Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 56

Chapter 56

Abinda Ake Gudu Book 1 Complete Hausa Novel 1,199 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ba don yana ganin mutuncin Qasim din ba tun ranar da ya gansu da Asmau da a lokacin zai fada masa. "Yarinya dake duk kin rikita min lissafi. Amma zan rama ne, sai kin shigo gidanki" "Nima fa ka rikita min" "Me kika ce?" Zancen zuci ne ya fito fili tayi saurin toshe bakinta. Ta rasa inda zata sa kanta don kunya. Tana ji yana mata dariya don yasan bata so yaji abinda ta fada ba. "I love you Matar Jikamshi. Nasan bazan kara samun nutsuwa ba idan ba aurenki nayi ba. Na riga na fadawa Hajiya amsarki nake jira a fadawa iyayena maza. Idan kika zabi Qasim zan tayar da yaki a zuciyarki" Wani dadi ne taji yana ratsata. Ashe tana da rabon samun farinciki a rayuwarta. Ita ma tana son shi kuma ta shiryawa duk wani nau'i na gori da zai iya zuwa daga danginsa. Abinda ake gudu ya riga ya faru sai dai a kiyayi gaba. " 'yarka da Yassar ma bazasu barni ba idan na zabi wani ba kai ba. Da ka tashi sai ka hada da zuciyata data Amatullah kuma harda ta kanina." Da tasan irin yadda yake ji a ransa da ta rage yi masa magana ko don ta sassauta masa. Ajiyar zuciya yayi har tana jin sautin "Say you love me please" ya fada cikin sanyin murya. Yau daya zata sakaya kunyarta ta farantawa mai faranta mata "I do love you _Jikamshina_" Kafin ya kara magana ta kashe wayar gabadaya don tasan zai sake kira. Kwanciya tayi akan gado tana juyi ita kadai zuciyarta kamar an wanke mata. Shi kuwa rike yake da wayar a hannu yana murmushi. Hmmm bari dai ace an daura musu aure. Ranar Asmau zata san tana da masoyi. Zaiyi iya kokarinsa wurin nuna mata soyayya da cewar itama har yanzu tana da darajarta a cikin mata. Abinda ya wuce a baya sai ayi ta addua da fatan Allah Ya yafewa musulmi kurakuransu. ***** Tana ta maimaita hirarsu a kwakwalwarta tana dariya Amatullah ta shigo "Ummina Umma tana kiyanki" Ai da sauri ta sauko daga kan gadon. Shaf ta manta Umma tace tana son ganinta. Saurin da take yi yasa Amatullah tace "Ummi guduwa zamuyi ne? Me nene akan gadon?" Asmau tayiwa kanta dariya sannan ta dauki Amatullah tana juyi da ita. Soyayyar Jikamshi ta zame mata wani bangare mai mahimmanci a rayuwarta. Tana juyin tana dariya. Amatullah tana tayata duk da bata san dalilin murnar Ummin ta ba "Ummi abin dadi ne ya fayu?" "Shine zai faru in sha Allah Ama, muma Allah zai bamu rayuwa mai tsafta kamar kowa" "In ce Alhamdulillah?" Amatullah ta tambaya "Fadi kinji Aman Ummi" Sai da ta gama murnarta ta kama hannun Amatullah suka fito. A falo ta barta ta karasa dakin Hajjo. Kafin ta shiga taji muryar Anti Bintu tana magana sama sama da ji kasan ranta a bace yake "Yaya Bara wallahi Asmau tana son Ishaq. Don ta fada miki zata sallamesu duk su biyun kawaici ne kawai. Ita a tunaninta bata da wata kimar da namiji zai aureta. Don Allah kada ku shiga tsakaninsu. Hajjo kiyi mata magana " Hajjo tace "Bintu nima ba wai naki Ishaq bane. Ki tuna wacece Asmau, tana da tabon da babu ruwan da zai wanke shi duk duniya. Qasim da iyayensa sun san komai game da ita kuma dazu muke ji ashe saboda ita yaki aure tuntuni wai kada kishiya tayi mata gori ko habaici" Anti Bintu tace "to duk abinda yayi ai ba wai sunyi da ita zata aure shi bane. A yadda na kula da irin son da Ishaq yake