Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 62

Chapter 62

Abinda Ake Gudu Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

basu tausayi. Ace har rubutun cikin waya ya isa ya sa mutum aikata zina. Abin da ban tsoro da firgici saboda babu wanda ya isa ya tserewa kaddara sai dai komai akwai sila. Hajiya Lubabatu tace tunda zata je dubo Amatullah tana so dukkansu suyi mata rakiya. Kukan Bilkisu suka ji Hajiya ta tashi da kanta sai dai kafin ta fito Bilkisu ta koma dakinta tana kuka. Bata taba sanin wannan labarin ba. A iya tunaninta baban Amatullah ya rasu ne ko ya saki Asmau. Tsoro ne ya kamata saboda akwai wani saurayinta da suke chatting a facebook. A hankali ya fara sako mata zantukan banza tun bata amsawa har ta dan fara sakewa yanzu. Wai har ya iya tambayarta ta kwatanta masa kayan baccinta da daddare. Tayi saurin dafe kirji, yanzu idan da abin yayi nisa kila itama ta shiga sahun masu bawa samari jiki. Kuka take sosai tana tausayawa Asmau kuma har ranta tana fatan Uncle Ishaq ya aureta ko don ya rufawa rayuwarta asiri. Sabon saurayin da suke dan satar kallon juna dashi ta kira a waya tana sheshshekar kuka. Numbar ma a wayar Uncle ta dauka batare da saninsa ba. Da sallamarsa ya dauka cikin muryar da ta dashe da kuka tace "Yassar ne?" ABINDA AKE GUDU🙆🏽45 Batul Mamman💖 Mamaki ne ya kama Yassar, kamar ya san muryar amma bashi da tabbas. "Da wa nake magana don Allah?" "Bilkisu ce" Tsorata yayi, shima yana neman numbarta amma yanzu da ta kirashi da alamun kuka sai yaji hankalinsa ya tashi. "Bilkisu me ya faru?" To me kuma zata ce masa? Tausayin kawunta take yi amma tana tsoron yi masa shishshigi. Uncle Ishaq yana da dadin sha'ani amma babu mai son ganin bacin ransa. Fasa maganar tayi na son ta roke shi ya lallaba yayarsa kada ta ki Uncle dinta tace "babu komai, anjima zamu zo duba Amatullah" tayi masa sallama ta ajiye wayar. A ransa yasan don zasu zo ba shine dalilin kiran ba. Tashi yayi ya shirya ya tafi asibitin. Zai jira su zo ya sami damar tambayarta. Ko dai ta lura da yawan kallonta da yake yi ne? Yayi murmushi, tun zuwansa gidansu na farko ranar da kare ya biyo Asmau ya fara jin wani abu game da Bilkisu. Sai dai duk hayaniya ta Yassar bai taba yin budurwa ba. Ta nan bangaren tsoro ne dashi kamar farar kura. ***** Col. Ishaq na shiga dakinsa ya fada kan gado ko takalmi bai tsaya cirewa ba. Kansa ne yake wani irin ciwo kamar ana buga masa kusa. Ga zuciyarsa ta gama tafasa da bacin rai. Wai yau shine kannensa har da Mussadiq dan karamin cikinsu suke fada masa magana son ransu. A gidansu akwai tsari na girmama na gaba sosai. Sun tashi da so da kaunar juna. Lalurar kowa tare suka haduwa suyi maganinta. 'Ya'yan Ismail biyar duka maza karamin ma bai shekara ba. Amma saboda yadda suke bashi girma duk shi yake sakawa yaran suna. Haka yaran Dahiru guda uku. Gidansu gwanin sha'awa baka ce babansu ya dade da rasuwa ba. Amma yau akan auren Asmau duk sun ture wani girmamawa da shakuwa kowa ya fadi son ransa. Da akanta kadai suka tsaya ya tabbatar da har yanzu yana dakin suna cacar baki. Sai gashi saboda irin rayuwar Asmau ta baya har gori Ismail yayi masa. Gori da abinda yafi so a rayuwarsa, haihuwa. Shi da kullum yake kwantarwa da yayansa hankali. Kafin rabuwarsa da Badariyya ma yaransa biyu manyan a wurinsa suke. Dumi yaji a idonsa yayi saurin mayar da hawayen dake neman zubo