Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 8

Chapter 8

Abinda Ake Gudu Book 1 Complete Hausa Novel 1,198 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

taje wurinsu ba ta tsira ba. Tana cikin wannan tunanin taji ana cewa, "Azare mutum daya Azare mutum daya" Ko dogon tunani batayi ba ta nufi motar da sauri. 'Yan kamasho har sun fara baibayeta ana tambayarta ina zata je. Da shigarta motar dreban yazo suka gama surutansu da 'yan uwansu drebobi ya tada mota suka harbi titi. ***** Har karfe tara babu motsin Asmau. Anti Bintu da Jafar ne zasu kaita asibitin duk sun shirya. Umma tace aje a tashe ta idan batayi wanka ba su tafi a haka ta yi idan sun dawo. Aina'u aka tura taje ta dawo tace bata ganta ba. Shema'u tace kila tana bandaki kije kice mata tayi sauri ita ake jira. Da gudu Aina'u ta dawo tace "Anti na duba bata daki kuma bandakin a bude yake". Umma na jin haka tace a tashi a dubota karshenta buya tayi saboda kada aje asibitin. Da farko Yassar da Aina'u kadai ne suka duba dakunan da bayan gidan suka dawo basu ganta ba. Hakan ya soma tsorata Umma kowa ya tashi a rude suka shiga nemanta. Ganin babu alamun za'a sameta a gida Shema'u ta kira wayarta. Tayi mamaki jin muryar Walida. Bayan sun gaisa Walida tace wayar na hannunta. Tun ranar da abin ya faru zance ya fara bazuwa mahaifinta har gidan yazo ya dauketa da kansa lokacin da aka sake mayar da Asma'u asibiti kuma ya haramta mata sake zuwa gidan. Shema'u tayi kasake har Walida ta gama bayani sannan tace zata turo Yassar ya karbi wayar. Tana juyowa Umma ta kalleta a tsorace "Kada kice min an sace wayar ne". "A'a Umma tana wurin Walida." "To ina Asmau ta shiga, ni Bara'atu daga wannan sai wannan". Da gudu Jafar ya dawo falon da takarda a hannunsa wadda ya gani a tsakiyar gadon dakin su Asmau. Jiki babu kwari ya mikawa Umma ta karba hannu na rawa. _Umma ina mai rokon gafararki a lokacin da kike karanta wannan takardar nayi nisa da gida. Nayi nadama da bakincikin halin da na saka ku na kuma jefa kaina. Sai dai na dauki komai a matsayin kaddara. Na tafi ne saboda bana son ku daukarwa kanku zunubin kashe rai. Zan haifi abinda ke cikina da izinin Allah zan kula dashi batare da na fada mummunar rayuwa ba. Ki yafe min kuma ki cigaba da yimin addu'a. Allah Ya hadamu cikin aminci. Sannan ina mai kar tabbatar muku cikin nan na Abubakar ne. Ku yafe mana._ _Asmau_ Kuka mai sauti Umma ta saka wanda yasa Shema'u saurin karbar takardar ta karanta. A take itama ta fashe da kukan. Umma sai sumbatu take saboda tsabar tashin hankali. "Asma'u ki dawo wallahi babu mai cire miki cikin. Ki dawo na yafe miki. Ina zaki je ke kadai a wannan duniyar da amana tayi mana karanci?" Duk wanda yake wurin sai ya tausayawa Umma. Dama da mayafi a jikinta tace Jafar ya dauko mukullin motarta yazo su fita neman Asma'u. Nan da nan kowa ya fita suka fara karade unguwar. Daga nan sune gidajen kawayenta da tashoshin mota tare da hoton Asmau suna tambayar ko an ganta. ***** Karfe goma na safe tayiwa Qasim a kofar shagon mai gyaran waya. Mai shagon a wurin ya sameshi a ransa yace dan anace ya iso. Allah Ya taimake shi ya gama gyaran shiyasa da fara'arsa yace "ranka ya dade ai yanzu nake shirin kiranka idan na bude shagon." "Baka da abin da zaka fada min. Gyaran waya sati guda kuma na biyaka. Kawai sai ka zauna kana ja min rai." Gefe ya matsa mai shagon ya bude. A cikin