Chapter 22
Chapter 22
kazanta saboda karatun labari wanda a ciki tsafta da kula da miji ake koyarwa? Wata ma bata girkin akan lokaci sai taji mijinta ya kama kofar gida zai shigo ta ruga kicin. Wata ta bar yaro da kazanta har sai ta gama karatu. Wata kuwa da wayar zata shigo bandaki tana biyan bukatarta tana karanta labari. Idan hakane karatun labaran masu dauke da darussa bai amfanemu da komai ba sai kasala, ganda da kazanta. Ki zama mace mai tsari a rayuwa komai kiyi shi a lokacin da ya dace. Babu abin takaici sai kinga mace da tsakar dare ko asubar fari tana cigiyar novel ga mijinta a gefe bawan Allah kila yaso ta bashi hakkinsa na aure ma amma ya hakura don kada ya takurata. Idan mara hakuri ne ayi ta samun sabani. Asmau nasan Yaya Bara tana kokarinta a kanku. Gashi aiki yayi mata yawa duk don biya muku bukatu. Kada ki watsa mata kasa a ido da dabi'u marasa kyau kinji ko". An tuno da Idon kuka ana mata fada tana sana'arta. A take tayi nadamar daukar shawarar Walida wanda yasa take yin abubuwan da a da can tasan basu dace ba. Kukanta ya tsananta da ta tuna tabbas irin yadda suke gudanar da soyayyarsu yanzu yana da alaka da canjin da ya fara tasowa daga gareta. Wai ita ce suke rungumar juna da Abubakar. Abubakar dinta mai riko da addini ta zama sanadiyar da suke munafuntar kawunansu da iyayensu. Anti Bintu ta cigaba da yi mata nasiha mai ratsa zuciya sannan ta tashi. A ranar ta ga canji sosai a wurin 'yar tata. Asmaunta ta da ta dawo. ***** Abubakar na kwance a daki yana kallon wasu hotunan Asmau. Tun daren jiya da ta turo ko baccin kirki ya kasa yi. Yau da ciwon mara ya tashi irin wanda ake samu idan sha'awa tayiwa mutum yawa. Ya rasa abinda yake masa dadi ko office ya kasa zuwa. Shawara ya yanke zaije Zariya a ranar ko dan yaya yayi dan abinda zai kwantar da kwadayinsa. A yadda yake sonta bazai iya neman wata matar a waje ba. Ita dinma bashi da niyar ayi mai gabadaya ta bakin Qasim. Dan dai abinda ba'a rasa ba yadda sai samu yaji dadi. Da wannan shawarar ya tashi yayi wanka ya hau shirin zuwa Zariya. ABINDA AKE GUDU🙆🏽17 Batul Mamman💖 Kafin ya fito ya kira Asmau a waya ya sanar da ita zai zo. Jikinta a sanyaye ta amsa masa don ita yanzu kunyar ganinsa take yi. Ko ba'a fada ba daga nasihar Anti Bintu tasan cewa duk abinda ya faru laifinta ne. Har daki taje ta sanar da Anti Bintun zai zo kamar yadda ta saba. "Ki dora abinci dashi amma ki bar dan waken sai gobe don bazan bawa suriki dan wake ba" Ita da Asmau duk dariya sukayi sannan ta wuce ta dora shinkafa da miya. Wuraren karfe uku ya iso Anti Bintu tazo suka gaisa sannan ta basu wuri. Yau Asmau hijab ta saka dogo har kasa fuskarta babu kwalliya sai hoda da kwalli. Jikinta duk babu kwari tayi nadama sosai. Abubakar kuwa tamkar ya hadiyeta da kallo. Anyi sa'a yaran gidan suna ta gilmawa a falon. Da laasar suka tafi islamiyya shi kuma yaje yayi sallah. Ana idarwa ya dawo ya kalli Asmau dake zaune a can gefe. "Asmy dawo nan kusa dani nafi jindadi". Ya nuna kujerar gefensa. Tashi tayi kamar wadda kwai ya fashewa a ciki. Tana zama ya kama hannunta ya rike yana lumshe idanu. Can kasa take jin muryarsa "I love you so much Asmy. Ina ma anyi aurenmu kiga irin abinda nake nufi." A kwanakin baya har so take ya rike mata hannu amma