Chapter 63
Chapter 63
Ishaq ya kara murmusawa "to ai babu damuwa Mami ga kannenki nan sai kibi daya daga cikinsu ki kwana a gidansa" Mami ta saki baki don batayi tunanin haka zai ce ba. Tayi zaton zaije ya bawa Hajiya hakuri. Duk sun san bacin ranta yafi karfi akan gorin haihuwar da aka yi masa ne. "saboda Allah ya zaayi naje gidan kannena na kwana da girmana" "To bari mu dawo daga masallaci sai na baki key din gidana. Babu datti sosai saboda karshen sati maigadi yana min shara. Sai ki tafi da taki 'yar Bilkisu ta tayaki kwana" yana gama magana yayi gaba kamar bashi ya fada ba. Sun san sun tabo soja yau sai yadda ta yiwu kuma. Bayan fitarsu masallaci Mami da Safiyya suka zauna suna ta magana akan lamarin auren Asmau da kuma karin laifin da Ismail ya janyo musu. Bilkisu dai shiryawa tayi a daki ta fito ta zauna jiran zuwa asibiti don tasan dole aje da ita tunda mai aikinsu bata nan. Tare suka dawo daga masallacin su Dahiru suna ta bashi hakuri ya nuna musu komai ya wuce. Wurin Hajiya ya je ta shirya ita ma tace motarsa zata shiga su tafi. Suka fito falo Bilkisu tabi bayansu suma sauran suka fito. Bilkisu na gaban motarsa Hajiya a baya Safiyya tazo ta kama daya kofar zata bude ya juyo ya watsa mata harara ba shiri ta saki kofar. "Ki koma kibi motar 'yan uwanki masu haihuwa. Ni Hajiya zan dauka da 'yata." Tayi saroro tana kallonsa. Dahiru da yaji ya dan matso wurin motar "Yaya don Allah kayi hakuri ka manta da zancen nan. Kuma ka yarda ta biku ko Mami ta shigo. Kaga sai ayi saving din mai mu tafi da mota biyu" Col. Ishaq ya wani kankance ido ya kalli Bilkisu "toshe kunnenki kinji mai gadon zinare" ta kuwa tura yatsu a kunne tare da sunkuyar da kanta. Hajiya tasan karshenta wata maganar mara dadi zai yabawa kaninsa tace "a gaban 'yarku zaku nuna min hali ko, kai kuma Dahiru kusan yadda zakuyi ku taho" Col. Ishaq ya mayar da kansa ciki albarkacin Hajiya suka ci. Dole mota biyu suka yi don daya zata matsesu saboda Dahiru da Safiyya duk akwai jiki. Yana soma tuki Hajiya tace "kai" "Naam" "Kayi hakuri da abinda suka yi maka don Allah kada kuyi min gaba. Aure kuma da kaina zan sami kakar Asmau muyi magana in sha Allahu. Tun farko na fada maka dole zaka fuskanci kalubale ta ko'ina saboda wannan abu fa ba wanda ake iya saurin kawar da kai bane a kansa. Ni dai ina sonta kuma na baka goyon baya ka nemi aurenta. Allah mai yawan gafara ne da jinkai. Idan bama iya kawar da kai ga kuskuren mutane to bamu san da wane laifi mu kuma Allah zai kamamu ba" Allah Sarki Hajuyarsa akwai zurfin tunani. "Hajiya nagode sosai amma ki bar maganar auren. Asmau bata cancanci ta kare rayuwarta bata haihuwa ba. Nima daga yanzu bana fatan kara neman aure. Mu bari kawai tabi shawarar iyayenta a zauna lafiya." Sosai Haj Lubabatu taji tausayin Ishaq. Duk sallah bata fasa yi masa adduar samun rabo saboda yadda yake son yara. Da suna kanana har goya masa kannensa tana yi saboda yadda yake mata nacin zaiyi raino. Sai ayi goyon ya zauna a falo ko baki tayi baya jin kunya. "Dole kayi aure shine cikar dan Adam. Kayi addua kamar yadda nake maka. Allah Ya kawo maka mace tagari" ya amsa da amin amma ba don yana tunanin zai kara son wata bayan Asmau ba. Shi fa bashi da raayin auren da babu soyayya. Kuma soyayyarsa ta kare a wurin