Chapter 53
Chapter 53
da wani ba" "Don Allah kayi hakuri" tace idonta na kawo ruwa. "Ki fada min ni dashi waye ya fara nuna miki so" "Kai ne" ta amsa masa jiki a sanyaye. Bata son bata masa rai ko kadan saboda yadda take sonsa. "Alhamdulillah, da ya rigani zan ci girma na bar masa ke don bazan iya tarayya da wani akanki ba. Ina da kishi mai zafi wanda ban taba sanin kaina dashi ba sai yau. Amma tunda na riga shi sai dai shi ya hakura. Ina sonki kuma bana jin zan iya hakura dake." Shiru tayi tana kallon kasa. Tun bayan rasuwar Abubakar ta cire rai da sake samun soyayyar wani da namiji sai gashi yanzu har mutum biyu ne suke sonta. Mutum biyun da take matukar son daya, dayan kuma take ganin girmansa. Duk su biyun kuma tana jin kunyar nuna musu bata sonsu a yadda take ganin ba karamin darajata suka yi ba da suke sonta da aure. Col Ishaq yana kallo yadda ta shiga rudani. Kamar yadda ya fada mata da ace Qasim ya rigashi to zai hakura ne indai ya tabbatar da gaske yake sonta. A yanzu kuwa yana da yakinin shi Asmau take so kuma ya riga saboda haka yana nan daram sai yaga abinda ya turewa buzu nadi. Shi kishin kara masa so da kaunarta yayi ma. "Kamar kwana nawa kike bukata na baki ki sallame shi" Ji karfin hali ta ayyana a ranta. A fili tace "bangane ba" "Kin gane, karin bayani kike nema dai. Bansan iya matakin da kuka kai ba ke dashi shiyasa zan baki lokaci kuyi rabuwar arziki. Shima don na fahimci kamar yana da halin kirki ne." "Ya kake so nayi? Kaima na fada maka babu zancen aure a raina shima kuma hakan na sanar dashi" "Idan babu zancen aure a ranki kin tanadi yadda zakiyi da soyayyata wadda yanzu ma na fara nuna miki ita. Idan bakiyi wasa ba nan gaba kadan saboda yadda zan rinka yakin neman sonki da kanki zaki ce gobe a daura mana aure" Dariya tayi, shi a komai sai ya saka wasa tace"kai Jikamshi" "Allah kuwa Asmau" shima ya mayar mata da murmushi. "Ni da ban taba cewa ina sonka ba. Amma kana da confidence a kaina" Kansa ya shafa yana kallonta. Baya gajiya da kallon Asmau ko kadan. "Asmau kina sona. Nima ina sonki. So bana bukatar sai kinyi ta maimaitawa da baki. Akwai lokacin da zaki rinka fada da kanki" Ita kam Jikamshi yana bata mamaki. Sai ya fadi magana ya kuma dake abinsa. "Ki shiga ciki bana son kina shakar kurar nan. Kada ki manta da abinda nace. Idan kin sallame shi zan turo iyayena a fara maganar aurenmu" Magana taso yi ya sanya yatsansa akan lebensa alamun tayi shiru. "Idan rokona zakiyi akan Qasim kada ki bata bakinki. Nan da sati biyu idan baki sanar dani yadda kuka yi ba ki zaki ga magabatana sunzo. Ki kula min da kanki da princess dina. Yau duk kin rikita min lissafi na kasa bata kulawa yadda ya kamata" "Ni babu ruwana." "Harda tsakinki. Sai da safe" "Allah Ya bamu alkhairi" Tana kallo ya shiga mota ya zauna sannan itama ta juya. "Matar Jikamshi" Cak ta tsaya amma bata juyo ba sai murmushi da take yi. "I love you" Hannuwa tasa ta rufe fuskarta cike da kunya tayi hanyar gida a kunyace. ****** Daurewa kawai Col. Ishaq yayi har suka karashe hirar cikin wasa. Da ya rage shi kadai yana tuki tunani yake kada iyayen Asmau su bawa Qasim ita saboda sunfi sanin shi sannan abokin Abubakar ne. Saurin kawar da tunanin yayi daga ransa. A zatonsa ya gama soyayya akan Badar sai