Chapter 30
Chapter 30
daga yanayin maganarsu ta kula a buge suke. Wanda ya danfi tsahon yayo kanta kamar zai doketa dayan yayi saurin rike masa hannu "Haba Annur, duba da kyau mahaukaciya ce. Tunda Allah Yasa bamu tabata ba kawai zo mu ware". Mai suna Annur ya ja tsaki "da ka barni na mareta. Haka kawai zata janyo mana makara a wurin party din. Sai an gama zabe fine chicks din" Ciwo ne ya sake kwasarta tayi kasa tana rike baya. Jajayen idanunta da suka rine don kuka ta daga tana kallonsu tace "don Allah ku taimaka min" Wanda ya hana a mareta yace "kai Annur it seems matar nan haihuwa zata yi". "Gaddafi bazan tsaya a wurin nan ba. Kaima kasan yanzu haka an fara nemanmu a gida. Allah Ya kawo wani amma ba mu ba. " Da sauri yaja hannun abokinsa suka shiga mota. Gaddafi ya leko da kansa ta taga yana kallon Asmau kwance a kasan gefen titi. Motoci basu da yawa saboda har lokacin goma na safe bata yi ba. Gashi titin fita gari ne. Annur ya fizgi motar da gudu Gaddafi yana rokonsa da su taimaka ko wane gari suka gani su sauketa a nan wani ya kaita asibiti. Tsaki da zagi Annur ya rinka yiwa abokinsa kafin ya juyo da motar suka dawo inda take. Ransa a bace yace Gaddafi ya shigo da ita. Kuma ya zauna a baya tare da ita saboda kada ta kai masa duka. Shi duk saurinsa ya isa party din abokinsa da za'ayi a Jos batare da sun sami matsala a hanya ba domin kuwa ko license na tuki basu dashi. Da sauri Gaddafi ya taimakawa Asmau ya shigar da ita motar. Ciwo ya fara tsananta a gareta sai gumi take yi. Annur ya soma yiwa Gaddafi magana da turanci "Tun farko da nasan haka zaka yi min da ban ce ka raka ni Jos dinnan ba. Amma babu komai zanyi maganinka. Hmmm yau 'yan matan Jos suna da manyan baki" ya karasa maganar yana wata shu'umar dariya. "Kayi hakuri Annur ni kaina bansan meyasa ta bani tausayi ba. Ji fa yadda take gumi ko magana bata iyawa. Allah Ya tsinewa wanda yayi mata cikin nan dai" Ciwon taji ya lafa mata ta kallesu tayi dan murmushi. Ga dukkan alamu Yassar zai girmesu duk su biyun. Ita ma turancin tayi musu wanda hakan yasa hankulansu dawowa gareta "Wanda yayi min ciki ya rasu fatana Allah Ya jikansa. Ku kuma ina yi muku fatan shiriya daga Allah kada ku fada mummunan hali nan gaba." Annur ya juyo kamar ba shine yake tuki ba yana kallonta da mamaki dan sauran mayen da yake duk ya tafi "wai dama ke ba mahaukaciya bace. Gaddafi kaga ka dauko mana masifa ko? Ke police ce ko 'yar mafiya?" Kasa bashi amsa tayi saboda ciwo. Yana maida kansa titi saura kadan ya bugawa wani. A haka ya cigaba da tukin Gaddafi yana yi mata sannu. Sun isa wani gari yayi kokarin tsayawa su sauketa sai ya kula da 'yan sanda a gefen wurin. Dolensa ya sake taka mota yana ta sharara gudu. Basu tsaya a ko'ina ba sai da suka shigo garin Jos. A wannan lokacin ba karamin tausayin Asmau duka su biyun suke ji ba. Wai dama hake ake nakudar gaske ba ta fim ba. Idan taji ciwo tana addua sai taji suna tayata suna yi tare. Idan ka matso kusa da motar sai ka zata duk su ukun suke nakudar, sai sharba gumi suke yi kamar babu AC a motar . Bakin gate din wani asibiti da yayi musu kama da na gwamnati suka tsaya. Sai da Annur ya taimakawa Gaddafi suka fitar da ita daga