Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 52

Chapter 52

Abinda Ake Gudu Book 1 Complete Hausa Novel 1,197 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

tayi abinda zai bata masa rai. Amma laifinsa ne don ranar da suka dawo yace zai zo shiyasa yau ta fito wurin Qasim da kwarin gwiwarta. So take yi ta fara sallamarsa sannan shima wanda yayi nasarar samun soyayyar tata ta nemi su rabu. Duk iya tunaninta karatu ne kawai mafita garesu ita da Amatullah. Qasim bawan Allah ya kula da yadda ta canja lokaci guda har ya fara tunanin waye a motar. Motar ya rinka kallo da Asmau. ****** Kamar ya juya haka ya rinka ji sai dai kuma hakan ba girmansa bane tunda har ya shigo gidan. A zuci ya karanta *Hasbunallahu wa ni'imal wakeel*har yaji bacin ran ya ragu sannan ya fito yana zuba _kamshi_. Taku yake daidai har ya iso kusa dasu. Kamshin turarensa da yake sanya Asmau nishadi ne ya fara ziyartar ta. Taji bugun zuciyarta ya tsananta. A iya saninta da Jikamshi baya boye magana ko gaban waye. Bata san me zai ce a gaban Qasim ba, mutumin da bai cancanci wulakanci ko kadan ba daga gareta. Yana karasowa ya saki fuska duk da ta ciki na ciki ya mikawa Qasim hannu yayi masa sallama. Qasim ya karbi hannun shima cikin fara'a ya tashi suka gaisa. Sai kuma suka kalli Asmau suna jira ta gabatar dasu. Tsuru tayi da ido kamar wadda tayiwa sarki karya. Da kyar ta saita kanta tace "Yaya Qasim ga baban Amatullah da nake fada maka. Col. I M Jikamshi." Sake kama hannunsa Qasim yayi yana murmushi "naso ace har gida nazo na sameka domin kara mika godiya bisa taimakon da kayi mana. Allah Ya saka da alkhairi Ya bada lada. Ashe manyanmu ne masu tsaron kasa. Bari na baka girmanka yallabai." Gyara tsayuwa Qasim yayi ya daidaita kafafunsa sannan yayi saluting Jikamshi. Shima murmushi yayi ya tsaya a attention ya mayar masa da salute din duk suka yi dariya banda Asmau. Col. Ishaq yace "ka kirani Ishaq kawai. Asmau bata iya kiran sunana kai tsaye ne shiyasa kaji tana maka kwana kwana ko" ya fada yana mata kallon da ke kara kashe mata zuciya. Ta sunkuyar da kanta kawai. Abinda take gudu kenan ya bata kunya a gaban Qasim. Ta daure tace "ga Yaya Qasim shi dan sanda ne" "Allah Sarki, its a pleasure meeting you. Ai ta bani labarinka. Kune manyan ai muna bayanku. Baka ji ana cewa abokin kowa dan sanda" Col Ishaq ya fada yana kara kallonsa zuciyarsa fal kishi yana ta kokarin dannewa. "Nima ta fada min yadda ta hadu daku. Muna kara godiya." "Kada ka damu ai yiwa kai ne. Amma me kuke yi a waje haka ga kura? Ina tsammanin damuna ta kusa tsayawa dai" yadda yayi maganar Asmau ce ta fahimci da biyu yake yi. Shi kuwa Qasim ya dan sosa kai yana dariya. Ko babu komai Jikamshi ya girme shi "Yallabai kenan. A tayamu addua dai muna nema ne" Wani abu ne ya tokarewa Col Ishaq makoshi yaki sauka kasa. Wai ya taya shi addua. A zuciyarsa yace (Allah Yasa kada ta taba yi maka soyayya irin ta mace da namiji.). Abu daya ke yi masa yawo a ka shine kada Asmau ta juya masa baya. Wannan Qasim din wani sanyi ne gareshi mai sa mutum yaji dadin mu'amala dashi. A fili kuwa murmushin yake yayi "ah to bari naje naga Amatullah sai na tafi. Dama ita nazo gani kewarta ta isheni" daga nan gefe ya matsa ya kira Yassar. Bai dade ba ya fito ya shigar dashi ciki. Ransa a bace da ya hango Asmau da Qasim yana taya Jikamshi kishi. Bayan sun