gashi lokaci guda Asmau ta wargaza masa tunani. Yana zuwa gida dakin Hajiya ya wuce. Bayan sun dan taba hira ya sanar da ita zancen Asmau. Tayi mamaki sosai don bata taba hasko hakan ba. Bilkisu da tayi niyar fada mata kuma ranar tun a hanya yaja mata kunne. Shiru tayi na dan lokaci kafi tace "Kai yanzu kana tunanin sai ka aureta ne kawai zaka iya kyautata rayuwarta da ta Safina?" "Hajiya nifa ba don in kyautata musu kawai nake son aurenta ba. Ina sonta ne tsakani da Allah" Ko kunyar yace yana son mace baiyi a gabanta. Tayi iya kokarinta wurin nuna masa kunyar dan fari amma duk baya biye mata. Yanzu me ya kawo zancen soyayya a gabanta. "Bazan zama irin iyaye marasa karbar kaddara ba musamman da na san komai game da ita. Kai ba yaro bane da zan ce baka san abinda ya kamata ba. Amma ka jira nayi shawara da 'yan uwana dana mahaifinka. Kasan zancen duniya baya buya. Gara su sani tun kafin ayi auren sabo gudun gutsiri tsoma" Murmushi yayi ya nuna mata tsantsar farincikinsa. "Hajiya nagode da kika fahimce ni. Ina fata ko sun nuna rashin amincewa don Allah kada ki hanani aurenta don wallahi bakiji yadda nake jinta a zuciyata ba" Haj Lubabatu ta kawar da kanta gefe a kunyace. Ya cigaba da cewa "idan tayi murmushi ji nake kamar...." "Kai tashi ka bani wuri zancen ya isa haka" ta fada amma kafin ya tashi ita tayi gaba. Dariya yayi dama tsokanarta yaso yi. Sai da ya gama shirin bacci ya dauko wayarsa zai kira Asmau yaga missed calls da bakuwar number har uku. Ya kira numbar ga mamakinsa sai yaji muryar Qasim. Sun sake gaisawa yace ya karbi numbarsa a wurin Yassar ne don su rinka gaisawa. Hira suka dan taba cikin mutunta juna. Suna yin sallama ya kira Asmau. Ta dauka kafin tayi magana yace cikin muryar shagwaba "Matar Jikamshi kin cuce ni" Gyara zama tayi a dan tsorace." Me nayi kuma"? "Wannan dan sandan saurayin naki wallahi yana da mutumci. I feel guilty nace ki rabu dashi gashi har yana min waya." Ta dan murmusa "to ko na barshi kai ka janye" "Ba haka nake nufi ba fa. Kawai dai naji babu dadi ne. Da kin sani wani dan caburus kika nemo wanda zanji kwarin gwiwar yiwa rashin....." ya dan toshe baki "wai shekarunki nawa ne? Kinsan dole na kula da abinda zan fada a gabanki saboda kada na bata yarinya" "Nice ma yarinyar. Shekarata ashirin da takwas fa" "Kai, kai ,kai...kada azo a kamani ina soyayya da 'yar yarinya" Asmau sai dariya take yi tana juyi akan gado, Ainau daga gefe tace "love in Tokyo" Pillow ta jefeta dashi ta cigaba da dariyarta saboda yadda Jikamshi yake mata shagwaba yau "shiyasa nace ka hakura ka janye kawai ka barwa yaro" "Ai baki isa ba yarinya. Bayan duk kin gama kashe min jiki da wadannan idanuwan naki. Na dai fada miki ina tausayinsa ne amma bance ki tausaya masa ba. Ki gaggauta sallamarsa kada ya janyo zuciyarki da kirkinsa" "Jikamshi" Sai da ya gyara kwanciya ya amsa mata "mene ne?" "Babu komai, sunan kawai nake son fada" "Shi mai sunan ba kya son shi?" "Ina so" Da sauri ta tashi zaune da ta gane abinda ta fada. Ta rasa dalilin da yasa idan tana tare dashi take manta komai tayi ta sakin baki. Ko dai ta fara zama irinsa ne??? ***** Washegari Malam Musa ya zaunar da iyalinsa ya fada musu cewa nan da sati mai
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103