Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 9

Chapter 9

Abinda Ake Gudu Book 1 Complete Hausa Novel 1,198 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Sun tausayawa Umma sosai Baba yace zai sa a bada cigiya a kafafen yada labarai. ***** Shiru Asmau na zaune a cikin mota banda addu'a babu abinda bakinta yake ambato. Tana daga gefe ta ja hijab dinta ta rufe rabin fuskarta. Sunyi nisa sosai taji wani daga gaba yana tsaki da zage-zage. Na kusa dashi wanda da alama abokinsa ne yace "ya dai kake tsaki kai kadai Bala?" Wanda aka kira Bala ya nuna masa wani hoto a wayarsa "ka duba don Allah yadda ake rashin imani a duniyar nan. Dubi fuskar yarinyar nan kai kace idan aka saka mata hannu bazata ciza ba...." Hankalin sauran 'yan motar ya koma jin jawabin Bala. Shi kuwa ya cigaba da magana cikin bacin rai "....wai yarinyar nan ce ranar aurenta ta kashe mijin saboda ya gano tana da ciki kuma yace ba nasa bane. A cikin gidansu fa aka tsinci gawar tasa a bandaki ta buga masa guduma a keyarsa bayan an kai ta, ance a halin yanzu tana hannun hukuma. Shegiya Allah Yasa su harbeta ma" A hankali Asmau ta daga kai ta kallo hoton da duk 'yan motar sai da suka karbi wayar suka gani. Gabanta ne ya fadi sosai da taga hotonta ne. Cikin dan lokaci an canja labarin gabadaya. Ba karamin mamaki tayi ba da taga hoton da ita kanta yanzu bata dashi a wayarta. Mutane kamar jira sukeyi abu ya faru sai ayita yayatawa ana ta kara gishiri da maggi a zancen. Kafin ka ankara zancen ya sauya daga ainihin yadda yake. Shiyasa ake so mutum ya kiyaye me yake saurin turawa mutane a kafafen sada zumunta (social media). Sake rufe fuskarta tayi don kada su ganeta. Wani daga kujerar baya yace "nima ina da wani hoton nata daban da wannan harda mijin" wayar tasa ya miko shima da hotonsu na dinner ita da Abubakar. Mutumin ya cigaba da cewa "ni a yadda aka turo cewa akayi kafin a daura auren aka tsinci gawarsa a bandakin hotel shine aka kalawa yarinyar. Ana tunanin wata yayiwa ciki ta kashe shi." Har zuciyarta zancen yayi mata daci sai dai kafin a gama ganin hoton wata tace itama taji labari amma cewa akayi rasuwa yayi a gidansu kuma a ranar aka gane amarya nada ciki. An rasa gane ko cikin waye nasa ne ko na yayansa don amaryar tana bin maza. Duk masu bayani na matar ne yayi kama da gaskiya. Duniya kenan, kowa da abinda zai ce ba tare da yasan gaskiyar lamari ba. Asmau tana ji motar ta kaure da tsine mata ita da Abubakar ga wadanda suka yarda ciki yayiwa wata. Rufe ido tayi kamar mai bacci tana kukan zuci har suka shiga tashar Azare ta jihar Bauchin Yakubu. ABINDA AKE GUDU ๐Ÿ™†๐Ÿฝ7 Batul Mamman๐Ÿ’– Ba karamin gudu Qasim yayi ba a hanya. Allah ne Ya kawo shi Shanono lafiya. Kai tsaye gidansu ya nufa. Gida ne irin ginin gargajiya amma yasha gyara ciki da waje ga sabon fenti. Duk shiririta irinta Qasim baya wasa da lamarin iyayensa. Shiyasa albashinsa duk wata a hidimar gidan yake tafiya ko tunanin aure baya yi duk da shine babba. Kanwarsa daya Jamila wadda ada yaso Abubakar ya nemi aurenta. A soro ya tarar da mahaifinsa Mal Musa zagaye da dalibansa samari da magidanta wurin su goma. Da dai-dai Qasim ya gaisa dasu sannan ya gaishe da mahaifinsa. Yana durkusawa gaban Malam sai hawaye ya kufce masa. Ganin haka daliban suka tashi gabadayansu suka yi sallama da malaminsu. Hankakin Mal Musa a tashe yace "Baba wata matsalar ka sake