Chapter 20
Chapter 20
na amfani Shu'aibu da Bara'atu sun saka. Kwanan amarya biyu su Bara'atu suka iso Kano. Kayansu ta kwatantawa masu mota aka kai hotoro ta wuce kofar mazugal. Makota ke sanar da ita su Hajjo sun tashi. Tayi mamaki sosai to ina suka koma? hotoro ta wuce da sa ran zata je gidan Lami a kwatanta mata inda suka koma. Suna isa gate din gidan Jafar ya fita ya budewa mijin Anti Bintu da ya tuko su a motar da yanzu ta zama ta Bara'atu ya shiga. Yaran Rabe su biyu ta gani suna wasa a waje ga Hajjo zaune karkashin bishiyar goba tana shan iska. A sanyaye Bara'atu ta karasa kirjinta na dukan uku uku. Hajjo ta washe baki tana yiwa jikokinta maraba. Bara'atu ta gaisheta tana kallon kofar gidan a bude. Hajjo tayi tsaki "ya naga duk jikinki yayi sanyi ne? Ki kwantar da hankalinki nayi tunanin bai kamata na matsa miki ki auri Rabe ba shine muka dawo gabadaya a taro a kula da marayu. Kuka ne ya tasowa Bara'atu sai dai kafin ya kai ga fitowa ta ga Sagira yar kanwar Hajjo ta fito Garzali yana binta a baya yana tsokanarta. Hajjo ta saki murmushi "ga amaryar Rabe fa shekaranjiya ta tare. Bari tazo ta nuna miki dakunanku ke da yara. Daki har biyu Rabe yace a baku. Su Jafaru dakinsu yana nan kusa da na kawunsu Garzali" Innalillahi wa inna ilaihi raji'un kawai Bara'atu ke fada saboda tsananin bacin ran da take ji a wannan lokacin. ABINDA AKE GUDU🙆🏽16 Batul Mamman💖 Wannan karshen satin tun alhamis Abubakar yazo. Kullum sai yaje wurin Asmau sunyi hirarsu yadda suka saba. Ranar asabar ya wuce Shanono wurin Qasim suka je daurin auren wani dan uwan Qasim din. Daga nan suka koma gidansu sai zuwa yamma yayi niyar komawa cikin Kano. Zaune suke a dakin Qasim suna kallon ball wayar abokin nasa tayi kara. Rage sautin TV din yayi ya amsa wayar. Ya dan jima suna hira d wadda Abubakar ya fuskanci mace ce sai daga baya yaji akalar hirar ta canja. Qasim yana tambayar yarinyar wane irin kaya ta saka. Murmushi yayi bayan ta bashi amsa "me kika saka a ciki?" "Ni kwance nake a daki da shorts(gajeren wando) ina shan iska ina tunaninki" (karya yakeyi. Kufta da wando ya saka). Irin wannan hirar ya kusa rabin awa suna yi da budurwarsa. Abubakar sai kada kai yake don takaicin wannan hali na Qasim. Yayi fadan da nasihar har ya gaji gashi ya kasa rabuwa dashi saboda shakuwarsu. In dai hirar banza ce a waya to Qasim ya ciri tuta. Sai ance ya fidda matar aure yace duk mata babu tagari. Mugun kallon da Abubakar yake jifansa dashi yasa ya katse wayar yana dariya. "Ya Ustaz irin wannan harara haka. Ni fa bance ka tsaya jin hirar ba duk ka wane hade rai." "Yanzu bazaka dena wannan muguwar dabi'ar ba? Ina jiye maka tsoron kada watarana kayi me gabadaya. Kasan zuciya bata da kashi". Kujerar kusa da Abubakar ya dawo ya zauna. "Kaima kasan duk abuna bazan yarda nayi lalata da 'yar mutane ba. Irin wannan hirar dai da dan abinda ba'a rasa ba shi muke yi don mu rage yawa. Sanin kanka ne yadda aure yayi tsada ni kuma ba wani abu na tara ba. To kuma ga abu mu muna so suma matan suna so. Sai a taimaki juna". Runtse ido Abubakar yayi "ji yadda kake cewa a taimaki juna kamar wani aikin kwarai. Kana dan malam har ka manta haramcin taba jikin macen da ba muharramarka ba? Ko ka manta inda Allah SWT Yake cewa : *WALA TAQRABUZ ZINA INNAHU KANA