Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 92

Chapter 92

Abinda Ake Gudu Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

zuwa jin ya aka kwana. Amarya mai bakin aku tayi ta bayani dalla dalla. Gani yayi duk ta damu da bakin da bata san ko su waye ba yace "nayi miki gwaninta shine kike bata rai. To kije wurinsu ina daki idan kun gama" Asmau taji wani iri. Maganarsa kadai ta sanar da ita ransa ya baci. Ya juya zai fita ta riko hannunsa "kayi hakuri Jikamshina" Ya danyi murmushi "babu komai akwai lemo a fridge kuma ina jin da cake sai ki basu" Fita yayi ya barta ta rasa yadda zatayi. Gashi yayi fushi sannan ga bakin da idan bata je ba zasu tafi da ita a baki. Haka ta yafa mayafi ta fita wurinsu. Su a takure ango ya basu kunya ita kuma ta kasa sakin jiki saboda kunyar an shanyasu a waje ga Jikamshinta yana fushi. Basu dade ba suka tafi ko irin leken gidan amarya basuyi ba tunda ansan yana gidan. Suna tafiya ta koma dakinta ta canja kays zuwa wasu riga da siket da suka fiddo da jikinta sosai. Tasha turare da kwalliya ta tafi bawa angonta hakuri. Zaune ta same shi akan wata doguwar kujera ta dakin ya gama shiryawa yana waya da alama Mami ce. Tunda Asmau ta shigo ya ganta da kwalliya da kamshin da take zubawa ya nemi fushinsa ya rasa. Hannu ya mika mata alamun ta karaso. Tana ji ya sallami Mami ya dubeta "apology accepted" Tace tana jindadi "tun kafin na bada hakurin" "Ganinki ya kori fushin amma ki sani bazan yarda da bakin nan ba. Sati biyu kawai aka bani a wurin aiki. Bazanyi sharing dinsu da bakin nan ba. Anjima zamu hada kaya gobe in sha Allah zamu je Yankari Game Reserve" Ta sunkuyar da kai ta kara bashi hakuri sannan tace "ko naje na fara hada kayan yanzu?" Ya ja hancinta "yanzu kuma ai lokacina ne ranki ya dade" ABINDA AKE GUDU🙆🏽57 Batul Mamman💖 Washegari garau ta tashi kamar ba ita ba. Sai a lokacin hankalin Col. Ishaq ya kwanta ya lallai wani satin ta huta har ta kara samun lafiya. Sun cigaba da harkokinsu cikin kwanciyar hankali ya karbo mata form din Jamb suka cike tare sai jiran lokacin jarabawa. Bayan sati daya Walida ta kirata ta sanar da ita zata kawo mata ziyara da neman shawara. Dadi ya kama Asmau ta shiga dakin Jikamshinta ta fada masa ta same shi ya mike akan gado yana baccin gajiya ko uniform dinsa bai iya cirewa ba. Daga taje ta zuba masa abinci kafin yayi wanka sai bacci. Asmau ta tsaya tana kallonsa cike da tausayi. Babu abinda baya wadata su dashi ita da Amatullah. Ji tayi a ranta inama zata haifa masa da ko 'ya mai kama dashi. Yana da tsayi da girma kana ganinsa kaga soja. Bata gajiya da kallon mijinta abin alfaharinta, komai nasa yayi mata. Fuskarsa kullum bata rabo da yi mata murmushi, idan kaga ya hade rai to yana wurin aiki ne. Amma duk da haka mutanen dake karkashinsa suna yabonsa da kirki da iya jan mutane a jiki. Col. Ishaq mutum ne mai jama'a, a irin zamansu da kyautatawarsa gareta haihuwa ce kadai tasan zata yi ta faranta masa rai sosai. Hawaye taji ya zubo mata tayi saurin sharewa kada ya gani hankalinsa ya tashi. Wayarta ta saita a kansa ta kashe flash light ta fara daukarsa a hoto. Sai da ta gaji don kanta ta juya zata fita taji ya tade mata kafa ta fado a kansa. Da farko ta tsorata sai kuma ta fasa bayan taji yadda ya riketa a jikinsa. Ta dube shi idanunsa har lokacin da alamar