Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 19

Chapter 19

Abinda Ake Gudu Book 1 Complete Hausa Novel 1,196 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Allah Yayi masa rasuwa". Kuka Bara'atu ta saka har yaranta suka fito. Ganin Ummansu na kuka suma suka fara. Bare Shemau da Jafar masu wayo sosai. Cikin dan kankanin lokaci sauran abokan aikinsa suka zo. Bintu da mijinta ma duk sun zo da makotansu. Karfe uku suka kama hanyar Kano. Basu tsaya ko'ina ba sai kofar gidan Marigayi Mal Yahaya a unguwar kofar mazugal. Hajjo tayi kuka sosai na rasuwar danta sai fadin irin halinsa na hakuri da kawaici take yi. A nan aka yi masa sutura aka kaishi. Bara'atu duk ta rame a cikin 'yan kwanakin nan saboda tashin hankali. Saukinta daya shine canjin data gani a tattare da Hajjo. Mutuwar ta daketa sosai shiyasa duk tayi sanyi. Sabanin yadda ta saba yanzu tana jan su Shemau a jiki. A da kuwa sai dai tace su dena kallonta da kwala-kwalan idanunsu na mayu. Bayan sati biyu da rasuwar gabadaya 'ya'yan Hajjo suka taru da Kawun Bara'atu tare da wani malami da Rabe ya kira akan rabon gado. Kafin malamin ya fara jawabi Bara'atu ta sanar dasu cewa tana da ciki. Ran Rabe yayi matukar baci ita kuwa Hajjo abin yayi mata dadi. Dole aka hakura da rabon gado sai ta haihu. Da amincewar Hajjo ta koma Zaria saboda makarantar yara. Tausayin Bara'atu ne kawai ya kamata tun bayan rasuwar Shu'aibu. Bayan wata shida ta haifi 'yarta mace Hajjo da kanta ta zaba mata suna Aina'u. Yarinyar duk tafi sauran 'yan uwanta kama da mahaifinsu shiyasa ta shiga ran Hajjo sosai. Kano suka dawo lokacin kafin tayi arbain. Kwana goma da haihuwar Bara'atu Rabe ya sake dawowa da Malamin rabon gado. An gabatar masa da dukkan kadarar Shu'aibu wanda ya hada da motarsa guda daya da kuma makeken gida da ya gama ginawa a unguwar Hotoro sai 'yan kudade a banki da kuma wanda wurin aikinsu suka bawa iyalinsa sai kuma wata gona a Zaria. Malam ya gyara zama "Tunda mamacin yana da 'ya'ya da mata sannan mahaifiyarsa tana da rai duk 'yan uwansa basu da gadon shi." Rabe yaji kamar an kwada masa guduma "Malam ya zaka ce bamu da gado? Dukkanmu fa uwa da uba daya muke. Ni nan da kake gani shi ya saki nono na kama ko ba haka ba Hajjo?" Malam yayi murmushi "Alh Rabe ai shi rabon gado ba'a yi masa katsalandan. Allah SWT da Kansa Ya raba saboda haka babu wani son zuciya a nan. Zan nemi 'yan uwana malamai kamar mutum biyu sai muyi abinda ya dace. Allah Ya jikan Alh Shu'aibu". Malamin na fita Rabe ya soma fada ya dubi 'yan uwansa. Babu wanda yace masa komai. Dama Garzali karamin cikinsu baya shiga sabgarsu sosai shaye shayensa ne a gabansa. Yaya Abu da Lami ma basuyi magana ba ganin Hajjo tayi shiru. A haka taron ya watse Bara'atu na mamakin wannan hali na Rabe. Har daki Rabe yabi Hajjo tana daga kwance akan gado ta tashi zaune. Ya numfasa yace "Hajjo kina jin malamin nan. Yanzu banda sharri yace bamu da gado. Nufinsa wannan gidan da Yaya yake ta shirin komawa Bara'atu da 'ya'yanta ne kadai zasu tare?" Hajjo tace "banda abinka Rabe ai haka rabon gado yake. Da so kake ace kaima ka shiga gidan ko yaya? Dubi fa yadda ya sake gyara gidan nan. Ni bana son tashin hankali. Kada na sake jin zancen nan ya taso". Da haka ta kashe maganar. Kwanaki biyu a tsakani Malamin ya dawo aka zo akayi rabo daidai da sharia. Gida da mota duk sun fada rabon Bara'atu da 