Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 4

Chapter 4

Abinda Ake Gudu Book 1 Complete Hausa Novel 1,199 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

tace "kiyi hakuri Asmau. Shima ba gaggawa yayi ba. Mu kuma da kike ganinmu a nan ba jinkiri muka yi ba. Duk mai rai yana da wa'adin da Allah Ya dibar masa na rayuwar duniya. Mutuwa nada daci amma babu abinda hakuri da tawakkali ya bari." Maganganun Umma suka sake saka mutanen dakin kuka. Asmau kuwa taki bude idon. Duhun da take gani ido rufe ya fiye mata akan hasken da babu Abubakar a cikinsa. Duk yadda aka rinka rarrashinta sam taki yarda ta bude idonta balle ta tashi zaune. Suna haka suka ji sallamar Haj Yalwa da Abdulhalim. Ita da Umma suna hada ido sai kuka. Suka rungume juna suna yi ana basu hakuri. Umma tace cikin kuka "Mama Yalwa me yasa kika fito? Allah Ya jikan Abubakar....Innalillahi wa inna ilaihi rajiun" Dakin ya sake rudewa da koke koke. Bayan sun dan nutsu ne Mama ke tambayar ya jikin Asmau. Umma ta dan tabe baki "tana jinmu tun dazu ta farfado amma taki bude ido. Mama Yalwa ni dai banso fitowarki yanzu ba. Mutane zasuyi ta cigiyarki a gida. Da zamu samu ta tashi muma duk gidan zamu taho yanzu." "Zamana a gidan bazai dawo dashi ba Umma. Komai na gani ji nake kamar karya ne Abubakar yana nan." Tashi Mama tayi ta koma gaban gadon da Asmau take kwance tana hawaye. A hankali Mama ta tayar da ita zaune ta rungumeta a jikinta tana shafa mata baya. Abdulhalim yana tsaye daga bakin kofa zuciyarsa cunkushe da bakinciki. Cikin nutsuwa Mama ta soma magana "Asmau kuka ba soyayya bane tsakaninki da Abubakar. Kiyi masa addua da fatan samun rahmar Mahaliccinmu. Da iliminki amma ace kin kasa karbar kaddara? Dukkanmu nan jiran lokaci muke yi. Ki daure ki tashi indai ba kina son ki nuna cewa kinfi karfin jarabta daga Allah ba." Jin haka Asmau ta bude idonunta da suka kumbura da kyar. Dai dai ta rinka kallon mutane kafin ta sake fashewa da wani kukan mai shiga rai aka shiga tayata. Babu mai bawa wani hakuri sai Abdulhalim. Shima da ya gaji fita kawai yayi daga dakin. Likita yazo ya sake duba Asmau ya tabbatar musu cewa zasu iya tafiya da ita gida. A haka suka tafi ko da suka iso gate din gidansu Abubakar da yake shine a farko kafin nasu wani kukan ta sake fashewa dashi. Mutanen da suka zo daurin aure sun koma zaman makoki. Duk a nan suka sauka suka shiga gidan. Gaban Asmau sai faduwa yake balle da taji ana cewa ga amaryar nan ta shigo. Mutane da dama suka taso ana kallonta. Kowa na fadin albarkacin bakinsa na dangane da tausayawa gareta. Bayan sun shiga gidan dakin Mama aka wuce da ita. Ko zama batayi ba Umma tace mata taje tayi alwala saboda batayi azahar da la'asar ba. Jiki kamar wadda bata da laka haka ta shiga bandakin jiri na dibarta ta dauro alwala tazo ta biya sallolin dake kanta. Tana sallar tana zubar da hawaye. Bayan ta idar ta dade tana kuka da addu'a. Sadiya ta hado mata tea mai zafi ta mika mata. Kai ta girgiza alamun bazata ta karba ba. Kusa da ita Sadiyan ta zauna " ki daure ki sha ko yaya ne sai kici abinci. Kowa da kika gani dauriya kawai yake yi Asmau." Nata hawayen ta share sannan ta dubi Shema'u tace "Anti Shema'u kisa baki ta sha ko kadan ne". Taruwa akayi ana lallabata tasha tea din amma taki har Umma da Mama suka dawo daga waje inda suka karbi gaisuwar wasu maza 'yan unguwar. Suma