shiga ciki Qasim yayi ta yabon saukin kai irin na Col. Ishaq "kamar ba babban soja ba, ji yadda yake jana kamar ya dade da sanina" "Uhmm" kawai Asmau tace a sanyaye. "Asmau wace shawara kika yanke mana?" Ta dago kai a hankali "Yaya Qasim ni dai da mun bar maganar nan" "Kinga Asmau duk abinda kike gudu baki da tabbas a kansa. Yana iya faruwa ko kuma kiga bai faru ba. Haka nan ma masu aure na fuskantar matsaloli musamman mata daga dangin miji. Bance komai zai tafi mana daidai ba amma nayi alkawarin tsaya miki har karshen rayuwata" Tausayinsa ta kara ji. Banda tsoronta na aure ko kadan bata jin son Qasim sai tausayinsa saboda yadda yake mata. "Ka dan kara min lokaci, ban samu nayi maganar da Umma ba" "To babu komai, shi garaje ai bashi da alkhairi. Duk yadda kuka yi ki sanar dani. Sannan zan kiraki idan na koma gida in sha Allah. Akwai keke da na siyowa Amatullah bari na dauko yana bayan mota" "Nagode" "Wai kin gode, mutum da 'yarsa? Shiga ciki bari na dauko" Da sauri sauri tayi shige. ***** Daga kallon kofa sai agogo Col. Ishaq yake yi tunda ya zauna hankalinsa baya tare dashi. Ji yake kamar ya koma wajen ya hana zancen. Hajjo ce take kokarin janshi da hira sai Amatullah tana bashi labarin Wushishi. Yassar kuwa kamar yaje ya dauko Asmau yake ji. Da ta shigo Jikamshi ya kafe ta yayi da ido ta kasa kallon inda yake kawai sai ta shige dakin Umma inda suke ta hada kaya ita da Ainau zata koma gidanta washegari. Qasim ya shigo da keke mai kyau na yara. Amatullah sai tsalle da murna. Tana ta cewa ta gode kamar yadda Umminta ta koya mata. Hajjo ta dubi Col Ishaq "da kai da Qasim kuna shagwaba yarinyar nan da yawa. To ni ina nawa keken?" Suna dariya Yassar yace "kada ki damu ni zan siyo miki irin mai katuwar tayar gaban nan na zamaninku" Umma ta fito tayi godiya sannan Qasim yayi musu sallama ya fita. Sai da suka ji tashin motarsa Col Ishaq shima ya tashi yace da Amatullah ta kira Umminta su gaisa. Umma ta jinjina kai tunda ya shigo dazu ta kula ransa a bace yake yana dannewa. Gaskiya akwai matsala nan gaba sai dai fatan Allah Ya zabawa Asmau mafi alkhairi cikinsu. ***** Tana kwance akan gado har wani zazzabi ke neman kamata saboda tunani Amatullah ta fada mata sakon babanta. Ta dan zaro ido "Baba Qasim ya tafi?" "Eh ya tafi kuma ya kawo min keke mai kyau" "Kinyi masa godiya ko" "Nayi masa Ummi" "Muje kiyi wasa kafin lokacin bacci yayi" ****** Baya falo da ta fito sai ta saka takalmi ta fita waje. Tsaye yake a jingine da motarsa yana danna waya ta hasko fuskarsa. Kamar mai taka kwai haka Asmau ta karasa gabansa. "Ina wuni" Muryarta tana masa dadi, wani irin sonta yake kara ji yana shigarsa. Sai dai kishi yasa ya kasa amsa gaisuwar. "Asmau wallahi ina da kishi sosai. Kada ki bari na kara ganinki a yanayi irin na yau. I can't take it" Ta kara sunkuyar da kai da jin furucinsa. "Kinga ki dago kanki ki kalleni magana zamuyi" Mayafinta tasa ta rufe fuskarta gabadaya. kunyarsa take ji. "Kina so na bude fuskar ne da kaina?" Ta girgiza kai da sauri "To ki bude da kanki kafin hakurina ya kare" Hannu tasa ta bude fuskar tare da dagowa a hankali. Fuskarshi ta bata tsoro saboda babu digon wasa "Jiranki da nayi a falo dazu yana cikin lokutan da bazan manta ba a rayuwata. Zuciyata bazata juri ki hadani

Table of Contents

Chapters

103 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});