Chapter 64
Chapter 64
'yan uwansa suka fuskanci yadda suke jifan juna da kallo. Ita duk kunya ma take ji musamman saboda su Hajiya da Mama. Amatullah ce ta kurawa Ismail ido tace "kai da Babana iyinku daya. Kaima sunanka Jikamshina?" saboda irin kamaninsa da Ishaq. Ya Salam, Asmau ji tayi kamar kasa ta tsage ta shige. Allah Ya taimaketa ma Amatullah bata ce irin yadda Ummia ke fada ba. Don kadan daga aikinta ne yin hakan.Col. Ishaq kansa yau yaji kunya karo na farko a rayuwarsa game da fadin magana a gaban kowaye batare da yaji komai ba. Su Musaddiq sai kallon kallon kallo ana dan murmushi. Ismail kuwa yace mata "nima babanki ne 'yan mata" ya karasa wurin gadon da murmushinsa. Ta kalli Col Ishaq tayi masa gwalo " Babana kaga nayi sabon baba ko. Ni yanzu na dena yin baba da kai" Yace "subhanallahi me nayiwa princess dina haka. Kai Ismail tashi ka bani wuri mu sasanta ni da 'yata" 'Yar dramarsu tasa mutanen dakin dariya. Amatullah tayi saurin rike hannun Ismail tace "yanzu baka wasa dani sosai sai da Ummi na. Nima ga sabon Baba nayi" Asmau ta rasa abin cewa. Tsiyar yaro mai surutu fa kenan. Yau Amatullah ta gama bata kunya. Safiyya tace "amma da baban nan naki da Ummi basu kyauta ba. Yanzu ga sabo nan mun baki. Amma kiyi hakuri Babanki so yake ku koma gidansa sai ku rinka wasan tare kullum shiyasa yake yi da Umminki" Kana gani kasan Amatullah taji dadin wannan zancen tace "Ummi kuje kuyi wasa da Babana to idan kun gama mu koma gidansa." Yau kam ta kai karshen jin kunya, shi kuma Col. Ishaq saboda shawarar da ya yanke ta rabuwa da ita shiyasa yau bai bada amsar da zata karasa bata kunya ba. Hajiya da Mama Yalwa sai sunkiyar da kai suke. Ita Mama harda mamakin dama son Asmau sojan nan yake bata sani ba. Ismail ji yayi ta shiga ransa. Dama yana son 'ya mace gashi duk maza gareshi. "Ki kyale wancan Baban kawai kinga a gidana zan siyo miki kayan wasa da alawa" Tace "ai Ummi ma tana siya min. Ta hanani kwadayi. Kuma bana yi sai tace min Allah Yayi miki albayka" Yarinya karama sai basu sha'awa take yi. Mami kallon Asmau take yi. Yanzu mace mai kamannin kamala irin haka ace a waje ta haihu. Kai wannan duniya mai rudin bayin Allah. Amatullah ta sake cewa "sabon Babana in kayanta maka Allahu?" Dahiru yace mata "karatu ake cewa ba kayatu ba" Tuni ta bata rai "kayatu fa nace ba kayatu ba" Daki ya kaure da dariya. Col. Ishaq yana kallon yadda 'yan uwansa duk suka mayar da hankali gareta. Murmushi yayi yana fatan ko nan gaba idan ya roki alfarmar a bari tazo gidansu ta yini wurin Hajiya bazasu yi mata gori ba. Ido suka hada da Asmau tayi murmushi sai taga ya dan sunkuya kamar zai duba waya. Bata kawo komai a ranta ba. Ismail ya samu shiga wurin Amatullah yace "karanta min a kunnena ni kadai kada su ji" Ta fito da ido da mamaki "Ummi fa tace mai yada mai yada dan wuta, mai ji mai ji kafiyi." Nan dariya aka yi suka ce to sai ya kiyaye yarinya tasan rada babu kyau. Daga kai yayi ya kalli Asmau ta danyi murmushin jin kunyarsa. Su Mami suma mamakinta suke yi. Ga dai ta yadda ta haifi 'yar nan amma ga dukkan alamu tana da tarbiya sosai. Tunda ta bude baki ta fara karanto sunayen Allah gudu biyar da tsallake. Musaddiq ji yayi inama 'yarsa ce. Ga muryarta akwai dadi tana yi kamar da addu'a "YA RAHMANU YA ALLAH-AMIN YA