'ya'yanta. Gonar Zaria an sayar aka fitarwa Hajjo nata sauran duk na 'ya'yansa ne. Bakin cikin Rabe baya misaltuwa. Ya kwallafa rai sosai akan gidan. Bara'atu ta koma Zaria suka fara shirin dawowa Kano gabadaya. ***** Rabe zaune gaban wani malamin tsibbu ya gabatar masa da bukatarsa ta son a toshe bakin Hajjo duk abinda ya fada ta amince. Dariya Malamin yayi sannan ya karbi kudin aikinsa. "Indai wannan ne matsalarka an gama." ***** Bayan sati daya Hajjo ta zaunar da Rabe fuskarta cike da damuwa " idan baka fada min matsalarka ba wa kake dashi wanda ya fini?" Kansa a kasa yayi dan murmushin takaici "Hajjo ko na fada bazaki amince ba. Gani kike yi kamar cutar da iyalin dan uwana nake son yi". "Ko kadan Rabe, fada min abinda ke ranka". "Dama nayi tunani ne bai kamata na bar zuri'ar Yaya ta wulakanta ba. Kinga matarsa tana da sauran kuruciya. Idan tace zatayi aure waye muka sani da zai kula da ita da 'ya'yan da zuciya daya? Ni a tunanina ta bani su tunda mun rabo da Laraba sai na kara aure na rikesu gabadaya. Ko kuma....." "Ina jinka, ko kuma me?" Dan murmushi yayi mai nuna yana jin kunyar abinda zai fada "nace ko zaki yi mata magana ta amince na aureta. Kinga sai mu zauna tare gabadaya da yaran. Babu zancen a rabata da 'ya'yanta." Shiru Hajjo tayi yana tunani.."yanzu matar da ko wata uku batayi da haihuwa ba kana ganin ba'ayi wauta ba idan aka bijiro mata da zancen aure?" Dadi yaji batayi fada ba "nima ba wai yanzu yanzu zan ce ayi auren ba. Kawai dai tasan da maganar ne". Hajjo ta kada kai "shawararka tayi kyau , ranar asabar zata zo su fara kawo kayansu sai kayi mata magana a lokacin. Asabar da yamma Bara'atu na shayar da Aina'u a tsohon dakinsu Rabe ya shigo babu ko sallama. Da sauri taja rigarta ta suturta jikinta rai a bace. Wani kallon kasa kasa yake mata yana murmushi. "Mutum da kayansa meye kike wani rufe jiki"? Maganarsa ta bata mata rai tayi yunkurin tashi yace ta zauna magana zasuyi. Zama tayi a nan ya sanar da ita bukatarsa. Hade rai tayi tana kallonsa a wulakance. "Rabe bahaushe yace in maye ya manta uwar da bazata manta ba. Duk irin cin kashin da kukayi min a gidan nan don rashin kunya zaka ce kana son aurena. To ni ba shashasha bace, nasan sarai abinda kake nema a gareni. Gida ne ya tsokale maka ido kake son mu koma daga nan dani da yaran da abinda kake ganin sun samu mu koma mallakinka. To wallahi kayi kadan. Ko mazan duniya sun kare bazan aureka ba." Hajjo ta shigo tana kallon yadda Bara'atu take fadawa danta magana. Tuni ta rufe ido ta fara fada. " yanzu saboda yana son rufa miki asiri kike masa wannan rashin mutumcin? Idan har baki aure shi ba to ki sani dole ki bashi yaran nan." Fada sosai Hajjo tayi Bara'atu bata tanka ba. Washegari ta koma Zaria suka karasa hada kayansu wata mai zuwa zasu taho idan sun karbi takardun yara na makaranta. ***** A nasa bangaren Rabe yayi ta zuga Hajjo akan ta bari ba sai ya auri Bara'atu ba kawai ta amince ya zauna a gidan da nasa yaran sai ya hada duka ya kula dasu. Itama Hajjon ta zo a tare da ita tunda gidan akwai dakuna. Yaci galaba domin Hajjo ta amince. Sannan tace ya nemi mata yayi aure. Ita ya barwa zabi ta hadashi da 'yar kanwarta. Bayan sati uku aka daura aure amarya ta tare a sabon gida a Hotoro. Ba ayi mata kaya da yawa ba saboda kusan komai

Table of Contents

Chapters

103 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});