yau sai taji ta tsani hakan. Tana son nuna masa kuskuren abinda tasan ya fita sani amma dole tabi lamarin a hankali kada yayi mata mummunar fahimta ko yace ta mayar dashi dan iska. Har lokacin tafiyarsa yayi bata iya sakin jiki dashi ba. Shi kuwa gabadaya ya kasa samun nutsuwa. Bakin motarsa da ya ajiye a wajen gate ta raka shi ai kuwa yana bude motar ya rungumota jikinsa. Dama layin ba mutane sosai saboda unguwar bata gama cika ba ga duhun dare. Wasu hawaye masu zafi Asmau taji sun taho mata ta hadiye. Dole ta sami lokaci suyi magana da Abubakar akan wannan abin. Rungumar da take jindadi daga gareshi yau bata so. Tana wannan tunanin taji yayi mata abinda bai taba yi ba. Abinda take ta mararin faruwarsa. Bakinsa ya hada da nata yayi mata rikon da bazata iya kwatar kanta ba koda tayi niyya. Hawayen da take boyewa ne suka sakko ganin Abubakar tamkar baya cikin hayyacinsa. Abubuwan da yake mata sun fara wuce gona da iri. Ba shi ya saketa ba sai da don kansa yaji hankalinsa ya fara dawowa gareshi. Ganin tana kuka ya soma bata hakuri. "Asmy kiyi hakuri please. Na rasa dalilin da yasa nayi miki hakan. Ki sani ina sonki tsakani da Allah kuma in sha Allah bazan sake kwatanta miki haka ba sai munyi aure". Yadda yake maganar sai ya bawa mutum tausayi. Tabbas baya son abinda yake yi sai dai karfin sha'awarsa da tsananin rudin shaidan yasa ya kasa hakuri. A hankali ta share idonta "Yaya Abubakar don Allah mu dena irin wannan abin kaga babu kyau." "Na sami Asmy, ni kaina na rasa gane yadda akayi muka fada ga wannan masifar. Ki share idonki kinji matar Abubakar". Kafin ya tafi sai gashi ta sake sosai hankalinta ya kwanta. Suka rabu zuciyar kowa tana nata sake saken. ***** Abubuwan da suka gudana tsakanin Abubakar da Asmau su suka rinka yi masa yawo a kwakwalwa. Yayi tunanin zaiji saukin sha'awar dake damunsa sai abin yayi tsanani sosai. Kullum cikin mafarkinta yake yi. Baccin kirki ya gagare shi sai tunanin yadda zaiyi ko dai a matso da aurensu ko ya kashe yunwarsa ko sau daya ne. A nata bangaren hatta hirar da suke yi a waya yanzu tana kame bakinta daga hirar da bata dace ba. Ta tarkarta tunaninta kaf zuwa lokacin aurensu ko sa sami nutsuwa da kwanciyar hankali saboda tasan duk su biyun yanzu a matse suke da ganin wannan lokacin. Bayan kwana biyu ya sake zuwa wannan karon ko waya baiyi mata ba. A hirarsu da Anti Bintu ya nemi izinin ranar asabar da Asmau zata tafi zai zo ya kaita da kansa a cewarsa baya so ta shiga motar haya. Anti Bintu tayi shiru na dan lokaci saboda ba haka sukayi da yayarta ba. Dama tasha za'a kaita ta tafi saboda motar Kawu Yusuf tana gareji wurin makanike. A duk dan tunaninta bata hango wata matsala ba duba da irin siffa ta kamala da suke dashi su biyun. Asmau kanta bata ji komai ba saboda yau hirarsu duk irin ta da ce. Cikin nutsuwa da kiyayewa. Soyayya mai tsafta irin wadda masu yinta basa son rabuwa da juna. Kwanaki ukun da suka zo kafin tafiyarsu Abubakar yaji babu dadi. Har wani zazzabi ne ya kamashi saboda ji yake tamkar ana hura masa wutar sha'awar kasancewa da mace. A yadda yake ji ko ba Asmau bace wannan karon zai iya nema. Ranar da zasu tafi wurin karfe goma ya iso. Asmau da yaran harda dan kukansu
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103