FAAHISHATAW WA SAA'A SABILA* (ISRA' 32) Ma'ana _KUMA KADA KU KUSANCI ZINA DOMIN ITA ALFASHA CE KUMA HANYAR BATA_ Taba jikin budurwa da niyar gusar da sha'awa batare da kunyi abin gabadaya ba yana cikin abinda Allah Yayi hani dashi. Kallo wannan da irin maganganun nan da kuke yi duk yana ciki. Wata rana sai kaga anyi abinda ake gudu azo ana cizon yatsa." Qasim yayi murmushi jikinsa ya danyi sanyi sai dai shaidan bai barshi ba. "Naji kuma duk nasani to amma ka manta cewa Allah SWT mai yawan gafara ne da jinkai? Idan mutum ya aikata irin haka tuba fa kawai zanyi a kankare min zunubin. Haba Abubakar kaima kasan yadda zuciya take. Ni a haka nasan ina kokari don ban taba ketawa kowace mace haddi ba. Za'ayi abin sama sama gayyar ta watse." Abubakar yace "Muna cikin wani zamani ne da hanyoyin gurbata tarbiya musamman masu nuni da zina suke da matukar yawa. Cartoon wannan sai kaga mage da bera suna kiss. Duk a haka ake lalata mana zukata. Na dade da sanin ina cikin maza masu karfin sha'awa shiyasa kaga na dage da yawan azumin litinin da alhamis. Idan naga abin zai dameni har sauran ranaku inayi. Manzon Allah SAW yace a lokacin da mutum yake zina fa babu imani a tare dashi. To me zaisa mu biyewa son zuciya haka kawai kana kan wata mace mala'ikan mutuwa ya ziyarce ka". Qasim ya dubi abokinsa. Tabbas Abubakar ba tun yau ba baya cikin maza masu kallon mata. Shiyasa ake masa kallon mai kunya sosai shi kuwa yana yi ne don ya kare zuciyarsa. "In Allah Yaso zanyi kokarin denawa sai dai fa abin sai a hankali. Bazan maka karya ba wallahi na saba sosai. Allah mun tuba." Da haka hirar ta kare bayan la'asar Abubakar ya koma gida. ***** Washegari lahadi Umma ta tafi da Aina'u yinin 'yar wata kawarta sai Asmau da Yassar a gida Abubakar ya kirata a waya zai zo suyi sallama don yau da wuri yake son tafiya. Sauri tayi ta karasa girki sannan tayi wanka ta canza kaya. Kwalliya tayi sosai irin yadda take karantawa 'yan matan littafi na yiwa samarinsu. Ta saka wata doguwar rigar atampa maimakon ta daura dankwali tasa hijab ko mayafi mai mutumci yadda ta saba sai ta dauko wani karami a kayan Aina'u ta yafa rabin kanta da yasha sabon kitso duk a bude ta gaba. Falo ta koma ta zauna sai taji kunyar ya ganta a haka. Ta tashi ta koma zata canza wata zuciyar tace tayi zamanta abinda sun kusa aure kuma dai haka ake yi yanzu don ita duk abinda ta karanta har ranta gani take yi daidai ne saboda a yadda ta dauki marubuta masu buga littafi da online komai suka rubuta basa kuskure. Sake shafa hoda tayi ta dawo falon. Tana zama Abubakar yayi sallama tare da neman izinin shigowa ta amsa masa. Gabansa ne ya fadi da yaga Asmau. Tayi kyau sosai gashi tana da 'yar kiba sai rigar ta kamata a kirji da kugunta. Ba wai bai taba ganin yanayin jikinta ba saboda yau da gobe yakan ganta babu mayafi amma sai bisa kuskure. Yau kuwa shigar ta tsaya masa a kokon rai har ya kasa dauke idonsa daga gareta. Murmushi tayi na nasara saboda yadda taga yanayinsa ya canza. Tunda ta fara karance karance da hirarsu da Walida taji ta matsu ko hannunta ne ya dan rike itama taji yadda ake ji. Wani juya ido tayi duk sauran kunyar suka bace "Mine ka zauna mana." Wani jan numfashi yayi "Asmy kinyi kyau" Tayi masa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103