mata ba zai hakura kai tsaye ba." Umma kanta tasan wanda Asmau take so amma bazata iya yiwa Alh Adamu musu ba kamar yadda shima yaji nauyin Mal Musa. Idan ta biyewa Bintu jan zancen kawai za'ayi ta yi azo zumunci ya sami rauni. "Bintu don Allah ki bar zancen nan. Komai ya kure tunda ranar lahadu zasu zo kawo kudi. Itama sai tayi hakuri ta karbi kaddara" A fusace Anti Bintu ta mike "ni bazan zuba ido ina kallo a cuci yarinyar nan ba. Ba kwa tunanin kada *abinda ake gudu* ya sake faruwa? Don kaddara ta fada mata shikenan kuma bata da damar zabar wanda take so" "Abinda ake gudu ya riga ya faru kumq shine yasa dole duk muyi hakuri. Kina jin da hakan bata faru da rayuwarta ba zan amince da auren nan ne? Yanzu kuwa bamu da bakin magana tunda mu za'a taimakawa. Ki dena bata bakinki akan maganar nan. An gama yanke shawara tun dazu" Hajjo ta rasa yadda zatayi da su biyun. Kowacce ta kafe har suna neman yin fada "don Allah kuyi hakuri. Bintu kece karama, mu taru kawai mu tayata addua." Hawayene kamar an kunna famfo yake saukowa daga idanun Asmau. Dama shiyasa Qasim yace ta jira zuwan lahadi? Yanzu shikenan tun ba'aje ko'ina ba an datse mata samun farinciki daga wurin Jikamshi. Duk maganar su Umma kuma gaskiya suke fada. Ita din tana da tabo a rayuwarta. Wannan yasa a komai shawararta zata zamo ta karshe. Iyaye zasuyi ta ganin kamar komai suka yanke shine alkhairi gareta. A sanyaye ta shiga dakin ta zauna a kasa. "Umma indai auren Qasim kuke gani shi yafi dacewa dani na amince" Anti Bintu ta taso ta tayar da ita tsaye. "Asmau wace irin magana ce wannan. Ishaq kike so kuma na shaida yana matukar sonki. In Allah Ya yarda shine mijinki" Umma taji tausayin Asmau har ranta amma yadda abin yazo musu ne basu da yadda zasuyi "Bintu na dauka mun gama maganar Ishaq dinnan" "Yaya Bara'atu bazan bar maganar ba sai naji daga bakin Ishaq ko shi din ya hakura" Cikin kuka Asmau tace "Anti Bintu ki bar maganar kawai. Allah Yasa hakan shine mafi alkhairi" Tashi tayi ta fita jikinta duk babu kwari. Gobe in Allah Ya yarda zata kira Jikamshi ta bashi hakuri. Bata san wace irin rayuwa kuma zatayi da Qasim ba. Mutumin da bata taba jin sonsa ko kadan a ranta ba. ABINDA AKE GUDU🙆🏽42 Batul Mamman💖 Sallar isha kawai tayi ta kwanta sai kuka. Ganin bazai fishsheta ba yasa ta tashi ta dauro alwala ta soma nafila. Yi take tana kuka tana kara istigfari. Rokon Allah take Ya yafe musu kuskuren da suka aikata wanda har yau yake bibiyar komai na rayuwarsu. Daga nan tayi adduar fatan samun nutsuwa da dukkan wanda Allah Ya kaddara zata aura. Tana sallar Anti Bintu ta shigo da niyyar sake bata baki ta tarar tana sallah. Gefen gado ta samu ta zauna tana jiran ta idar. Tunanin wannan al'amari ne ya rinka damunta. Idan akace *abinda ake gudu*to ba faruwar laifin ake ji ba. Abubuwan da zasu iya biyo bayansa. Asmau ta dade tana ganin tasirin hakan a rayuwarta tun ranar da Abubakar ya rasu. Miji ya rasu ranar daurin aure sannan a sami amarya da ciki. Ai ko a iya nan aka barta ta kafa tarihi a rayuwa wanda duk mutumin da ya santa idan suka hadu sai ya tuna. Ga 'ya ta haifa itama nan gaba tana kara wayo zata iya bukatar jin waye ainihin babanta. Idan kuma marasa tausayi cikin mutane suka goranta mata yanayin haihuwarta ko na sakan

Table of Contents

Chapters

103 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});