Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 48

Chapter 48

Abinda Ake Gudu Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

da ita a zuciyarsa. Har mamakin kansa yake yi. Bai yarda sonta yake yi har haka ba sai bayan 'yar hirarsu ta dazu. Yana son muryarta, kunyarta, yanayinta....ya dan shafa kansa yana murmushi ya tura mata da text "Asmau Ummin Safina ki shirya, don Jikamshi da gaske yake. Kiran wayarki kuma yanzu na fara. Gudnyt" ***** Hannunta har rawa ya soma bayan ta karanta text din. Wani abu taji ya ratsa jikinta gabadaya don dadi. Bayan Abubakar bata taba tunanin sake jin wani abu makamancin wannan akan kowane da namiji ba sai akan Col I.M Jikamshi. Sai dai kuma wutsiyar rakumi tayi nesa da kasa. Yaudarar kai ne ma ta yarda wani abu yayi nisa tsakaninsu. Tafi kowa sanin ko ita wacece, bata cikin mata da zasu sami rabon aure a wannan duniyar. Dadin dadawa Jikamshi ba karamin mutum bane. Yana da wata kima ta daban a idonta, sam bazata so suyi rabuwa mara dadi ba. Gara tun ba'a soma ba kada a fara. Tana wannan tunanin ne bacci ya kwasheta. Washegari Umma ke fada mata su fara shiri nan da kwana biyu zasu tafi Zaria da Aina'u. Sati daya zasu yi daga nan zata zo ta same su su wuce Wushishi. Jin zata je Zaria wurin Anti Bintu yasa ta farinciki har ta dan manta da tunanin da ta kwana ta tashi dashi. Shirye shirye suke yi daga ita har Aina'u sun hada kayansu da komai. Yassar ne zai kaisu ya dawo washegari. Da yamma ne ta tafi gidan Jafar saboda yace yana son ganinta tace ya bari zata zo da kanta. A gida ta bar Amatullah tana bacci. Sun dan taba hira da Sabira ta tashi ta basu wuri. Ba wani dogon abu bane maganar karatu yayi mata wanda yace sunyi shawara ne da Shemau zasu hada kudi su biya mata ta koma makaranta. Kuka take yi sosai kamar yasan abinda take son yi kenan. "Yaya Jafar Allah Ya saka da alkhairi. Nagode sosai, nima abinda yake raina kenan don bana son nayi ta zaman haka." "Kada ki damu Asmau. Ina so ki manta da rayuwar baya kiyi kokarin gina rayuwa mai kyau daga yanzu. Kada ki manta ko ke wacece a duk inda kike. A yanzu da kika dawo gida inda mutane suka sanki suka san labarin rayuwarki ki zauna da shiri na fuskantar kalubale kala kala. Dole duk inda kika shiga kiji maganganu marasa dadi daga bakin mutane daban daban. Abinda nake bukata daga gareki bai wuce ki toshe kunnuwanki ba. Komai yayi farko yana da karshe. Ki mayarda dukkan lamarinki ga Allah sai kiga kinyi nasara." Tayi murmushin takaici "hakane, kuma nagode da shawararka. Dole ne nayi hakuri da dukkan abinda mutane zasu ce game dani da Amatullah. Irin labarinmu dai da wuya yake zama tarihi. Duk wanda ya sanmu duk sanda muka hadu sai sun tuna. Wannan kaddara har jikoki idan da rabo nasan za'a goranta musu wata rana" ta kare maganar da kuka. Tausayin kanwarsa yaji sosai. Ya dade da sanin cewa illar zina tana bibiyar mutum duk inda yaje. Musamman idan akwai haihuwa tsakani. Fatanmu kawai Allah Ya tsare mana imaninmu Ya karemu daga fadawa sharrin shaidan da mukarrabansa. "Ki tsarkake zuciyarki Asmau, daga nan ki barwa Allah komai. Rayuwa ce kowa da irin tasa. Babban abin dubawa dama shine tuba da komawa ga Allah. Idan kika yi haka to babu ruwanki da zancen mutane. Duk wanda ya fiye bibiyar kuskuren dan uwansa don tonon asiri to Allah na kallonsa kuma Shine Yasan yadda zaiyi da bayinSa." Godiya ta sake yi masa har