RAHIMU YA ALLAH-AMIN YA MALIKU YA ALLAH-AMIN...." Haka tayi ta yi har karshe. Mami ta y kurawa Asmau ido, yarinyar bata da makusa sai abinda tayi a baya. Idan har aurenta zai sa dan uwanta ya dawo mata kamar da, to zata amince da auren nan. Sai dai fa dole su shirya da jin surutu da gorin 'yan uwa da sauran mutane. Copied By HAYATU BABA ZUBAIRU (admin Arewa hausa novels Novels villa Duniyan novels Hayat hausa novels Hausa novels and fashion And Cool novel, makeup and cooking) WHATSAPP NO: +2347039625239 ABINDA AKE GUDU🙆🏽46 Batul Mamman💖 Surutun Amatullah ke tashi a dakin da masu biye mata. Tsakani da Allah ta shiga zuciyar Ismail. A ransa ji yake ina ma yarinyar nan ta cika 'ya kamar kowa. Ta tashi har karshen rayuwarta bazata taba jin wata magana mai muni game da haihuwarta ba. Col. Ishaq kuwa Asmau har ta gaji da kallon inda yake tsaye. Duk iya yinta ta kasa yin sa'ar kallonsa a daidai lokacin da yake kallonta. Shi kuma yana sane yake dauke kansa daga gareta idan yaga ta dago nata kan. Duk son da yake mata dole ya rabu da ita indai tsakaninsa da Allah yana son farincikinta. Duk wani tanadi da yake yi mata da Amatullah maganar Ismail ta rusa komai. Zaiyi kokarin taimakonta ta kowane fanni na rayuwa musamman karatu da tace tana son komawa. A shirye yake ya dauki nauyin hakan idan bazai kawo matsala tsakaninta da wanda ta aura ba. Ko kawai ya hada kudi ya bata a matsayin gudunmawar aure. Shi kadai yake ta tunaninsa har su Umma suka shigo ita da Anti Bintu da Shemau. Ba haka su Mami suka tsammaci ganin dangin Asmau ba. Gashi dai suna da rufin asiri sannan ga hadin kai. Wani abin mamaki wai harda babar wanda yayiwa Asmau ciki ake jinyar Amatullah. Mamakinsu bai karu ba sai da Alh Adamu ya shigo. Mutum mai fara'a jan mutane a jiki. Ya gaisa da kowa sannan ya zauna yana tsokanar Amatullah. Lokacin dakin ya cika sosai shiyasa Haj Lubabatu tace su tashi su tafi. Tun daga kan Mami har Musaddiq sun yaba da 'yan uwan Asmau. Kaddara kam babu inda bata giftawa. Kuma idan ta ratso kamata yayi dukkan musulmin kwarai ya karbeta hannu bibbiyu. Ashe ba daidai bane idan 'yar mutum tayi ciki ko zina a kyamaceta a koreta. Hakan ba komai zai kara musu ba sai bushewar zuciya idan basuyi sa'a kamar ta Asmau ba. Ba'ace a nuna musu sunfi kowa ba ko a shafe girman laifinsu a mayar dasu kamar komai bai faru ba. Amma a jasu a jiki ta hanyar nuna musu kuskurensu da wajibcin tuba da nesanta daga aikin dana sani. Asmau ta zama babban misali. Duk da iyayenta sun yafe mata kuma ta tuba amma fa har abada da gaban abada idan akwai baza'a taba mantawa ba. Ita da ta manta da haka a rayuwarta sai ranar da taji ance *shiga aljannah cikin aminci*. Ya Allah Kasa mu dace. Ita da Anti Bintu suka fito rakiya. Sai a lokacin suka hango Bilkisu da Yassar a wurin wani benci. Kusan kowa ya manta dasu ma. Duk abinda taji daga bakin iyayenta da kakarta ta tambayi Yassar ya tabbatar mata da haka ne. Bilkisu tayi kuka sosai taji tausayin Asmau. Ta fada masa shawarar da kawunta ya yanke na rabuwa da Asmau saboda matsalarsa. Nan fa hankalin Yassar ya tashi. Bai ga wanda ya dace da yayarsa ba kamar Col. Ishaq. Suna wannan tattaunawar ne suka hango fitowar su Ismail. Bilkisu ta rasa inda zata saka kanta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103