Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 95

Chapter 95

Abinda Ake Gudu Book 1 Complete Hausa Novel 1,197 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

bita ya sameta zaune a kasa a kuryar gado tana kuka a hankali. Bai ce mata komai ba ya bude inda take ajiye mayafai ya dauko mata wani kato mai kauri. Tayar da ita yayi tsaya ya yafa mata sannan ya riko hannunta suka fito falo ya dauki mukullin motarsa. Cigaba yayi da jan hannunta har gaban mota. Ya bude mata ta shiga ta zauna sannan ya cewa Mal Sabo idan ya dauko Amatullah ya kaita gidan Ismail. Sai ta kula ya mikawa Mal Sabon wata karamar jaka wadda take tunanin kayan Amatullah ne a ciki. Da ya zauna ya tayar da motar Ismail din ya kira ya fada masa za'a kawo Safina kila ta kwana. Shi kuwa sai murna yace dama yana gida. ***** Barrack dinsu suka je bangaren asibiti. Ita dai binsa take a baya har suka shiga ciki. Wani office ya shiga ya barta a reception. Ba dadewa ya fito yace ta shigo. Hussaini ne a ciki sanye da kayan sojoji amma ya dora coat din likitoci. "Ranki ya dade sai ki zauna a waje kuma? Sir kasan fa ita ce mai hadani da Walida ya kamata ka tayani kamfen" Duk su biyun ya kula babu wanda dan guntun wasansa ya bawa dariya. Shima sai ya ci serious ya koma mazauninsa. Yasan yau abokin nasa a matsayin shugabansa ya shigo. Col. Ishaq ya kamo hannunta da ya matse wanda yatsun sun kumbura faratan kuma sunyi jawur alamar taruwar jini daya har ya fashe ta saman farcen "Doctor a duba mata hannun nan bana so ya zama babban ciwo" Hussaini ya kallo hannun sai ya dauki waya ya kira nurse aka zo suka tafi da Asmau yace ayi mata dressing. Bayan sun fita yace "ai yadda na ganku ne har naji tsoro ko anyi fadan masoya ashe amarya ciwo taji" "Kaga ba batun wasa ina so duk wani test da akeyi a gano ciki kayi mata please" Hussaini ya mike da sauri "Sir ciki??? Iko sai Allah, bashi da abokin tarayya. Lallai Allah maji rokon bayi." Col Ishaq yayi masa wani irin kallo "me kake nufi ne? Kafi kowa sanin matsalata yanzu na fada maka zancen ciki kuma kana murna" "Wannan ai abin farinciki ne da murna. Bari na fada musu ayi test din Allah Yasa akwai. Kai da kaina zanyi mata ma" Ran Col. Ishaq ya soma baci yace "Hussaini bana son wasa. Kada ka manta banda dangina bani da wani amini sama da kai. Kai kadai na fadawa komai game da Asmau kafin na aureta. Sauran a gari suka ji idan har sun sani. After all these years aure kasa da shekara ko wata shida bamuyi ba tace min tana da ciki" muryarsa tayi rauni sosai dauriya ce kawai yake. Zama Hussaini yayi a kujerar da take kallon ta Col. Ishaq hankakinsa a tashe. "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un. Kada kace min zarginta kake yi. Col. Ishaq Jikamshi waye ya fada maka bazaka taba haihuwa ba? Na tabbatar ba ni bane" Maganar ta fara daure masa kai yace "ku likitoci kun iya boyewa mutane zahirin abu sai kuyi ta rufa rufa don kada ku tsorata patient. Ka gwadani ka kuma hadani da likitocin da lalurata ta shafe su. Kowanne sai ya cemin lokaci ne baiyi ba. wane magani ne ban sha ba. Sai gashi Badar ta haihu daga yin aure. Wannan ya tabbatar min ni nake da matsalar. Nine bana haihuwa " Hussaini ya jima yana kallon abokinsa kafin yayi magana "idan ni ko wasu a nan zamu boye maka idan bazaka taba haihuwa ba, asibitocin da kaje a kasashen waje kasan bazasu yi maka karya ba. Babu wanda