motar. Tsoronsu daya kada a kamasu ayi tunanin ko sato ta sukayi ko suna da alaka da ita. Cikin tsananin jin ciwo Asmau ta tambayi sunansu suka fada mata. "Bansan daga ina kuke ba amma ina muku fatan alkhairi da shiriya don nasan iyayenku ba rayuwar da suke yi muku fata ba kenan. A duk inda kuke ku rinka tunanin lahirarku. Nagode sosai." Daga haka ta lallaba ta karasa bakin gate din. Wannan karon sai da Gaddafi yayi da gaske Annur ya ja motar suka tafi. Kasa daga kafarta tayi taji kamar zata fadi wata mata mai uniform din masu shara da wanke bandaki ta tareta daga baya tana yi mata sannu. Daga nan bata san da yadda aka shigar da ita asibitin ba. Ko awa daya bata cika ba Allah Ya taimaketa ta haihu. Tana jin wannan kukan na jarirai taji gabadaya damuwarta ta gushe burinta kawai taga abinda ta haifa. Nurse din da ta karbi haihuwar tace mata kin sami 'ya mace. Asmau tayi murmushi tare da dago kai ta kalli kyautar da Allah Yayi mata tana hamdala. Gata da 'yar Abubakar sai dai babu shi kuma babu iyayensu. Kaddara ta riga fata a kansu. Ba don haka ba da yanzu iyayensu za'a mikawa jaririyar. A wani dan zani aka nade 'yar aka miko mata. Ta zuba ido tana kallonta. Sai kuma kuka ya kwace mata da ta tuna bata da wata hanyar kulawa da 'yar. Ko suturar da zata saka mata bata da ita. Wannan mai sharar tayi mata Allah Ya raya sannan ta fita daga dakin. Ba jimawa ta dawo da wasu tsofaffin riga da zani amma a wanke ta bawa Asmau fuskarta a sake. "Ga wannan akwai ruwa a bandaki ki gyara jikinki sai ki saka. Idan kin fito sai ki fadi wa za'a kirawo a danginki." Asmau kamar kada ta bata yarinyar haka take ji. A rayuwarta bata taba son wani kamar yadda take jin son jaririyarta ba. Tayi godiya ta karbi kayan ta wuce bandakin. Bata dade ba ta fito aka kaita dakin hutu. Wani likita yazo ya dubata yace babu wata matsala amma sai da safe zasu sallameta. Ya bata takardar magungunan da zata siya. Bayan fitarsa mai sharar ta kara dawowa wurinta ta sake tambayarta ina 'yan uwanta saboda a bakin gate ta ganta ita kadai. Ya kamata a sanar dasu ko don su kawo mata abinci da kayan baby. Asmau bata da amsar da ta wuce kuka. Matar sai ta kyaleta ta koma bakin aikinta. Ita kuma ta cigaba da kallon jaririyarta tana bacci. Ikon Allah, yarinyar kama take yi da Mama Yalwa. Asmau sai ta rantse duk 'ya'yan Mama babu mai kama da ita kamar wannan yarinyar. Dama duk sunfi kama da Alh Adamu. Da namiji ta haifa dama sunan Abubakar zata saka masa. Amma tunda mace ce zata saka sunan mahaifiyarsa kamar yadda suka yiwa juna alkawarin sai sun sakawa 'ya'yansu sunayen iyayensu. Da wannan tunanin ta danyi murmushi. Babbar matsalarta yanzu bata san ta ina zata fara ba? Bata da komai bata da kowa. Sannan bata san irin tarbar da za'ayi mata ba idan ta koma gidansu. Wannan tunanin ya isheta ga kudin asibiti duk da na gwamnati ne tasan ko yaya za'a bukaci ta biya kudin wani abin. Hakan ne yasa tana ganin duhun dare yayi ga cikinta kamar anyi mata yasa don yunwa ta kwance dankwalinta ta goya jaririyar da shi sannan ta zura hijab dinta tayi waje. Gara ta gudu tun kafin ace ta kawo kudin da tasan bata da su. Ta kusa karshen
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103