Chapter 88
Chapter 88
so. Sai da tayi mai isarta yaji tana ajiyar zuciya. A zaune ma yake jingine da pillow yana kallonta ya rage hasken dakin sai fitilar gefen gado. Baiyi fushi ba ya matso kusa da ita ya sanyata cikin jikinsa. Fuskarta duk hawaye ta matsa kusa dashi itama don kokari harda zagaye hannuwanta a jikinsa ta kwantar da kanta a kafadarsa tana mayar da numfashi. Hankalinsa ya dan kwanta da yaji ta a jikinsa ya shafa mata kai "kukan me kika yi, dama akwai abinda zai saka ki kuka ki zabi yinsa ke kadai ki kasa fada min?" Saukar hawaye mai dumi yaji a kirjinsa tace "Jikamshina don Allah da gaske kana sona?" "Kinfi kowa sanin amsar tambayarki" Ta dago kanta tana fuskantarsa kunya sosai a tare da ita. Muryarta ce take nuni da rauni da ciwon dake cikin ranta "a yau na kara tsanar kaina da biyewa zuciya, nayi aure a matsayin budurwa amma na dade da rasa wannan darajar. Ban san na gama cutar kaina ba sai yanzu, lokacin da duk wata mace take jin ta isa a wurin mijinta idan ya sameta cikakkiyar budurwa. Na rasa wannan damar, bazan taba yi maka tinkaho da abinda bani dashi ba. Ina jin kunyarka ina jin kamar na cuceka ma...." Allah Sarki, tausayinta yaji ya kama shi sosai har tasa zuciyar ta raunana ya hanata karasa maganar ta hanyar da yasan dole tayi shiru. Sai da ya gama kissing dinta ya sanya yatsansa a saman bakinta. Tana kallonsa da fuskarta mai hawaye "ba karya kika yi min ba game da rayuwarki. Nasan komai kuma duk da haka Allah Ya sanya min sonki a zuciyata. ASMAU yarda da kaddara shine cikar musulunci. Abinda kika rasa bazai taba dawowa ba. Tunda kinsan baki da iko akansa babban abinda zaki yiwa kanki gata dashi shine hakuri da dangana. Mata da yawa suna aure a irin wannan yanayin kuma wasu sai kiga asirinsu ya rufu. Ke da naki ya fito fili kin zama misali ne ga sauran mata. Kinyi nadama kin tuba, kuma wannan ake nema daga dukkan musulmin kwarai. Allah Ya kara kare sauran mata daga haduwa da fadawa irin wannan sharrin." Wani kukan mai karfi yazo mata tace "wallahi sau daya ne...sau daya tsautsayi ya fada mana. Ka yafe min don Allah." Rungumarta yayi sosai a jikinsa duk dauriya irin tasa sai da yaji hawaye ya zubo daga idonsa. Ya Allah Ka nesanta mu daga tarkon zina. Mai zubar da kimar mai kima, ta zubar da girman babba, ta wulakanta mai daraja. Idan aka yita Allah zai iya yafewa wanda ya tuba amma wallahi tayi tambari kenan a rayuwar wanda yayi. A daidai kunnenta yace "Ashe duk yadda nake fada miki ina sonki baki taba yarda ba tunda har kike kokwonto a yau. Ban taba karyata zancenki ba. Da kinso tun ranar farko zaki iya cewa Safina ba 'yarki bace kuma zan yarda. Fatana Matar Jikamshi shine mu kasance ma'aurata har a aljannah." Ya kwantar da ita akan pillow yana kallon fuskarta "A daren yau nake so na goge miki duk wata damuwa da kika tsinci kanki a baya. Ina so na zama farincikinki. Ina so tarihin Asmau da Ishaq ya fara. A yau nake son rubuta kaina a zuciyarki. Ki yarda cewa kema abar so ce kuma da yardar Allah zakiyi rayuwar aure cikin jindadi kamar kowace mace. Abu daya kawai nake bukata yanzu daga gareki" Maganganunsa sun sanyaya mata zuciya. Tsoron da take ji na zata wayi gari taga canji daga gareshi saboda rashin cikarta yasa ta kuka. "me kake so" "Kice kina son mijinki" Sai da ta