masa. Duniya ta Allah ce kuma ba wurin tabbatar bayi ba. Da ace babu lahira sai yace rayuwar Asmau ta wuce abinda ake gudu domin komai daren dadewa sai an ambaceta ko 'yarta a matsayin mazinaciya ko 'yar zina. Ya tabbatar ko shugabar malaman duniya Asmau ta zama sai kaji mutane suna cewa "Wance kamar ba ita ce tayi cikin shege ba" "Ji yadda take nuna mana ita ta Allah ce kamar bamu san tarihinta ba" Amatullah kuwa ita ma bazata tsira ba. Komai kyawun rayuwarta sai an ce "kaga wance kamar ba shegiya mara uba ba" "wance fa da kuke gani babu aure aka haifeta" Irin haka da maganganun da suka fisu zafi mutane zasu fada a kansu. Babu ruwan kowa da yaya tsakaninta yake da Allah. Shin ta tuba ko kuwa. Zina ta zama mugun tabo mara gogewa. Tashi yayi ya zauna tare da daga hannuwansa sama. Hawayen da baya son yi ne suka zubo masa "Ya Allah Ka karbi tuban baiwarKa Asmau da sauran al'umma da suke cikin hali irin nata. Allah Ka basu rayuwa mai albarka su ji dadin tuban da sukayi bisa laifukansu, Ya Allah Ka bata miji nagari wanda zai zame mata alkhairi kuma mai wanke mata bacin rai da bazata taba dena fuskanta ba a dalilin kuskurenta na baya. Ya Allah Ka karemu da sauran musulmi daga fadawa alfasha kowace iri ce. Amin" Sai yanzu yaji saukin kuncin zuciyarsa ya tashi zaiyi wanka kafin a kira magariba. Abu daya ne a ransa yanzu, shine hakuri da Asmau da zaiyi. Ba karamin so yake mata ba amma dole ya barta ta auri wanda zata iya haihuwa dashi. Zafin soyayya ya rufe masa ido har ya manta yana da nakasa a rayuwarsa. Tunda baya haihuwa bazai cutar da kuruciyarta ba ta zauna da 'ya daya. Wanka ya shiga ya fito ya sanya riga da wando na yadi mara nauyi. Ya saka hula kalar adon rigar ya sha turare sai gashi ya fito a Jikamshinsa. Idan ka ganshi bazaka ce yana da damuwa ba saboda tunda yayi adduar nan babu abinda yake sai tasbihi ga Allah. Wannan ne ya saukaka masa damuwarsa yaji kwarin gwiwar niyarsa ta rabuwa da Asmau idan suka koma gida. Kafin ya fito text dinta ya shigo wayarsa. Yaa budewa yaga ta rubuta _missing Jikamshina_. Wani sabon sonta yaji ya ratsa shi. Kasa yi mata reply yayi ya tura wayar a aljihu. Yana fitowa ya tarar da kannensa jugum a falo domin kuwa Hajiya tana gama basu labarin Asmau tace su fice mata daga daki. Da ya fito duk da ransa babu dadi haka ya basar ya dubi mazan "Kuzo mu wuce masallaci" Suka tashi jiki a sanyaye. Mami tace "Yaya don girman Allah kayi hakuri da abinda Ismail ya fada. Wallahi duj don bama so ka auro wadda zata gurbata mana dangi ne" Suma sauran suka soma bashi hakuri. Ismail kuwa ko kallon yayansa ya kasa yi. Murmushi yayi wanda dukkansu sun san irinsa yake idan ransa ya baci "Magana ta wuce, bazan auri Asmau ba kamar yadda kuke so. *Amma ba don kun nuna rashin amincewarku bane, don baku isa ba*. Saboda kaddara ta fada mata ba zan ce sai na aureta ba duk da ni din bana haihuwa ko Ismail?" Ismail ji yayi kamar yayi kuka. Idanunsa tuni sun canja launi. Yayansu yana da kirki matuka, bai san yaya akayi shaidan yaja shi yayi wannan katubarar ba. "Yaya ka yafe min, wallahi Hajiya yau har zagina tayi bayan fitarka. Yanzu ma cewa tayi zamu rakata asibiti duba yarinyar Asma'un daga nan kowa ya fice mata daga gida. Hatta Mami Hajiya tayi rantsuwa bazata kwana a gidan nan ba." Col.

Table of Contents

Chapters

103 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});