Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 43

Chapter 43

Abinda Ake Gudu Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

a gefe ya fita. Col. Ishaq yana zaune akan kujera yana yiwa Amatullah wasa da tambayar ya jikinta. Asmau duk ta takura ta rasa abin yi. "Ki zuba mata abinci mana idan ke baki jin yunwa." Wai mutumin nan ina ruwansa da ita ne. Me yasa ya kara dawowa ma. Ta danyi tsaki a hankali sannan ta hada abincin ta zauna a daya gefen zata bawa Amatullah ya miko mata hannu alamun ta bashi plate din. "Kema ki zuba kici". Gefe kawai ta ja tana kallon ikon Allah. A baki ya rinka ciyar da Amatullah tana ta yi masa surutu. Asmau tana satar kallonsa. "Abinci nace ki zuba ba kallona ba" Ya Salaam! Ba karamar kunya taji ba ta tashi da sauri ta zuba abincin ta dawo tana tsakura da cokali. Ya tashi saboda ya fuskanci kunyarsa take ji. "Safina bari na je naga likitan da ya dubaki na dawo" Fita yayi ko waige babu. Asmau ta tuttura abincin kada ya dawo ya sameta. ***** Tambayoyi ya yiwa likitan game da ciwon Amatullah. Da ya fito ya tsaya bata lokaci don ya bata damar gama cin abincin. Gara da Allah Yasa yayi tunanin kawo musu abincinsa da yake tafiya office dashi ba don haka ba don ganganci fita zata yi ta bar yarinya ita kadai a daki. Wasu na nema ido rufe ita ta samu bata rike da kyau ba. Kafin ya dawo ta gama ta dauke plates din ta dauraye a toilet. Ya shigo yayi mata alama da ta fito waje. Darajar girmansa da take gani da tsoronsa da take ji a yanzu yasa ta fita. Ta tsaya can gefe ta sunkuyar da kanta. "Da ban zo ba sai ki fita ki Safina ita kadai a daki? Kuma shine harda koya mata karya. Allah kadai Yasan me kike koya mata kafin yanzu" Taji haushin maganarsa ta dago kai zata yi masa rashin kunya "ina ruwanka da abinda nake koya mata". Yanayin kallon da yayi mata kadai yasa ta kawar da kanta gefe "Ni kike fadawa haka?" Da wadanda ke karkashinsa zasu ji abinda ta fada kila idan ta fara tsallen kwado sai kafarta ta kumbura. Lallai tana da tsaurin ido. idan kayan jikinsa basu yi mata kwarjini ba ai shekarun da yake jin zai bata shabiyar ko sama da haka ya isa yasa taji kunyar idonsa. Da yake rashin kunyar ba dabi'arta bace sai taji babu dadi "kayi hakuri wallahi nagode da taimakon da kuka yi min. Abinda kaji na fada mata ma don babu wanda zai zauna min da ita ne" "Its ok, zan aiko muku da abinci anjima saboda haka kada ki fita ki barta ita kadai." "Nagode" "Har yanzu baki kira kowa a gidanku ba?" "Uhmmm sun ce zasu zo anjima". "Maman Safina kin iya karya" ya fada yana shafa kansa. Asmau taji kamar ta nutse a wurin. Kai wannan mutumi da bin kwaf yake. "Ance gobe za'a sallameku. Na fadawa likitan kada yayi sallamar sai nazo" Ta dan bata rai "saboda me"? "Saboda na kamaki da kyau. Ina son sanin inda zaki kai min 'ya idan kin fita daga nan" Cikin dakin ya koma ya cewa Amatullah zai je office ya dawo. Har da kukanta ita zata bishi. Asmau ta kalleta bayan ya fita a ranta tace ki gama ganinsa da kyau kafin ki dena ganinsa. Da yamma Haj Lubabatu ta saje dawowa har take tambayar Asmau ina iyayenta. Tace mata yanzu suka tafi za'a kawo musu abincin dare. Hajiya tace "ai mun zama daya nasan zamu hadu ko ba yau ba". A zuciyarta tana kokonton ko da gaske sun zo. Babu wani alamar kayan dubiya ga akwatunansu Asmau a