wata drawer ya dauko wayar Qasim wadda screen dinta ya fashe tun ranar alhamis da ya iso garin Zamfara. Duba wayar yayi ya tabbatar tayi sannan yayi sallama da mutumin ya fita. Bakin titi ya koma inda ya ajiye motarsa. Yana shiga ya kira mahaifiyarsa bayan sun gaisa ya sanar da ita wayar ta gyaru zata rinka samunsa. Dama ta wani yake ara a ofishinsu ya saka sim dinsa ya kira. Karamar wayarsa tana wurin kanwarsa da ya bawa kafin ya taho. Bayan yayi sallama da ita ya kira numbar Abubakar. Kullum idan ya ari waya sai ya gwada amma a kashe yake samunta. Dariya kawai yake yi yace ango ya dau hutun waya kenan. Sai da aka fi kwana uku a haka ya fara damuwa ko sace wayar aka yi. To da yake data aro yake amfani shiyasa bai matsa ba sosai. Yau kuwa yayi sa'a gwaji daya ta shiga. Sai da ta kusa tsinkewa yaji an dauka. Ko magana bai jira anyi ba yace "Haba mutumina, daga aure sai ka yar dani. Nayi ta kira bana samu gashi tawa wayar ta lalace. Ya madam? Ina fata duk kuna lafiya." Shiru yayi saboda yaji ba'ayi magana ba. "Hello, Abubakar ko baka jina ne?" Ya dan cire wayar yana dubawa ko gyaran ne baiyi ba. Daga daya bangaren yaji ance "Qasim". Muryar tayi kama da ta Abubakar sai dai ya tabbatar bashi din bane. Rike wayar yayi yaji an sake kiran sunansa sannan ya amsa "Ango me ya sameka ne? Naji muryar taka taso ta canja min." Abdulhalim ya hadiyi yawu sannan ya shafa kansa yana tunanin da yadda zai fadawa Qasim abinda ya faru. "Qasim nine Abdulhalim, dama Abubakar ya fada min anyi maka transfer a wurin aiki da karin girma". Sai a lokacin Qasim yayi ajiyar zuciya da ya gane mai maganar "Wallahi kuwa baban Yaya. Kuma da yake ko wata ba'ayi da bani query ba shiyasa dole na tafi kada nayi laifin da za'a koreni. Daga karin girma ace na fara wasa da aiki" Yana dariya yake maganar sannan ya tambayi ina amininsa ango Abubakar. Shiru Abdulhalim yayi na dan lokaci sannan yayi ajiyar zuciya yace "Qasim Allah Yayiwa Abubakar rasuwa a ranar daurin aurensa". Wani duhu-duhu Qasim ya fara gani da kyar ya iya cewa "kai, karya ne Wallahi. Abubakar din? Abubakar fa nake nema kaninka mai wannan layin". Abdulhalim yasan za'a rina. Abubakar da Qasim abokai ne tun aji daya a firamare. Cikin nutsuwa ya labartawa Qasim abinda ya faru. Tamkar karamin yaro haka Qasim ya rinka kuka. Har wani zazzabi yaji ya kama shi a lokacin. Ya dan gyara murya yace "ina Asmau?" "Tana gidansu" Abdulhalim ya bashi amsa a takaice. Qasim yayi alkawarin zuwa Kano a satin idan ogansa ya bashi dama. Mahaifiyarsa bata sami zuwa bikin ba saboda ciwon kafa kuma kanwarsa wadda su biyu ne dama ita take jinyarta. Kila shiyasa basu ji zancen rasuwar ba tunda a Shanono suke. Daga nan suka ajiye wayar Qasim ya tafi office. Duk wanda ya ganshi yasan yana cikin tashin hankali. Koda yaje wurin ogansu da hawaye a fuskarsa ya fadi bukatarsa. Labarin ya taba zuciyar ogan ya bashi damar tafiya a ranar ya dawo wata lahadin. Gidan da aka bashi yaje ya canja kaya cikin kankanin lokaci ya kama hanyar Kano. ***** A can Kano an bazama neman Asmau. Umma tayi kuka har ta gaji. Hajjo da 'ya'yanta suka zo har gidan suka yi mata abinda suka saba. Har cewa sukayi ita ta turata yawon karuwanci. Da zance ya kai kunnen Mama Yalwa ko kadan bata ji dadi ba haka ma Baba da sauran 'ya'yan gidan.

Table of Contents

Chapters

103 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});