Chapter 83
Chapter 83
din wanda ba'ayiwa shafi ba. Kowa sai cewa yake tafi jiya yin kyau. Komai da ta saka ya dace da kayan sai daukar ido take. Amatullah ma Najah sai da tayi mata kwalliya kada da ta dace da yara aka daukesu hoto da Umminta. Ana fara tafiya ango yazo daukar amaryarsa. Drebansa ke jan motar sai wani abokinsa a gaba. Ko kadan ba haka yaso ba amma wannan tsarin na Mami ne. Kasa dena kallon Asmau yayi tunda ta zauna. Itama yayi mata kyau sosai domin kuwa korayen kayan sojoji ne irin wanda suke sawa lokutan taro a jikinsa. Sai yau ta kara jin soja yayi. Fuskar nan tasa ya gyara saje ya kara haske da kyau. Ji yayi inama daga wurin dinner sai gidansu. Ya mika hannu mai sanye da farar safar hannu mai santsi zai riko nata da yasha lalle suka ji kukan Amatullah. Kuka harda ajiyar zuciya wai Umminta da Babanta zasu tafi su barta. Ana ta rarrashinta akan suma can zasu je yarinya taki amincewa. Col. Ishaq yace a miko masa ita. A tsakiyarsu ta zauna ta hana ruwa gudu don har suka isa wurin surutu kawai take yi. Gata a tsakiyar iyayenta duniya tayi mata dadi. Da suka je wurin ya fara cika. Duk masu cewa zasu sword crossing dinnan kowacce ta je. Gashi dai card admit ne amma haka wurin ya cika sai san barka. Iyaye ma ba'a barsu a baya ba. Hajjo da Yaya tagwai ma duk tsufansu sunce basu taba ganin bikin sojoji ba dole ne ayi dasu. Tare da sauran yara aka hada Amatullah sannan MC ya sanar kowa ya zauna ango da amarya zasu shigo. Yace a zauna ne saboda a tsaye dogaye zasu karewa marasa tsaho. Duk sojojin wurin cikin uniform din occassion suke. Dole su burge mutane. Sannan babu hargitsi don biki ne na manyan kasa da kowa baya son tsokano su. Layi ne sojoji suka yi hagu da dama mutum goma goma. Kowanne ya rike hularsa a hannu daya sannan suka hada takubbansu ta sama inda amarya da angi zasu wuce. Kida ne mai taushi yake tashi aka umarci amarya da ango da su taho su wuce. Babu masu daukar hoto ta waya don ance kowa ya zauna. Masu daukar hoto biyu ne kawai wadanda aka hayo su suke binsu. Sun zo inda zasu shiga karkashin takubban hularsa na makale a hannunsa ya lankwasa hannun damansa yayi mata alama da ta rike. Duk da tana jin kunya haka ta zura hannunta ta cikin nasa suka fara tafiya. Jama'a kuwa sai tafi har suka wuce suka zauna. Duk taron da akayi da tsari dole ya bada sha'awa. Irin wannan taron akayi a bikin Ishaq da Asmau. Tana daga mazauninta ta hango Qasim table dinsu daya da Ma'u suna ta hira. Ta nunawa Jikamshinta yayi murmushi "Allah Yasa shima tashi Asmaun mace ce tagari kamar tawa" "Amin" ta amsa tana 'yar dariya masu hoto suka sami na yi. Yaya Tagwai tace da Hajjo "wai ku a bikin Kano tsufaffi basa takawa ne? Tunda muka zo kidin yara ake sakawa suna ta rawa." Hajjo tayi dariya sosai sannan ta yafito Yassar da hannu tace aje a saka wakar da zasu iya takawa kuma a fada filin nasu ne tsufaffi. Ango da amarya dole su sauko. Yassar ya rinka dariya yaje ya fadi sako amma don shakiyanci wakar da yace a saka bata dace da Yaya Tagwai da Hajjo ba da sauran irinsu masu kashin kafa yayi laushi. Sai da suka fito tsakiyar fili ga ango da amarya kawai aka soma wakar Uban Duma ta Ali Dawayya. Hajjo ta karkace itama Yaya Tagwai ta gotar da kafa daya zasu fara taku suka ji sautin yafi karfinsu. Kunnen Yassar ta jawo yace "wallahi Hajjo tsohuwar waka nace ya saka kuma ita ya saka." 