Chapter 87
Chapter 87
Tana fitowa duk an ragu sai yayarta Shemau. Za'ayi sirri na 'yan uwa ta nuna mata inda ta ajiye kayan gyaran da aka bata a wata drawer "Don Allah kada ki rinka yi musu shan koshi. Komai sama sama yafi ko don kada ki sha wanda zai illata ki. Ga wannan kuma ki saka" Asmau ta karbi kunshin ledar da Shemau ta bata. Doguwar riga ce abaya amma ruwan madara. Rigar ta tsaru karshe da mayafinta. Bude baki tayi zata fara godiya da dan hawayenta Shemau tace "indai tayi miki kyau shikenan. kiyi sauri ki shirya kiyi sallah kada ango yazo kina daure da tawul. Mu zamu tafi ga Zulaiha nan da Walida sune kawayen naki dama. Sabira da mijinta bai kamata ta zauna ba." Shemau bata fita ba sai da Asmau tayi sallah ta shirya. Wani turare mai maiko ta bata ta fara shafawa kafin aje ga sauran. Kamshi ne zai tarar da Jikamshi. Bayan tafiyarsu daga ita sai su Walida suka dawo falo don ba'a son wannan zuwa har uwar daki da abokan ango. Alamun bude gate ya sa hankalin Asmau tashi. Mayafinta ta gyara kafin su shigo. Su hudu ne harda angon. Biyu abokansa da kaninsa Ismail. Bata iya ganin kowa sai muryoyi da take ji. Ba wasa suka tsaya yi ba nasiha ce dai da addua. Sai a lokacin taji muryar maigidan nata yace Amin. Daga nan suka tashi yace akwai dreba zai ajiye su Zulaiha. Abokin nasa mai dauko amarya yace shi zai je. Ashe Walida ce ta dauke masa hankali. Tana ji ya fita rakiya ta kasa bude mayafin bare ta tashi. Lokacin da ya rufe kofar gidan kuwa zuciyarta ba karamin harbawa take ba. Anyi an gama yau ga Asmau a matsayin matar Ishaq. Motsi da kamshinsa taji a kusa da ita ta sake kankame mayafin. Shiru bata ji ya zauna ko yayi magana ba. A hankali taji an bude gaban mayafinta ya shigo da kansa ciki. Ashe a gaban kafafunta ya durkusa. Zatayi baya yasa hannu ya zagayeta ga mayafinta ya rufe su sai kamshin turaruka da numfashinsu. Babu abinda zata iya yi sai kawai ta rufe idonta cike da kunya. A hankali yake mata magana "Kinyi kyau Matar Jikamshi, yau so nake kamshinki ya rikita ni shiyasa zanyi ta like miki" Sake runtse ido tayi tana jin wata irin kunyarsa tana karuwa a zuciyarta. Ya dago kanta tare da matso da bakinsa kusa da nata ga hancinsu yana gugar juna "Ko na daukeki ne?" A nutse ta bude ido suka sauka cikin nasa. Murmushi tayi masa yaji gabadaya ta hargitsa masa lissafi. Irin wannan farincikin a karkashin inuwar aure halattaccen zama kawai Allah Yake sako shi. Bai dena kallonta ba ya rike mata hannu suka tashi. Mayafin ya cire ya ajiye a kan kujerar ya karewa rigarta kallo. Shemau ta iya zabe. Sai a lokacin ita ma ta kula da kayansa. Yau ma harda babbar riga a shaddarsa ruwan madara kamar kayan jikinta. Hular kuwa a kasa ta ganta kusa da inda take zaune. Yana rike da ita har suka je dakinta. "Shiga ki jirani naje nayi wanka. Kunyarki nake ji da nace ki rakani. Amma kiyi alwala kafin na dawo" Yana kashe ido tana sunkuyar da kai. Sai da ta shiga ya wuce yana murmushi. ***** Da abin sallah ya shigo harda mayafinta na falo sanye da kayan bacci riga da wando. Ya shimfida musu abin sallar tana kallonsa sannan ya nuna mata alamun ta tsaya suyi sallah. Kira'ar Jikamshinta ta tafi da ita don nutsuwa da bawa harufa hakki. Raka'a