bacci ya sake kwantar da kansa ya rufe ido. Tace "Tun yaushe ka tashi?" Bai bude idon ba yace "tun da kika shigo kina kare min kallo mana. Ko nayi miki kyau ne" Tayi murmushi tana shafa sajensa "kullum ma kyau kake min Jikamshina. Musamman idan kasa kayan nan kamar kada ka fita" Yaji dadin abinda ta fada. Kamar yadda mata ke son a yabe su haka maza suke so suma matansu su yaba musu. Wayarta ya karba ya daukesu selfie suna yiwa juna murmushi. Bayan ya dauka yace "Matar Jikamshi kinyi kuka ko" Asmau tayi saurin kai hannunta wurin idonta zata goge sauran hawayen da tayi lokacin da take tsaye yana bacci. "Abu ne ya shigar min ido fa" "Uhmm uhm Matar Jikamshi kada mu fara yiwa juna karya. Na kuma san halinki da saurin kuka. Fada min me kika saka a ranki." A nutse yake kallonta ta sake shige masa tana jin wani hawayen na kokarin zuba. "Kawai ina tunanin abinda zanyi maka ne na faranta maka rai sosai. Kayi min komai a rayuwa har bana jin akwai matar da tayi dacen abokin rayuwa kamar ni. Har kunyarka nakan ji a raina in ga kamar bana yi maka abin da ya dace" "Babu abinda nake so daga gareki da baki bani ba. Kin bani Asmau da duk abinda Asmau ta mallaka. Adduata kullum Allah Ya bamu zaman lafiya mai dorewa." Ta amsa da amin hawayen da take boyewa suka gangaro. Ba su suka fito ba sai da Amatullah ta dawo daga islamiyya lokacin an kusa kiran magariba. ***** Bayan ya tafi aiki da safe sannan Amatullah ta tafi makaranta ta gama gyaran gida ta dora abinci. Walida na son alala shiyasa da tayiwa Jikamshi nashi abincin ta gyara wake tayi musu alala mai cike da dafaffen kwai da ta yanka kanana da kayan hadi. Kafin ta iso ta gama komai da zatayi har da juice din kwakwa da ayaba. Sai da tayi wanka Walida ta iso suka zauna hira. A hirar ne suna cin abinci Walida take neman shawararta akan abokin Col. Ishaq wanda shina soja ne kuma likita a nan asibitin barrack dinsu. Sunansa Hussaini, yana da mace daya da yara hudu. Asmau dadi ya kamata tace "ashe dai da gaske yake, Walida ki amince ni dai a dan haduwarmu a fuskanci mutumin kirki ne kuma mai addini. Yazo gidannan tare da Jikamshina yayi min tambayoyi a kanki. Dama shiru nayi sai kinji daga bakinsa." Walida tace "wato ko kunyata ba kya ji kike cewa Jikamshinki" "Don ma kada kice abin yayi yawa ne na tsaya a nan. Kinsan yadda nake ji dashi kuwa. Hmmm Jikamshi mijin Matar Jikamshi" tana magana tana kashewa Walida ido don tsokana. Ai kuwa ta kai mata dundu ta kauce suka saka dariya. Walida tace "to ya batun matarsa? Kinsan yadda muke da Anti bana son harkar kishiya. Ko shekara batayi ba a gidanmu Abba ya saki Mama. Auren shekara tara ya iya yi mata saki uku lokaci guda." Asmau tana tausayin Walida ta wannan fannin. Bata tashi tasan soyayyar mahaifiya ba kamar yadda suka sani ita da nata 'yan uwan. Tsakaninta da babarta sai anyi hutu. Shima babanta baya bari ta dade "Walida ba duka aka zama daya ba. Munje gidansa suma sun zo mana nan. Ni dai ina ganin kamar tana da kirki gaskiya duk da idan aka ce kishiya yanzu sai tunaninmu ya sauya. Ki dage da adduar neman zabin Allah. Idan mijinki ne sai kiga mun sha biki cikin kwanciyar hankali. Kada ki bari tsoron abinda baki da masaniya akansa ya sakaki ki amincewa da shi. Baki san

Table of Contents

Chapters

103 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});