'Yan taro suna ta dariya Yaya Tagwai ta gwangwaje abinta. Ango ma sai gashi yana juyi da abokai. Asmau dai kunya ta hanata rawa sai dariyar tsufaffi dake cikinta. Iyaye ma sunyi tasu da amarya da ango asa ta turanci asa ta hausa. Da taro yazo karewa su Hajjo sunyi hanyar fita aka saka Mata ku dau turame. Dafa juna sukayi ita da Yaya Tagwai suka koma fili suka sha rawa. Su Ainau sun sha dariya kamar cikinsu zai kulle. Hajjo tace ita ba don amarya tayi ba. Dole ta taka idan aka ambaci sarki. Sai wuraren shadaya da rabi wurin yayi saukin mutane anata tafiya gida. Col. Ishaq ya dubi Asmau wadda duk ta gama gajiya. Ga tsinin takalmi. Drebansa yace ya bashi key din mota ya bi wasu ya tafi gida. Abokinsa da suka zo tare yana wurin yace "ango duk tsiyarka fa tare zamu tafi. Naga kana sallamar dreba nasan ni zan biyo baya. Kasan Mami...." "Mamo ba Mami ba. Ka fita idona Captain. Wai Baraka ba tazo ba. Don Allah ka dauketa ku tafi dare yayi" Saluting dinsa yayi yana kyakyata dariya. "Na barku lafiya angon Asmau." A can gefe daya kuma su Mami ke neman Bilkisu a tafi gida an rasa inda tayi. Tana can ita da Yassar a wurin wasu kujeru. Abinci yake ci yunwa ta dame shi yaji sallamarta. Har kusan kwarewa yayi don baiyi zaton ganinta ba. Tayi murmushi ta zauna a kujerar dake kallon tasa. Yassar ya ajiye cokalin yana kallonta. Tace "ci abincinka mana" "Bazan iya ba. Ni bana iya cin abinci a gaban mutane shiyasa ma kika ganni a nan yanzu" "Ni kuma kaga so nake kullum ka rinka ci a gabana" Sauran abincin bakinsa ne yasa shi kwarewar da yake gudu da yaji abinda tace. Tayi masa sannu amma tarin yaki tsayawa. Da tayi magana sai ya sake yin tari. Bilkisu ta dan harare shi "dama saboda ni kake tarin? To aiki ya sameka don bazan dena yi maka magana ba" Yassar ya rasa me zai ce mata. Haka yake da kunyar mata tuntuni. Babu wanda zaice ga budurwarsa. Ta dan sassauta kallonsa tace "ni na gaji da kallon kallo da muke yi fa, sai yaushe zaka ce kana sona?" Wannan karon da ya fara tari har sai da ya sauko daga kan kujera. Yana dafe da kirji tana yi masa sannu yace "ke haka danginku suke ne, basa jin kunyar magana" Turo masa baki tayi "to ba wani bane a cikin 'yan biki yace yana sona ba. Kuma har cewa yayi zaiyiwa Uncle magana shima soja ne a karkashinsa yake" Yassar ya ware ya koma ya zauna yana kallonta babu zancen wasa "don Allah kada ki amsa masa. Nima zanyi sojan nan har Yaya Ishaq ya karbo min takarda zanyi short service" "Uncle Ishaq nake ce masa fa" tana magana kamar zata yi masa kuka Duk ya rude da tayi zancen wani soja yace "to nima Uncle Ishaq kinji" Ta juya masa ido "to kana sona kenan na sallami wancan" Kai ya sunkuyar kasa da gaske kunyarta yake ji ya gyada kai a hankali. "Ni da baki zaka fada" "Kiyi hakuri zanyi miki text ko na kiraki" Shan kunu tayi "zan cewa wancan ya turo kawai" Yassar ya sake rudewa "me yayi zafi kiyi hakuri. Ina sonki mana ai ko ban fada ba kin sani" Sai yanzu yaga alamu taji kunya ta rufe kuskarta da mayafi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103