gefe wanda ya kamata ace an tafi dasu gida. Da Ishaq ya koma gida da daddare sai da ta fada masa. Yace shima yana son bincike ne a kanta ko don yarinyar da take tare da ita. ***** Sai wurin karfe tara na safe Col. Ishaq ya dawo washegari amma sau biyu yana aika musu da abinci har da kayan kwalama na yara. A lokacin aka basu takardar sallama da magani. Sauran kudin da ake binsu duk yaje ya biya mutumin da ya kawo musu abinci ya kinkimi akwatunanta. Asmau ta dakatar dashi yace Yallabai ne ya saka shi. Dauka kawai yayi zai fita Ishaq ya shigo yace ya wuce dasu gidan Hajiya zasu biyosu a baya. "Bangane ba" Asmau ta fada a tsorace. "Nima namu gidan zam wuce don Allah kace ya ajiye min kayana" "Kinga ki wuce muje akwai tambayoyin da nake so nayi miki daga nan nayi alkawari zan kaiki gidanku da kaina." "Ni bazan bika ba, haka kawai na sani ko....ko..." Yayi murmushi "karasa mana. Ko satar mutane nake yi. Nima tsoron da nake ji kenan ko sato Safina kika yi". Idonta har ya ciko da hawaye tace "wallahi 'yata ce, don Allah ka barmi mu tafi." Fita taga zaiyi daga dakin tace cikin kuka "zanyi maka ihun barawo" Col. Ishaq yayi dariya ya kalli Amatullah "Safina ina babanki?" Ta sake lafewa a jikinsa "ga ka" "To kinji, idan kina son 'yarki ki biyoni. Taimakonki nake son yi albarkacin wannan yarinyar" "Bana son taimakon ka bani 'yata...." tafiyarsa taga yayi dole tabi bayansa tana dan gudu gudu saboda yadda ya soma yi mata nisa. Gaban wata mota mai kyau suka tsaya baka ya bude gaba ya ajiye Amatullah wanda dadi ya isheta sannan ya zagaya ya zauna a wurin dreba. Babu yadda Asmau ta iya dole ta bude baya ta shiga. Suna hada ido ta mudubi ya kashe ido yana murmushi ita kuwa ta murguda masa baki. Shi da Amatullah suke ta hira tana bashi labarin gidansu Umma Zulaiha. Gidan Hajiya ya wuce dasu zuciyar Asmau tana ta daridari. Duk kunya ta dameta haka tabi bayansa suka shiga gidan. Haj Lubabatu ta tarbeta cikin fara'a aka kawo musu abinci. Col. Ishaq yace Bilkisu taje ta yiwa Amatullah wanka. Asmau tabi bayansu da ido yarinya sai murna takeyi ta sake dasu. Hannunsa ya dan kada a gabanta ta dawo daga tunanin da take yi. Yace "Malama Asmau ina ganin ya kamata ki sanar damu ko ke wace ce. Hajiya ma ta fahimci akwai abinda kike boyewa shiyasa na kawoki nan ki fada mana a gabanta." Asmau ta soma hawaye "naso ace yadda muka hadu cikin mutumci mun rabu a haka batare da na tonawa kaina asiri a duk inda na tsinci kaina ba" Hajiya tace "kada kiga kamar mun takuraki, rayuwar Safinatu muke dubawa shiyasa. Idan har baki da wurin zuwa ga yarinya mai lalura lallai kina bukatar taimako" "Ina da iyaye da 'yan uwa. Kuma a garin nan muke" Col Ishaq yace "to me ya rabaki da gida har kika kasa fada musu kuna asibiti"? Asmau tayi ajiyar zuciya sannan ta basu labarin rayuwarta. Tun Haj Lubabatu tana kada kai ha[truncated by WhatsApp] ABINDA AKE GUDU🙆🏽33 Batul Mamman💖 Gidan suna dai ya koma wurin zuwa kallon Asmau da 'yarta. Bayan anyi sallar la'asar ne ta tuna da Col. Ishaq da ya kawo su. Dafe kai tayi saboda tasan bata kyauta ba. Ganin su Umma yasa ta manta da kowa. Shema'u ta fadawa cewa dan matar da suka zo tare shi ya kawosu kuma yana waje. Haj Lubabatu tana jinsu sai dai

Table of Contents

Chapters

103 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});