Matar Jikamshi. Ya kai hannu kan giya zai canja yaji Bilkisu ta dora nata a saman nasa ta kankame. Ya dan kalleta ya kula kuka take yi a hankali. Yace "nine ko, nasa Maminki kuka" Muryarta na rawa tace "a'a Uncle don Allah kada kaki auren Ummin Amatullah" Murmushi kawai yayi yana kwanar shiga asibitin motar Musaddiq tana bayansa. "Allah Yayi miki albarka kinji. Ki cire duk abinda kika ji dazu daga ranki.... Wai ma wa ya koya miki labe? Bari mu dawo yau sai kinyi tsallen kwado" Da guntun hawayenta tayi murmushi. Hajiya ma murmushin tayi. Taji dadi da fushinsa bai shafi 'ya'ya ba. Boot dinsa ya bude ya fito da ledoji biyu cike da tarkacen kayan kwadayi na yara sai katon din ziza. Yana tasowa daga office ya siyo kafin ya wuce gida. Bilkisu tazo taya shi dauka sai ga su Ismail da sauri kowa ya dauki abu daya cikin su mazan. Ya kawar da kansa gefe don yasan suna neman shiri ne. Abinda bazasu samu kenan a nan kusa ba. ***** Shi da Hajiya ne a gaba sai Bilkisu da ta jero tare da Mami da Safiyya tana tambayar Mamin kannenta. Sun kusa zuwa dakin suka ga wata mace ta fito daga wani daki da hijab dinta har gwiwa tana kuka. Col. Ishaq bai san lokacin da ya isa gabanta ba da sauri ba hankali a tashe yace "Matar Jikamshi menene?" Asmau kuka take yi kawai "Amatullah ce ta sake samun attack. Likita zan kira" Shima a rude yake yace "koma wurinta bari na kira likitan" Kasa komawa dakin tayi tabi bayanshi da gudu tana ta zubar da hawaye. Duk sunji tausayin Asmau da yadda ta gigice. Dakin da suka ga ta fito Hajiya tace "mu shiga mu jirasu" Mami ta bude kofar suka shiga da sallama. Mama Yalwa ce a tsaye kan Amatullah tana ta kakari. Safiyya na jin yadda take kakarin ta matsa kusa da gadon da sauri tace "wannan ba attack din asthma bane. Ba kuji yadda take numfashin ba, majina ce a kirjinta" Mama Yalwa tana jin haka ta saka bakinta a hancin Amatullah ko kyama babu ta rinka zuke mata tana tofarwa. Tana kaunar Safina fiye da sauran jikokinta sosai saboda yarinya ce mai tattare da tabo mai muni a rayuwarta. Bayan zina mace aka fi gani da nason zunubin duk da cewa dole idan anyi akwai namijin da suka yi tare. To amma namijin sai ya tsira daga aibatawar mutane saboda shi ba'a ganewa a jikinsa. Idan ya karyata babu yadda za'ayi dashi. Sharrin zuciya ya cutar da Abubakar wanda yayi sanadin cutar da Asmau. Gashi a karshe Safina ita ce abin ya kare a kanta. Mama ta dan share hawayenta sai ga Amatullah ta ware saboda hancinta ya bude. Sai a lokacin suka gaisa dasu Haj Lubabatu. Mama tace "Hajiya duk wadannan yaranki ne? Masha Allah" Hajiya ta dan murmusa "ya mai jikin?" Mama tace " gata nan duk ta ruda mu." Ta kalli Safiyya "nagode miki kinji. Ya sunanki ne?" Safiyya ta fadi sunanta kenan su Asmau suka shigo tare da likita. Ga mamakinsu a zaune Amatullah take ta jingina da pillow. Asmau taji wani sanyi a ranta sannan ta matsa kusa da Amatullah tana mata sannu. Likitan ya dubata ya tabbatar harda mura tayi mata mugun kamu. Magunguna yace zai turo nurse ta kawo musu. Bayan fitar likitan Asmau ta gaishe da su Mami. Cikin su babu sa'anta duk sun girmeta. Sun amsa mata fuskokinsu babu yabo babu fallasa. Col. Ishaq yana tsaye daga wurin kofa. Idonsa kyam akan Asmau har
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103