Chapter 86
Chapter 86
ta jure ta kawar da kai ga dukkan maganar da zata ji musamman daga dangin miji. Haka Allah Ya kaddara mata dole ne kuma sai an sami masu yi mata wannan gorin. Hakuri, ladabi, biyayya, tsafta da iya girki kuma sai ta dage. Ishaq yayi mata karamci da yake sonta a haka ya aureta. Ta zage damtse ta kyautata masa. Kowa ya fadi nasa Asmau tayi kukanta son rai. Bayan ta fita daga dakin ba jimawa Zubaida tazo ta kirata dakin Yassar. Abin mamaki Uwargida ce a dakin Zubaida ta rufe kofar. Sake bawa Asmau hakuri tayi da taso bata mata rayuwa "idan naje muka gana da 'yan uwana zan koma Azare ne. Gidan nan ba zan barshi a cigaba da sabon Allah ba. Da kika ganni babana Limami ne. Da kuruciya muke sauka. Ina da ilimi na daidai gwargwado. Zanyi amfani dashi wurin bawa matan dake gidan shawara da koyar dasu sannan su koma gaban iyayensu. Ba ido gareni ba kada ayi abinda bazan gani ba. Za'a raya gidan da bautar Allah in sha Allah" Asmau taji dadi sosai haka ma Zubaida. Uwargida tace "Asmau ina so ku saurareni da kyau. Nasan sana'ata ba mai kyau bace kuma ina ta rokon Allah gafara. Amma ina son sanar daku wasu 'yan sirrikan rike miji da muke amfani dasu a da muna raba mata da mazansu muna aikata haram. Wannan abin idan kunyi a gidan miji riba zaku samu da lada. Ku zama marasa kunya amma ba tsiwa da fitsara ba. Duk abinda miji yake so kiyi masa kada yaje nema a waje. Wani kinkime jiki da hijabi a dakin miji sai a sallah ko kunyi baki. Ku zauna da kayan da zasu ganku da kyau suji suna sha'awarku." Zubaida da Asmau sai kunya aka fara sunkuyar da kai. Uwargida da taji sunyi shiru tace "kunga ni babarku ce. A bariki nayi amfani da wannan banga riba ba saboda aikin haramci ne. Amma ku gwada a gidan aure wallahi miji sai ya yaba muku. Da ajiye kunya mu kyautata musu muke raba auren soyayya. Matan hausawa kamar munfi kowa kunya. Muyi a waje sannan a gidan auren ma miji yana binki kina nokewa wai ke kin girma. Ai kullum ku nuna musu kamar yau kuka fara kasancewa tare. Sunayen soyayya na zamani samo ki kira abinki. Wani maigida ko baban wane an wuce wurin. Idan miji bai zo da kansa ba ke ki nemo shi. Hanyoyi gasu nan barkatai. Ku dan matso kada aji daga waje ace Uwargida zata bata ku. Allah Ya gani sharrin irinmu nake guje muku. " Ai kuwa su Asmau sunji batu a bakin Uwargida. To dama kunya a wurin irinsu sai a hankali. Baro zance kawai take Zubaida ta gama jin kunya. Ko da ta gama bayani sai dai su kalli juna suyi murmushi. ***** Wanka Asmau tayi saboda ance masu daukar amarya suna hanya. Amatullah kamar tasan ba da ita za'a tafi ba yau ta like mata. Da kyar da dabara Shemau ta hadata da yaranta tasa Yassar yayi saurin kai mata su gidanta. Nan da sati biyu sai a dawo da ita lokacin itama Asmau ta saba. Ana fita da ita kuwa Asmau tasa kuka. An rabata da Ama ji take gara kawai a bata ita su tafi tare. Da kyar tayi shiru ta shirya cikin wani material mara nauyi riga da skirt. Fuska tasha kwalliya sosai ga katon mayafi har ka ta lulluba. Jammu cikin kawayen Shemau ita ta matso kusa da Asmau ta damka mata wani abu kamar zuma kadan a kofi. Asmau ta dan dago kai ta kalleta. "Nasan kin sha abubuwa da yawa shiyasa na zuba miki kadan. Kinsan