ta kira Shemau tace zata je har gida tayi mata godiya. Dan uwa rabin jiki inji bahaushe...banga mai kamarka ba. Abinda suka aikata ita da Abubakar ba su kadai yake bi ba domin kuwa tasan za'a nuna iyayensu da 'yan uwansu idan dalili ya kawo suma a goranta musu. Kai zina laifi ce mai muni, kazanta ce mai kaskantar da mai daraja. Ya Allah Kasa mufi karfin zukatanmu. Masu neman aure maza da mata Allah Ka basu abokan rayuwa nagari. Mu kuma Ka bamu zaman lafiya da wadanda Ka hadamu dasu. ***** ASP Qasim zaune gaban mahaifiyarsa ya gabatar mata da zancen Asmau wanda ta dade da sanin kudurinsa akai. "Baba ni bazan hanaka aurenta ba. Babanku ma yace ya amince da auren. Abu daya nake so da kai shine ka tuna dukkan abubuwan da suka faru. Naso kwarai kayi aure kafin yanzu ta yadda ko ka auri Asmaun zaka hadata da wata matar" "Inna kenan, kina gudun ita kadai ta kasance surika a gareki saboda tana da 'ya kafin tayi aure?" "Dan nan yau da gobe sai Allah. Mutane da bakinsu bazasu fasa surutu ba" "Amma Inna nasha fada miki ina gudun zamansu da kishiya yaki dadi saboda gori. Da bata dawo ba kamar yadda kika bukata a shekarar nan zan nemi aure. Ku cigaba da yi mana addua." Ta kada kai "Allah Ya tabbatar mana da alkhairi. Haj Yalwa tace zata zo dasu su gaishe da Malam. Allah Ya kiyaye hanya" Qasim ya tashi ya leka dakin mahaifinsa har lokacin bacci yake yi. Shiryawa yayi cikin wani yadi mara nauyi ruwan toka yayi kyau sosai ya kama hanyar Kano daga Shanono. Ana magariba ya iso. Gidan Mama ya fara zuwa suka gaisa sannan ya kira Asmau ya fada mata zai zo idan an idar da sallar isha. Umma taje ta sanarwa. "Allah Sarki Qasim, gaskiya ya rike amana. Ji yadda yake kokarin kula daku duk da ba a garin nan yake aiki ba. Allah Ya biya shi da mafificin alkhairi." Asmau ta amsa da amin tana gyara goyon Husna da tayi. Suna cikin hira Qasim yayi sallama Umma tayi masa izini ya shigo. Cike da ladabi ya gaisheta ta amsa fuska a sake. Daga nan ta tashi ta bar falon ta koma dakin Hajjo. A nan ta sanar da Amatullah zuwan Qasim daya baban nata ta fito gaishe shi. Qasim ya ajiye kofin lemon dake hannunsa yana maida hankalinsa Asmau. "Asmau magana nazo muyi, ina fata zaki saurare kuma ki fahimceni." "Ina jinka Yaya Qasim" "Asmau kinsan irin shakuwa da abotar dake tsakanina da marigayi Abubakar" Ta gyada kai tana tuno masoyin da bazata taba mantawa ba a tarihin rayuwarta. "Duk abinda ya gudana a rayuwarku na sani na kuma san nima akwai sa hannuna a ciki. Bazan gaji da rokon gafararki ba saboda ance karfe daya baya amo. Kamar yadda kawa ta ribaceki haka nima nayiwa Abubakar, ga kuma sakamakon hakan duniya ta gani. Asmau tun kafin ki dawo na yanke shawarar aurenki ko a wane yanayi na sameki. Cikin ikon Allah yanzu na tsinci kaina da tsananin kaunarki" A razane ta dago kai ta kalleshi ta mayar da kanta kasa. Yayi sassanyar dariya "Nasan dole kiyi mamaki sai dai kuma ki sani burina ba wai na maye gurbin Abubakar bane. Ina so ki bani dama a matsayin masoyi na sami kaunarki na kuma zama uba ga 'yata Amatullah." Wannan shine ana wata ga wata. Ita fa ko kadan bata son maganar aure ma yanzu. Qasim wani babban jigo ne a rayuwarta saboda yadda ya damu da lamarinta da na Amatullah. Ya rike amanar Abubakar ba da wasa ba. "Yaya Qasim bani da abinda zance maka

Table of Contents

Chapters

103 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});