Chapter 94
Chapter 94
lokacin cikin kankanuwar murya tace *Alhamdulillah, I am pregnant*" Karfin adduar da yake a lokacin ta hana zuciyarsa bugawa. A hankali ya zame jikinsa daga nata cikin matukar kadawar zuciya ya kalleta. Murmushi take har lokacin hakan ya tabbatar masa ba karya take ba. Ta kula da kaduwarsa tace "nima ban gaskata ba sai da nayi PT dazu. Kaga ikon Allah ko Jikamshina" Bai iya cewa komai ba sai juya wa da yayi a sanyaye ya shiga toilet. Asmau tabi bayansa taji ya rufe da mukulli. Dama tasan wannan labarin ba karamin farinciki zai saka shi ba. Abu daya ne yazo kanta ko alwala zaiyi suyi nafila. Cikin sauri ta tafi nata dakin ta dauro alwala ta sako hijab ta dawo. Ko da ta shiga dakin toilet dinsa a bude yake amma baya nan. Falo taje da abin sallah biyu a hannu nan ma bata same shi ba. Tana lekawa ta taga ta hango yana fitar da motarsa daga gidan. Ta koma ta zauna da murmushi, wato ya tafi fadawa Hajiya. Gara da bai nemi ta raka shi ba ai da taji kunya. Shiru shiru har shadaya ta wuce bai dawo ba. Tana ta kiran wayarsa baya dauka sai daga baya ta ga wayar a daki. Hankalinta ya soma tashi amma bata son kiran Bilkisu ko Hajiya ayi zaton ta kasa hakuri daga miji ya fita. ****** Tuki yake bashi da wurin zuwa. Zuciyarsa ce take zafi har gumi yana karyo masa. Me yasa Asmau zata yi masa haka, yana da tabbacin tana son shi da zuciya daya. Amma waye ya fada mata lallai sai ta haihu zai cigaba da sonta. Ya dade da karbar kaddararsa me yasa ta aure shi idan bazata iya hakurin zama dashi ba. Waye ya bata wannan muguwar shawarar. Waye yayi sanadin rushewar farincinkin da yake bakin kokarinsa wurin ganin ya tabbata a rayuwar aurensu. Gefen titi yayi parking saboda baya ganin gabansa sosai. Zazzafan hawaye ne ya cika masa ido har yake ganin duhu. Ajiye girmansa yayi da mukaminsa yayi kuka, kuka na bakinciki da bacin rai. Kukan rasa mafita ga halin da abar sonsa ta saka shi a ciki. Sai da ya gaji da zaman ya rinka karanto addu'o'in neman sauki sannan ya koma gida. Asmau na zaune a falo a haka bacci ya dauketa. Zuciyarsa ta sake karaya da ya ganta rungume da abin sallah tana bacci ga Amatullah a kusa da ita. Dukawa yayi ya dauketa ya kaita nata dakin ya dawo ya tsaya yana kallon Asmau. Sai da ya daure zuciyarsa ya iya tabata ta bude ido a hankali. Magana taso yi ta kula da ja da kankacewar idanunsa. "Tashi kije ki kwanta" Bai bari tayi magana ba ya shige ya barta a wurin fuskarsa a daure cikin tsananin bacin rai. Yau da gobe tafi karfin wasa. Asmau ta fuskanci rayuwa irin wadda bata fatan wata mace ta gani. Yanayin da taga Jikamshinta ya sha bamban da abinda tayi tsammani. Wannan kadai ya bata amsar shirunsa da fitarsa daga gidan. _ZARGI_ irin wanda Allah Kadai Ya isa Ya wawarewa bawa. Sai dai abin mamaki gane hakan bai sata kuka ba. Ashe kuka wuri yake samu, ashe kuka rahma ne. Hannu tasa ta dafe kirjinta da taji yayi kamar an daure shi tamau ta kashe fitila da tv ta tafi daki. Duhu ta gani alamun ya kwanta sai ta koma nata dakin ta sako kayan bacci ta dawo. Tana kwanciya ashe a kansa ne saboda ya raba gadon ba kamar yadda ya saba ba. Yau a tsakiya ya kwanta. Ji tayi yana kokarin matsawa tayi saurin tashi tana bashi hakuri amma bai amsa mata ba. Bata yi