kalle shi tayi murmushi sosai sannan tace "I love you Ishaq, I love you Jikamshina. Ina sonka mijina" Ya riko fuskata a tafin hannuwansa ya matso da ita daidai da tasa yana mata wani irin kallo. "Lokacina da kika cinye kina kuka zaki fara biya yanzu" Kokarin guduwa tayi ya janyota ya danne tare da rufa musu bargo. Amarya da ango....asuba ta gari. _Mrs Othman Maman Jannah gaisuwa mai tarin yawa gareki_ ABINDA AKE GUDU🙆🏽55 Batul Mamman💖 Juyi Asmau tayi wanda yasa ta bude ido. Cikin na Col. Ishaq suka sauka da yake ta kallonta. A kwance take shi kuwa ya dora habarsa akan hannunsa daya ya zuba mata ido tana ta bacci. Ba karamar kunya taji ba tayi kasa cikin lallausan bargon da suka rufa dashi. Yana murmushi ya bude mata fuska tare da cewa "Na tasheki da kallo ko, duk laifinki ne da kika sa nake jin dama tun ranar da muka fara haduwa aka daura mana aure." Bai san irin yadda take jin kunyarsa ba. Ta rufe ido tana noke kai. Jin kanta take a takure kamar tayi tsuntsuwa ta gudu. Dama ya tabbatar da wuya yaji tayi magana. Duk da burinsa kunyarta ta ragu idan suna tare amma ya lura kamar karuwa tayi. Matsowa yayi daidai kunnenta yace "zaki iya tashi muyi sallah?" A hankali ta gyada masa kai sannan tace cikin wata karamar murya "asuba tayi?" Mamaki tayi domin gani take kamar yanzu ta rufe idonta ta fara bacci. Kamar yasan me take tunani yace "kina mamaki ne? Bayan kin cinye daren da kuka da ....." Da sauri ta rufe masa baki kafin ya fadi abinda yayi niyya. Ai kuwa ya ciji tafin hannunta a hankali ta cire shi daga bakinsa ta saki kara tana kwabe fuska zata yi masa kuka. Dariya ya fara da yaga da gaske kukan zata yi harda guntun hawaye ya kama hannun yana hurawa. "Yi hakuri my darling Asmau, matar soja bata kuka. Matar Jikamshi kuma ba raguwa bace" Kyale shi tayi yana rarrashinta ta daidaici kafadarsa sai saukar cizo yaji. Ta soma dariya da taga ya shige shi sosai ai kuwa suka fara kokawa yana cewa sai ya rama. Ga tsoron kada ya rama din da gaske ga dariya tana cinta. Tun yana zai rama har ya koma yana kallon yadda take dariya da hawaye a idonta. Ji tayi ya rungumeta a hankali "Allah Yayi miki albarka Matar Jikamshi. Yadda kike faranta min nima Allah Ya bani ikon yi miki haka." Nutsuwa tayi ta dena dariyar tana cewa amin ga adduarsu sai ga kiran assalatu. Col. Ishaq yayi saurin tashi "Kinga zaki sa mu makara ko? Na tashi da niyar nayi shirin zuwa masallaci sai na tasheki ne" "Ka tashi dai kana cin zalina daga zuwana gidanka" "Haka ma kika ce? Ji yadda kika cije ni fa. Ki zauna cikin shiri idan na dawo zan rama." Sai da ya fito daga bandaki ya saka doguwar riga zai tafi masallacin dake bayan layinsu yazo inda take kwance don bazata tashi yana dakin ba yace "ki kular min da kanki sai na dawo" ya kusa bakin kofa yaji tace "Allah Ya tsare min kai Ya dawo da kai lafiya" Yaji dadin adduar sosai har bazai iya kwantatawa ba "nagode Matar Jikamshi amma hakan bazai hanani ramawa ba idan na dawo." Daga haka ya fita itama ta tashi ta kimtsa tazo ta fara nafila. Bayan ta idar da sallolinta zama tayi tana ta mika godiyarta ga Allah. Hakika ta sami babban rabo da Allah Ya nufeta da yin aure duk da abubuwan da suka faru a rayuwar ta. Mata irinta nawa ne suke cikin tashin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103