Chapter 66
Chapter 66
sai hudu da rabi ake tashin yara. Ga karatun Qur'ani ba kama hannun yaro. Ita dai Asmau sai son barka. Kowa na kokarin kyautata musu. Shemau taso ace a makarantar da nata yaran suke zuwa aka saka Amatullah. Da yake saura sati daya hutun makaranta gwaji kawai aka yi mata suka bata aji, kayan makaranta da litattafai. Karatu sai an dawo zata fara sosai. Abdulhalim ya biya kudin komai. Alh Adamu ya kara masa kudi don kada ya shiga matsi tunda yana da nasa yaran. Amma yaki karba Amatullah 'yarsa ce baya bukatar taimakon kowa. Da ya dawo da ita gida kuwa an sha labarin sabuwar makaranta. Tana ta zuba zance akwai lilo da wurin computer irinta Uncle Yassar. Hajjo da Umma kadai ke amsa mata. Asmau na rike da waya a hannu tana ta kiran Jikamshi ta kasa samu. Bata jima da ajiye wayar Qasim ba yace mata iyayensa suna so a sake basu ranar da zasu dawo. Umma ce ta lura da yadda take ta tsaki ga waya a hannu tana ta dannawa. "Asmau wa kike nema ne haka? Kinsan dai wani lokacin network sai yaki dadi amma duk kinsa abin a ranki sai tsaki kike faman yi." Amatullah tayi caraf tace "kuma ni ta hana ni yi, wai tsaka ce yake yi" Ran Asmau yayi mugun baci ta kai mata duka ta sameta a gefen fuska "ban hanaki idan manya na magana ki saka baki ba. Tashi ki bar wurin nan kafin na kara miki" Kuka sosai Amatullah take yi don har dankunnenta sai da yayi tsalle. Umma da Hajjo har suna rige rigen janyota jikinsu. Umma itama ta harzuka tace "wane irin rashin hankali ne wannan Asmau. Daga tayi magana sai duka." Hajjo tace "kuma dukan ma a fuska, tayi kuskure don ba'a so a koyawa yara saka baki a zancen manya. Amma ya zaki mata hukunci irin wannan. Ji yadda dankunne ya karce ta" Suna kokarin jan Amatullah amma taki tsayawa. Da Hajjo ta saketa jikin Asmaun ta koma tana kuka "Ummi kiyi hakuyi na dena" Kuka Asmau ta saka, tasan bata kyauta ba don fushinta ta saukewa Amatullah. Ga zuciyarta dama ta gama rauni. Bata samun Jikamshi shima baya kira sosai sannan Qasim yana jiran amsarta na ranar da zasu dawo. Amatullah ta sake cewa "Ummina kin hakuya?" Cikin kuka ta rungumeta sosai a jikinta "na hakura Ama" "To ki dena kuka nima na dena"Amatullah ta fada tana share hawayenta. Wannan ya kara karyarwa Asmau zuciya ta cigaba da kukanta bilhaqqi. Umma da Hajjo suka tsaya kallon ikon Allah. Sai da tayi mai isarta ta dauki Amatullah suka shiga ciki. Suna tafiya Hajjo ta rike baki "Bara'atu anya yarinyar nan bata da mutanen boye? 'yan kwanakin nan na lura tana cikin damuwa. Wannan kukan ma da biyu ko uku ma zance take yinsa." "Nima haka nagani, bari naje naji ko menene" ***** Dariyarsu Umma ta fara ji Asmau tana bin Amatullah tana cewa zata shafa mata dettol a wurin da dankunne ya karceta ita kuma tana zagaye gado da gudu. Umma ta rike baki kawai. Asmau da Safinanta sai Allah. Tare suka ga wahalar rayuwa shiyasa shakuwarsu take bawa mutane sha'awa. Sakin fuska tayi ta shiga ta daga Amatullah. "Gudu wurin Hajjo kinji yarinyar kirki." Ta fice kuwa a guje tana dariya. Asmau kunya ta kamata ta ce "Umma kiyi hakuri don Allah". "Bakiyi min komai ba Asmau. So nake ki fada min abinda yake damunki. Ba'a so damuwa tasa iyaye su rinka hucewa akan 'ya'yansu. Amatullah bata kyauta ba da tayi magana amma ba da haka zaki tsawatar mata ba. Ko