biyu suka yi sai shafai da wutri sannan ya shiga jero addua da larabci kamar bazai dena ba. Bayan ya kai karshe suka shafa ya dawo gabanta ya dafa kanta ya sake wata sannan ya tashi zai nade abin sallar. Karatun Uwargida ta tuna ta dan matsa a kunyace ta karba ta ninke. Ya ji dadin hakan kuwa sosai. Fita yayi daga dakin ya dawo yace ta biyo shi. Falo suka koma ya ajiye mata snacks, nama, juice da youghurt. "Wanne kika so" Jikinta duk ya fara sanyi ta ce ta koshi. Yayi murmushi wannan salihancin duk zatayi ta gama ne. "Ni zanci kinga ya kamata ki zauna a kusa dani har na koshi ko" Tace "uhmm" kamar wadda ta tauna flagyl bisa kuskure. Centre table din na gabansa ta zagayo zata zauna a kusa dashi kawai ya janyota kan cinyarsa tare da yi mata rikon da bazata iya gudu ba. "kada kice min kunyata kike ji kin san ni dai bani da ita indai a kanki ne. Kema kuma haka nake so ki zama." Ta rausayar da kai gefe guda tana kokarin zillewa. "Idan ba kya so muci abincin sai mu koma inda muka fito ni bani da matsala." Tace "To bari na matso da plate din ni ina jin yunwa" Hancinta yaja yana dariya "ace sai da dabara zan samu kici abinci." Bayan sun gama ta kwashe komai ta kai kitchen din da bata gaji da gani ba tun da su Walida suka nuna mata. Da ta dawo ya kashe duk kayan wuta suka shiga ciki. Dakinta zata shiga yace "muje namu dakin ki saka masa albarka" "Brush zanyi" "Can ma akwai duk abinda zaki bukata" hannunta ya kama suka tafi. Ni'imtaccen kamshi da sanyi ne suka doki hancinta. Komai na dakin sabo ne. Dama dakuna hudu ne a gidan. Aka saka mata gado a biyu dayan aka mayar mata karamin falo. Nasa dakin ya dauki hankalinta. Ya shiga bandaki ta tsaya dube dube. Wani bakin abu mai santsi ta gani akan gadonsa ta dauka. Baki ta bude da ta gane ko meye. Rigar bacci ce mai kyau da ta dace da amare. Tana jin zai fito ta ajiye sai dai ya ganta. Ya zo ya rungumeta ta baya "rigar tayi miki kyau ko? Hmmm nifa ban ganewa kamshin nan naki ba. Ji nake kamar na mayar dake jikina" Asmau ta janye jikinta kai a kasa. Rigar ya mika mata yace taje ta shirya yana jiranta don yaga taki sakewa a nan. Idan ta wuce minti goma zai biyo baya. Dakinta ta koma tana mayar da numfashi kamar wadda tayi tsere. Sai juya rigar take yi a hannu. Karshe dai ta sake shiri ta saka ta dora zani ta fito. Daga bakin kofa ya tareta ya dagata sai kan gado. Sai dai kuma yana ajiyeta ta soma hawaye. Zuciyarta tayi mata nauyi sosai. A take ya rude yana tambayarta ko me ya sameta. Duk yadda zaiyi Asmau taki magana sai kuka har yaji babu dadi a ransa. A sanyaye yace "Kin tuna Abubakar ne? Addua ya kamata kiyi masa ba kuka ba" Tayi saurin girgiza kai. Idan ya tabata kuma jikinta rawa yake sosai. Ganin taki magana sannan kamar tana tsoronsa sai kawi ya kwantar da ita yaja bargo ya lullubeta tare da yi mata kiss a goshi "kiyi hakuri idan nayi miki abinda bakya so ne. Just sleep bazan dameki ba" Daya gefen ya koma ya zauna yana kallonta. Asmau ta juya baya tana kuka mai tsuma zuciya da tada hankalin mai saurare. Dole tayi kuka a wannan rana ko taji sauki a ranta. Yana gefe yana jin kukan har ransa amma ya rasa me take
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103