suka saka baki har Asmau ta karbi tea din. Bai fi rabin kofi tasha ba ta fara kwara amai saboda tun jiya rabonta da abinci. Haka ta rinka amai ta baki ta hanci abin tausayi. Ta galabaita sosai. Bayan ta gama aman Nasiba ta dagata zata shiga da ita bandaki ta gyara jikinta ta fadi kasa a sume. Nan da nan aka taru a kanta ana mata fifita. Aka shafa mata ruwa a fuska tare da sauke mata zip din rigarta don tasha iska amma duk da haka bata tashi ba. Mama tace aje a kirawo mata Baba a waje. Ita Umma gefe kawai ta koma tana kuka. Gani take yi kamar Asmaun ma ta cika. Shi da wasu suka shigo suka ga halin da Asmau ke ciki. Jafar aka kira da Abdulhalim suka sakata a mota aka kaita wani asibitin mafi kusa dasu. Su Mama suka biyosu a wata motar kowa bakinsa da addu'a. Bayan an bata gado wata likita da nurse suka zo suka tsaya a kanta ana ta kokarin ceto rayuwarta. Allurai kala kala kam tasha su. Likitar tace jininta ne ya hau ga kuma rashin kuzari a tare da ita. Gwajin jini ta umarci ayi mata don su gani ko akwai wani ciwon a tare da ita. Har wani likitan ne yazo suka taru ana ta abu daya sannan suka samu ta farfado. Su Umma sai godiya suke ga Allah. Mama na zaune a kusa da Asmau tana sake bata baki akan tayi hakuri kuma duk da ana mata karin ruwa ta daure taci abinci sai ga nurse din ta shigo. Shema'u ta tashi da kyar Anti Bintu tace " kema kina bukatar hutu tun dazu baki zauna ba. Kada kafarki ta kumbura". Murmushi Shema'u tayi sannan ta tambayi nurse din tana fata babu wata matsala a tare da Asmau. Nurse Ngozi ta washe baki cikin hausarta irin da inyamuran da suka zauna a Kano tace "babu wani masala sai abin murna...." ta mayar da kallonta ga Asmau "...congratulations ashe ciki ne yana baka wahala." Dummmmmm haka dakin ya koma babu wani abu da yake motsi na wani dan lokaci har maganar nurse Ngozi ta gama shiga kwakwalwarsu. ABINDA AKE GUDU ๐Ÿ™†๐Ÿฝ4 Batul Mamman๐Ÿ’– Kallon kallo suka fara yiwa juna. A wannan lokacin da za'a sake auna jinin Asma'u ba karamin hawa ya sake yi ba saboda tsananin firgicin da ta tsinci kanta a ciki. Mama ce tayi karfin halin kallon Ngozi tace" 'yar jakar uba bakinki ne cikin ai, dama Hausa bata gama zama ba dole kiyi shirme. Bari likitan tazo da kanta muji daga bakinta. Kila ma ciwon ciki kike son cewa kika ce ciki zaki karasa tsorata mu." Nurse Ngozi tace "Madam ina jin Hausa sosai fa. Yarinyarki is pregnant zata haihu shine abinda nake nufi." Takardar hannunta Umma ta fizga tana karantawa jikinta ya hau rawa. Shema'u ta karbi takardar suka hada kai ita da Nasiba da Anti Bintu suka karanta. Gabadayansu Asmau suka zubawa ido da tsantsar mamaki a fuskokinsu. Mama dake tsaye a gefe ta zaro ido tana tambayarsu me suka gani a takardar. Jafar ko kallon takardar baiyi ba ya fita wurin likitan inda Abdulhalim yake tsaye tana masa bayanin magungunan da aka rubutawa Asmau. Kamar wanda aka jeho haka ya shiga office din ransa ya gama baci. Abdulhalim ya tambaye shi ko jikin Asma'un ne. Jafar yace "ai gara ace jikinta ne da abinda mahaukaciyar nurse dinnan ta rubuta. Wai ciki? Asma'u ke da ciki kamar a tatsuniya...." likitar ya kalla "...ki taso muje ki sake gwadata don kada ku karasa gawar da ba taku ba." A tare suka koma dakin wanda yayi shiru kamar ruwa ya cinye

Table of Contents

Chapters

103 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});