yadda muke da Shemau kanwa na daukeki. Na bata sauran za'a ajiye a gidanki." Wannan kayan idan batayi da gaske ba cikinta sai ya baci. Kowa da nasa kuma duk abu daya ne. Suna son daga darajarta a wurin miji. Kafa kai tayi ta shanye tsumin. Jammu tayi dan murmushin jindadi. Tasan nan gaba Asmau sai ta nemeta da kanta. Sirrinsu ne na Sokoto. ****** Dirar motoci aka ji wanda yayi daidai da faduwar gaban Asmau. Shikenan ta zama matar aure. Auren da ta fitar da rai ashe tana da rabonsa. Gashi zata bar Umma ta kama rayuwar ibada. Su Mami ne suka zo daukar amarya da wasu 'yan uwansu manya. Da aka tashi fita da kyar aka bambare Asmau daga jikin Umma, ita ma Umma kukan take. Su Anti Bintu ma da Mama Yalwa sunyi nasu kukan. Motoci sunfi goma daga bangaren ango banda na dangin amarya masu motar gida da ta haya. Mata ne kawai suka cika gidan. Biki yayi albarka. Mutan Jikamshi sun dauki amaryarsu Asmau. A motarsu daga wanda yake ja wani soja ne abokin aikin Col. Ishaq sai Walida a gaba. A baya kuma Yaya Abu ce da Mama Yalwa suka saka Asmau a tsakiya. Gida ne flat mai kyau tun daga waje ga filawoyi sun fito ta saman katanga. Gate din a bude yake da yake bazai dauki motoci sama da uku ba dole aka bar wurin da za'a shigo da motar amarya. Tun a nan zaka san anzo gidan amarya saboda kamshin dake tasowa daga ciki. Wannan aikin su Shemau, ne da Rashida, Sabira da Suwaiba. Mata sai son barka ake gida yayi kyau sosai. A cikin falon aka kai Asmau wurin wasu mata iyaye ga Col. Ishaq ta bangaren Hajiya da babansu. Anyi barkwanci suka kare da nasiha. Babu mai iya tanka Asmau domin sun sha gargadi a wajen iyaye maza. Col. Ishaq yana da kwarjini basa son bata masa, ihsani ya sami tangarda. Daga nan aka wuce da ita dakinta wanda Umma tayi namijin kokari wurin sayan kayan kawata shi. kanta a rufe yake tana hawaye har aka zaunar da ita a bakin gado. Wata da tace gidanta na jikin na Asmau mai suna Husna tazo ta dan bude fuskar amarya tana murmushi "Masha Allah amarya Allah Ya bada zaman lafiya. Idan kina da matsala ki rinka nemana. In kina so ma ni kullum sai na shigo na taimaka miki." Ainau dake gefe tayi dariya, Husna baki san wannan angon ba. Sai da aka hada da magiya aka samu matan suka fara fita. Gidan ba babba bane sosai. Daidai mata da miji da 'ya'yansu. Gida ya watse sai makusantan Asmau. Har lokacin bata bude fuskarta ba. Walida tace "kinga ki tashi kiyi sallar isha in da hali kiyi wanka ki canza kaya. Kinsan saboda mutane dakin yayi zafi gaki a kunshe cikin mayafi" "Nima abinda zan fada mata kenan. An taho da kayanki sai ki sami 'yar rigar bacci mai kyau ki saka" Asmau bata san lokacin da ta bude lullubin tana kallon Zulaiha ba harda harara. Dariya suke mata sosai Zulaiha tace "meye na hararata, ki tashi ko na tonaki wallahi" Zubaida tace "don Allah tona" sauran suka rinka naci ita kuma Zulaiha tana ta ja musu rai. Da yake yau bakin yayi lakwas Asmau bata ce komai ba ta shiga inda aka nuna mata bandakin dake cikin dakinta. Sai hamdala take, ko a toilet ba karamin kashe kudi aka yi ba. Duk kayan toilet Abdulhalim ne yayi mata su. Wanka tayi da alwala ta mayar da rigarta akan tawul din.
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103