don gaba ki kiyaye" "In sha Allah Umma. Nagode" Wuri Umma ta samu ta zauna tace "zauna Asmau, magana zamuyi" Murmushi ta kirkiro "babu komai fa Umma, haushi ta bani ne" "To na tashi kenan tunda kina da wanda zaki fadawa matsalarki bayan ni" Daga magana kamar ance fara kuka kawai ta kwantar da kanta a cinyar Umma ta soma kuka. Tausayi ta bawa Umman ta fara rarrashinta "komai yayi tsanani maganinsa Allah. Yakamata ace kece mai fadawa wani hakan. Wa kike nema a waya har abin ya bata miki rai haka" Muryarta har ta dan shake tace " idan mutum ya dena nemanka a waya sosai alama ce ta ya hakura da kai ko, ko kayi masa laifi" Duk da Umma tasan wa Asmau ke so sai tace "waye baya kiranki a waya" Rufe bakinta tayi da sauri. Maganar ce take cinta amma bata yi niyar fada ba. Dan murmushi Umma tayi. Tun ranar da suka hadu da su Hajiya a asibiti kafin Anti Bintu ta koma Zariya ta fada mata yadda suka yi da Col. Ishaq. Ta sauke ajiyar zuciya "Ishaq ne baya kiranki?" Sake sunkuyar da kai tayi ta kasa amsawa. Umma tace "ki yawaita addua da neman zabin Allah nima zan tayaki." Abinda yake ta cin ranta ta kasa boyewa "cewa yayi zaiyi magana da Hajiya, ina jin saboda Amatullah bata amince ba. *Umma nayi kuskure ne da ban zubar da cikin ba na haifeta*? Wannan karon Umma ma sai hawaye "ko kadan Asmau. Haihuwarta shine maslaha gareki damu baki daya. Mun so bin son zuciya da muka dage sai kin zubar da cikinta. Ki duba ki gani yadda Allah Yayita mai kokari da ladabi. Kema kinsan ba iyawarki bace kawai tasa kike da yarinya mai tarbiya kamarta. Mata da yawa da iyayensu sukan gujewa kunyar duniya su zubar da ciki ko a yar da jariri. Sai anje lahira kuma ido ya raina fata. Ga laifin zina ga na zubar da ciki ko kashe jinjiri. Ko ki sami miji ko kada ki samu ki sani cewa rayuwarki ibada ce. Hakuri da tawakkali shine ginshikin farincikin dan adam. Batun Ishaq kuma kada ki damu zai nemeki da kansa ku kare magana. Da shi da Qasim wanda duk Allah Ya zaba miki ko waninsu sai mu ce Alhamdulillah. ABINDA AKE GUDU🙆🏽47 Batul Mamman💖 *Maman Farida mai Hanyar Ruwa. Ina gaisuwa da fatan alkhairi. Ga naki shafin yar uwa* *Amina Yau, Jikamshi yana gaisheki da kyau.* *Shafaatu mai masaukin baki a gidan Batul ina godiya* *Masu sakonnin gaisuwa bazan taba mantawa daku ba. Allah Yayi mana jagora* Sai yanzu Asmau ta dan sami nutsuwa a ranta. Tun da Jikamshi ya dena kiranta sosai ta fara tunanin ko Hajiyarsa ce bata amince ba. Amma yanzu Umma ta kwantar mata da hankali. Zata sake nemansa daga yau zuwa gobe. Idan taji shiru to zata bar komai ga iyayenta. A yanzu dai Umma da Mama Yalwa sun riga sun san da maganar Col. Ishaq. Mama har fada tayi da basu fada da wuri ba sai a asibiti ta ganewa idonta. Asmau ta san bazata bar maganar ba dole ta fadawa Baba. Bayan fitar Umma tashi tayi ta dauko Al-Qur'ani tana karantawa. Neman sauki kawai take a zuciyarta da ke kitsa mata abubuwa da yawa. Adduarta bata wuce idan Jikamshi bazai aureta ba zata mayar da hankali ga karatu, idan kuma iyayenta sun zaba mata Qasim duk da a yanzu sun san bata son shi to bazata yi musu ba. Fatanta bai wuce ta sami juriya wurin karbar duk wata jarabawa da tazo mata ba. ***** Washegari Umma ta gama shirin zuwa gidan Mama suyi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103