fushin ta bar masa dakinsa ba ta koma gefen gadon ta kwanta. Sai karfe takwas saura mintuna ta tashi a makare. Wayam ta ga baya dakin. Ta fita da sauri motarsa bata cikin gidan. Jikinta yayi sanyi ta koma tayi sallah da ya saba tashinta idan zashi masallaci. Ta shiga dakin Amatullah ta tarar bata nan ga kayan baccinta a kan gado. Dan murmushi tayi ko babu komai bai dena kyautatawa 'yarta ba. Haka Asmau ta yini ranar da kuncin zuciya. Duk bayan lokaci sai ta duba wayarta ko ya kira ko text amma babu ko daya. Haka ta ke zaunawa ta tsara masa kalamai masu ratsa zuciya ta tura masa. Idan ya gani a take yake gogewa. Sai yanzu yake nadamar auren Asmau yana mai nanatawa kansa tambaya daya *cikin jikinta na waye?*. ***** Sati guda suka yi baya mata magana kuma baya shiga sabgarta. Ita kuma tayi alkawarin bazata takura shiba har Allah Ya sauketa lafiya. Daurewa take tana nunawa kamar babu abinda ya faru ta cigaba da yin abubuwan kyautata masa ko da bazai kula ba. Walida ta kirata taji yaya murnarsa da ta fada masa tana da ciki ta shirga mata karya don ta rufawa mijinta da kanta asiri. ABINDA AKE GUDU🙆🏽58 Batul Mamman💖 A daddafe take iya yin komai. Cikin da alama mai laulayi ne domin bata son warin komai ga yawan tashin zuciya. Rashin wadataccen abinci yasa ko aman yazo sai dai tayi wahalar banza babu komai a cikinta. Cikin dan lokaci ta fada. Babu wanda ta iya fadawa damuwarta sai Allah. Kullum sallah take da karatu tana mai tsananta addua da neman mafita. Idan ta damu da yawa ta kira Umma suyi hira taji sauki a ranta. A nasa bangaren Col. Ishaq ba karamin jigata yayi ba da rashin Asmau. Sonta yana nan a ransa amma yana kyamar halin da ta jefa su a jiki. Har yau ya rasa matakin da zai dauka bayan fita harkarta da yayi. Gidan yayi musu zafi duk su biyun. Gado daya suke kwana ya juya mata baya. Haka zata yi bacci tana kallon bayansa tana hawaye. Ranar asabar lokacin sun dauki sati uku a wannan yanayin tana fitowa daga kitchen shi kuma zai shiga daukan cup ya hada tea. Kallon kallo suke yiwa juna ta matsa ta bashi hanya. Yana shiga ya bugo kofar da kafarsa ashe hannunta na wurin kofar ta matse. Ciwo taji har tafin kafarta tayi kara cikin zafin nama ya bude kofar. Hannun ta rike sosai tana fitar da hawaye ta kasa tsayuwa wuri daya don azaba. Mantawa yayi da fushinsa da komai ya kama yatsun nata biyu da yaga ta rike ya shigar da ita kitchen ya sakar mata ruwa. Idonta a rufe tana kuka a hankali. Ciwon bai dameta ba kamar yadda Jikamshinta ya canja mata. Har zuciyarsa yake jin kukan tana bashi tausayi sosai. Ya soma hura mata yatsun amma yana gani har sun fara kumbura. Fuskarta yake kallo itama yau bata kawar da nata idon ba ta zuba masa ido. Yadda ta rame shima haka ya rame. Yana rike da hannun ya kai yatsun nata bakinsa ya saka a ciki. Kallonsa kawai take tana kara sonsa duk da halin da suke ciki a lokacin. Kusan minti uku yatsunta na bakinsa sannan ya cire yace "kinji sauki ko nasa miki kankara" Yaushe rabon da yayi mata magana. Ita da jin muryarsa sai dai idan waya yake. Girgiza kai tayi ta janye hannunta ta tafi. Wani iri yaji, yunwar ma ta fita a kansa sai rudani na rashin sanin yadda zaiyi da Asmau. Dakinta ya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103