Chapter 103
Chapter 103
bata taba ganin wani abu daga gare shi da zai sa taji ya ware Amatullah saboda ba tasa bace ko kuma yanayin haihuwarta. Shiyasa a kullum bata gajiya wurin saka shi a adduarta. Abdallah na da wata uku Yassar ya dawo daga short service dinsa ya dage shi fa aure yake so. Ga ginin da Umma take yi masa da saura amma haka ya hada har da nasa 'yan kudin kafin aiki ya kankama. Bilkisu ta kunno shi sosai akan maganar aure kuma ya zama irinta. Dama zama dasu Jikamshi sai an koyi hali. Iyaye dai sunyi murna kuma an saka rana. Bikin Walida ma ya tashi su Asmau sunyi rawar gani. Sai da aka gama ta fara shirin makaranta an gama komai. Jikamshi ya cika alkawari bai hanata ba. Yarinya ta samu suke tafiya tare tana rike mata Abdallah idan zata shiga aji. Yana da wata tara amma da girmansa ga kamaninsa da babansa kamar yayi kaki. A haka ne wata rana ta tashi da safe da amai ko makaranta ta kasa zuwa. Gwajin farko ta gane ciki ne. Murna a wurin Col. Ishaq kamar cikin farko. Yayi ta tattalin matarsa. Dole ta yaye Abdallah ga karatu. A haka tayi ta fama har ta haifi 'yarta mace wannan karon a asibiti. Yarinya taci sunan Hajiya wato Lubabatu amma suna kiranta Amaturrahman. *Bayan shekara uku* Asmau ce tsaye a kofar dakin yaranta suna bacci. Amatullah da Amaturrahman akan gado suna rungume da juna. Shakuwarsu har ta baci. Saboda Amatullah bata iya fadin sunan kanwarta sosai itama idan an tambayeta sunanta sai tace Amatuyyahman. Duk yadda mutum yaso gyarawa sai tace ba haka Yaya take fada ba. Abdallah yana kwance a kan nasa gadon ga kayan wasa sun baza. Hannuwan Jikamshinta taji ya rungumeta ta baya tare da dora kansa a kafadarta. A daidai kunnenta yake magana "Tunanin me kike yi Matar Jikamshi?" Kwantowa ta sake yi a jikinsa tace "ina godiya ga Allah akan ni'imarSa gareni." Hannunta yaja suka tafi dakinsa ya tura kofar da kafa. Yana juyowa yaga tana hawaye. "Allah nagode Maka baki da aiki sai kuka. Ni kaina daga haduwarmu zuwa yanzu sau nawa kina sani kukan nan. Yau kuma me ya faru?" "Ina tsoron ranar da yaran nan zasu tsaneni. Gara gara ma su Abdallah amma Amatullah sai taji ina ma bani bace mahaifiyarta. Me zan fada musu a lokacin da suka kara wayo mutane suka sanar da su mamansu ta taba ciki a waje? Ya zanyi da Amatullah idan ta tuhumeni da gurbata mata asali? Idan suka kyamaceni yaya zanyi da rayuwata?" Kuka take yi da gaske. Kwantar da ita Jikamshi yayi ya kwanta kusa da ita kanta yana kan kirjinsa. "Daga ranar da kika ji rasuwar Abubakar da batun cikinki kin taba tunanin zaki kara samun nutsuwa a rayuwarki?" "A'a" "To a yanzu Allah Ya kyautata miki rayuwa ko kuwa?" "Ya kyautata min" "Ina so ki sani cewa tunanin gaban da baki gani ba babu alkhairi a ciki. *Abinda ake gudu* ya riga ya faru. Adduarmu shine Allah Ya kara karemu daga sharrin shaidan da mukarrabansa. Yara kuma da kike tunani bazasu taba guje miki ba da izinin Allah. Ke dai kiyi iya yinki wurin basu tarbiya da nuna musu so irin na uwa, sauran kuma mu barwa Allah. A karshe Matar Jikamshi, Asma'un Ishaq ina mai kara shaida miki idan duniya zata gujeki in sha Allah bazan taba rabuwa dake ba. Kece Ishaq, Ishaq kuma Asmau. I love you with all my being" Kara rungumeshi tayi sosai tana hawayen farinciki "I love you too Jikamshina. Allah Ya barmu tare" Suka ce Amin a tare. ***************** *ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH* Ina godiya ga Allah da Ya bani ikon gama wannan labari. Ina fata Allah Yasa mu amfana da abinda yake cikinsa wanda yake daidai. Kuskuren dake ciki Allah Ya yafe min Ya kawar da hankulanmu daga aiki dashi. Allah Ya karemu daga abinda ake gudu. Godiya mai tarin yawa gareku masoya wannan labari. Hakika kun cancanci yabo domin kun bani kwarin gwiwa sosai. Bazan kama suna ba domin kuwa kuna da yawa kada nayi abinda ake gudu na manta da wasu. Allah Ya saka muku da alkhairi. *Gaisuwa gareku* matan 1.Batul Mamman novel grp 2. Yan uwa na Fikrah writers association. 3. Taskira 4. Rufaida Omar fans 5. Maryam Ameen novels 6. Tafeesu novels 7. RAZ novella 8. Zauren Biebee Isah 9. Feenat Jaafar novels 10. Mss MJay novels 11. Hausa novels only 12. Hausa novels xallah 13. Zauren karatu 14. Fairytopia novels 15. Rash kardam novels 16. Queen Meemi fans 18. Fati Ali novels 19. N,N $ Z novels Da wadanda ban saka ba duk ina godiya da mika sakon gaisuwa.
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103