ya kai bature baro baro. Sai ya fada maka nan da lokaci kaza zaka mutu. Duk wani sakamakonka kana bani copy na ajiye. Babu inda akace bazaka taba haihuwa ba. Dukkansu suna cewa ko dai akwai matsala a mahaifar Badariyya ko kuma wani dalili dai ya hana cikin samuwa amma ba rashin lafiya gareku ba." Col. Ishaq ji yayi ya fara jin zafi. Me Hussaini yake nufi. Wai zai iya haihuwa???. Hussaini ya cigaba "idan wasu zasu boye maka ni bazan bari kayi ta kashe kudi kamar baka san zafin nema ba akan haihuwa alhalin nasan bazaka samu ba. Garin yaya ka yankewa kanka wannan shawarar har kake zargin matarka. Allah Sarki shiyasa naga ta kasa magana da kuka shigo. Bani da masaniya game da Asmau bayan abinda ka fada min amma bana jin zata aikata wannan mummunan aikin gareka. Kada ka manta taga rayuwa a dalilin kuskuren farko. Wallahi ni ka kara tsoratani akan zina. Idan har zaka zargeta duk son da kake mata lallai har a nade duniya fentin zina bazai taba barin Asmau ba. Ya Allah Ka nesantamu daga wannan bala'i " Jikin Col. Ishaq ya gama sanyi kam yanzu. A lokacin da Asmau tayi masa albishir da samun karuwa a lokacin tarihin rayuwarta ta baya ya dawo masa har yake tunanin ko a garuruwan da ta zauna ta cigaba da mugun aiki. Tashi yayi da sauri Hussaini ya dakatar dashi "ka jira nayi mata gwaji a tabbatar" Zama yayi amma jinsa yake a kan kaya. So yake ya ga Matar Jikamshi a jikin Jikamshinta. Wani irin sonta yake ji na daban yana ratsa shi. Gabadaya yaji ya tsani kansa da zuciyarsa da ta raya masa wannan mummunan zargi.. Tana zaune an saka mata bandeji a yatsun Hussaini ya shigo dakin da suke. Nurse ya bawa umarni ta debi jininta nan da nan ya karba ya tafi lab dinsu. Da kansa yayi gwajin har sau biyu ya tabbatar babu karya Asmau tana da ciki. Dawowa yayi yayi mata tambayoyi wanda tana amsawa tana hawaye. Yaji tausayinta sosai sannan suka koma office dinsa. Ko da suka shiga kunya ce ta kama Col. Ishaq ya kasa yi mata magana. Hussaini yana murmushi yace "congrats Sir, uwargida tana da ciki wata na uku kenan. Zan bata appointment idan tazo sai a bata maganunguna ayi scanning domin ganin lafiyar baby. Allah Ya inganta Ya raba lafiya." Col. Ishaq kamar yayi me don murna. Yana cewa Amin ita kuwa Asmau ta fita daga office din saboda kukan da yazo mata. A bakin mota ya sameta bayan Hussaini ya nanata masa lallai yayi kokarin shawo kanta saboda yayi mata laifi. Sun shiga mota sun zauna bata ko kalli inda yake ba. Shiru suka yi yaja motar sai gidan Hajiya. Ta goge idonta sannan tabi bayansa suka shiga ciki. Hajiyan na daki tana kashingide ya shiga da sallama. Ta tashi zaune tana amsawa. Asmau ta tsaya a bakin kofa kawai sai ji tayi ya kama hannunta ya ja har gaban gadon Hajiya. Kunya kuwa daga ita har Hajiyan. Zama yayi a kusa da ita a kasa sai ta fashe da kuka Hajiya tace "lafiyarku kuwa, me kayi mata" Baya son kukan Asmau haka kuma baya son bacin ranta wanda shine ya haddasa mata. Kansa a sunkuye yace "Hajiya daga asibiti muke yanzu, tana da ciki wata biyu" *Alhamdulillah....* Hajiya ta fada sai kawai ta rungumo Asmau jikinta. Abin mamaki kuka ta saka Asmau na tayata. "Waye yace babu Allah? Allah sarkin dukkan mai sarauta. Ubangijin Annabi Adamu tsira da AmincinKa ya kara tabbata ga Annabi Muhammadu SAW. Ban taba fitar da

Table of Contents

Chapters

103 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});