanta ba. Shi bai san me zai rinka fada mata ba a waya ko text. Shiru suka yi su biyun Yassar ya tayar da mota Asmau tana ta dariya. Abu yayi dadi zumunci zai kara kulluwa tsakaninsu. Tsabar murna a lokacin ta turawa Jikamshi text tana fada masa. Shi dinma ya nuna farincikinsa sosai yace sai sun dawo. Bilkisu dai har aka isa Jos bebiyar dole ta zama. Ansha biki Zulaiha ta sake bawa Asmau labarin yadda suka kare dasu Zinaru dama ta sanar da ita a waya. Asmau tace ina ma tana wurin ta ga idanun Zinaru mai son kudin tsiya. Daga nan suka koma hirar cikin Asmau da kuma Alh Najib da yake jiran Zulaiha ta gama iddah. Ita dai tace bata da ra'ayin aure tasha wahala a wancan ga yara har shida waye zai dauketa tare dasu. Shawara Asmau ta bata kada ta bari dama ta kubuce mata wurin yiwa babanta biyayya. Ranar Asabar da sassafe suka dauko amarya suka taho Kano da ita. Washegari akayi dinner sannan aka wuce da ita Shanono inda zatayi sati sannan su tafi Zamfara da angonta. Ranar da suka dawo Col. Ishaq kamar ya cinye Asmau. Kwanaki uku kawai ji yake kamar ya dade sosai basa tare. Itama tayi kewarsa domin kuwa duk kulawar da take samu bata kai tasa ba. ***** Cikinta na da wata shida ya fara siyayyar kayan baby. Wani lokacin yaje da ita wani lokacin kuwa sai dai taga ya shigo da kaya. Tun daga gadon yara (cot), kayan sawa da duk wani abin amfani ya tanada. Ita har gajiya tayi da cewa ya barsu haka. Mutum mai shekarunsa zaiyi haihuwar fari sai dai a zuba ido. Wata rana ya dawo daga aiki a gajiye yake fada mata ta hada kaya jibi zasu tafi Port Harcout an tura shi aiki na wata daya. Amatullah sun fara hutu sai a kaita gidan Umma kafin su dawo. Asmau ta zauna ta hada musu kaya washegari suka kai Amatullah gidan Umma sannan suka je yiwa Hajiya sallama. Tunda ya fara bayanin abinda ya kawo su Hajiya ta dakatar dashi. "Babu inda zaka je min da ita da wannan cikin. Wa kuke dashi a can da zaka kaita cikin arna ka ajiye. Idan haihuwa tazo yaya zaku yi?" Yace "Hajiya akwai musulmai kuma da sauran lokacin haihuwar har maje mu dawo" "Kasan Allah babu inda zata je. Ko dai ka fasa tafiyar ko kuma ita ta zauna a nan ko can hotoro. Wannan karon ba kyaleka zanyi ba irin yadda ka tabayi min har na bari kuka koma gida" Asmau kanta na kasa Col. Ishaq yaki shiru don ba karamar cuta bace gareshi tafiyar wata daya babu matarsa. Hajiya ta dage harda kiran Umma. Itama Umman tace abinda ta gani kenan da suka kai mata Amatullah sai dai batayi magana ba. Hajiya tace ta gama magana shawara na garesu. Jiki babu kwari suka tafi gida. Asmau tayi ta bashi baki akan yayi hakuri ya dena nuna bacin rai amma ya kasa. "Matar Jikamshi wata daya ba sati bane. Ta yaya zanyi kwanakin nan ni kadai bayan na riga na saba da yin komai tare dake" Idonta na shirin zubo da hawaye tace "kayi hakuri kaima kasan abinda ta fada domin amfaninmu ne. Bazaka iya fasa tafiyar ba? Wallahi bana son kayi min nisa" Kuka ta soma yi ya rungumeta "bani da yadda zanyi ne. Umarni ne daga sama" A ranar ko kadan basuyi bacci ba sai aikin rarrashin juna. Tayi ta masa kuka har muryarta ta dashe. Bayan ya dawo daga sallar asuba ya hada mata kaya a wani akwatin. Ko abincin kirki sun kasa ci haka suka fita ya kaita gidan Umma ya wuce office. Daga nan dreba ya kaisu airport su hudu suka tafi. Harda Hussaini wanda idan sun dawo za'ayi bikinsa da Walida. Sai da ya kusa sati sannan ta warware ta dena zaman daki. Umma tayi dariya kawai. Safe, rana da dare aiki yana yi masa sauki sai waya. Kafin su kwanta kullum sai anyi video call yana kallonta da cikinta da kuma princess dinsa. **** Kwanci tashi saura kwana biyu ya dawo gida. Ita da Sabira suka je ta tayata gyaran gidan domin tayi nauyi sosai. Harda kitso da kunshi Jikamshi zai dawo. Ranar da zai dawo kuwa karfe tara na safe ta gama shiri zata tafi gida. Umma ta rinka ja mata rai tana dariya a ranta yadda Asmau take ta kallon agogo. Sai goma da rabi ta fito ta ajiyeta a gida ta wuce office. Amatullah tana gidan Nasiba tana karasa hutunta. Karfe daya taji motarsa ta bude kofa da sauri. Col. Ishaq ya tsaya yana kallonta. Ciki yayi girma sosai. Ita ma shi take kallo har wani jiki ya danyi ta fasa rungumeshi taja da baya. Rufe kofa yayi yana binta "haba Matar Jikamshi kada kiyi min rowar kanki. A tausayawa bawan Allah" "Shine kayi kiba duk da baka gani na ko" Ya janyota yana murmushi "yau 'yan rigimar suna kusa ne? Bayan wata daya not even a kiss sai korafi zan samu. Bari na koma tunda bakiyi murnar dawowata ba" Kin sakinsa tayi ta rungumeshi sosai tana kuka "bazaka kara tafiya irin wannan ka barni ba. Kullum da kyar nake bacci" Yayi kissing dinta yana kallon fuskarta "na sani my sweet Asmau. In sha Allah next time kafata kafarki." Daki suka je zai shiga wanka yaga tana dan runtse ido ya tambayeta ko meye tace kafarta ce ta dan rike. Ranar sallah kawai ke fitar dashi daga gida. Kowa yana kokarin nunawa dayan irin yadda yayi kewarsa. Makale suke da juna kamar ranar aka kawo masa ita. A haka kuma tana ta dan jin ciwo daga mararta zuwa baya amma tana cijewa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103