samu a wurin aiki ne?" Qasim ya girgiza kai. A lokacin Jamila ta fito zata je makota inda Inna ta aiketa. Ganin yayanta yana hawaye yasa ta koma ta sanar da Innar abinda ta gani. Kokarin tashi tayi da kafarta daya da tasha dori sakamakon karayar da ta samu a kafar bayan ta zame a bandaki. Kafadar Jamila ta dafa ta kaita soron. Suna shiga suke jin Qasim yana sanar da mahaifinsa mummunan labarin da ya dawo dashi gida. Inna ta saki kuka hade da salati "Abubakar din da na sani ko dai wani kake nufi Baba". Ido fal hawaye ya fada musu abinda ya sani dangane da rasuwar amininsa. Inna da Jamila sai kuka. Ba tun yau Abubakar yake dan gida a wurinsu ba. Yadda Qasim ke zuwa Kano hutu haka Abubakar yake zuwa Shanono. Lokacin da Mal Musa ya sami mutuwar barin jiki ba karamar hidima iyalin Kwamishina Adamu suka yi musu ba. Lalurar iyayensa da canjin aiki da ya samu yasa basu je wurin bikin ba. A can Kano kuma tashin hankalin cikin Asmau yasa basu tuna da sanar musu ba. Bayan sun gama koke-kokensu suka shirya duk da yamma tayi Qasim yasa kujerar guragun da ake tura mahaifinsa a ciki a bayan mota sannan suka kama hanyar Kano. Ana gab da magariba suka isa kofar gidan Kwamishina. Maigadi ya sanar dasu cewa gabadaya 'yan gidan suna makota wato gidansu Asmau. Gaba Qasim yayi da motarsa suka karasa can gidan. Ya taimakawa mahaifinsa ya fito jingine da jikinsa suka shiga gidan. Jigum suka tarar da Umma da Mama Yalwa kamar basu sami sabani sakamakon jin batun cikin ba. Baba Kwamishina yana gefe shi da Abdulhalim suna ta bige bigen waya. Kowa ka gani da abinda yake yi. Sallamar Qasim ta sa hankalinsu ya koma ga kofa. Kuka sosai ya zowa Mama saboda ganin Qasim. Shima bayan ya zaunar da mahaifinsa gabanta ya koma yana kukan. Mutuwar Abubakar ta dawo musu sabuwa. Da suka dan nutsu ne Qasim yace " Umma ina Asmau ne?" Kamar yace a fara wani kukan suka sake dasa sabo. A gigice yace " ba dai itama ta rasu ba?" Jafar ne ya bashi amsa da cewar ba'a ganta ba tun safe. Qasim ya share kwalla "amma me yasa Asmau bazata yi tawakkali ba. Ina ta tafi haka?" Boye- boye bashi da amfani shiyasa Shema'u ta sanar dasu abinda ya faru. Idan ma basu fada ba a waje wasu zasu fada musu. Labarin yayi matukar razana Qasim da iyayensa. Lallai iyalan biyu suna cikin tashin hankali. Jikinsa duk babu kuzari ya dubi wurin da Malam da Baba suke zaune "ko da ba a gabana akayi ba, ni shaida ne cikin Asmau na Abubakar ne." Mama ta dago jajayen idanunta tana kallonsa " Qasim abokinka fa ya rasu, yanzu ka kyauta kenan kana binsa da wannan mummunar shaida". "Mama na san inda yaje nima a ko wane lokaci zan iya tafiya. Fadin gaskiya shine adalcin da zanyi masa." Daga nan ya basu labarin abinda ya sani dangane da Abubakar da Asmau wanda babu wani mutum da ya sani. Shi kadai ne yasan wannan sirrin. Falon ya sake rudewa da kyar Baba da Malam suka samu aka yi shiru sannan suka ce a tashi ayi sallar magriba zasu karasa maganar idan sun dawo daga masallaci. ***** Tun kafin azahar mota ta sauke su Asmau a tasha. Kowa na ciki ya dauki kayansa yayi gaba, ban ita. Sai yanzu take tunanin inda zata je kuma bayan nan. Bata taba zuwa Azare ba kuma bata san kowa ba. Wurin da taga an kebe domin sallah taje tayi sallah sannan ta karasa wurin masu abinci ta sayi wake da shinkafa da

Table of Contents

Chapters

103 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});