Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 98

Chapter 98

Rufaffen Sirri Book 1 Complete Hausa Novel 1,251 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

haka ba,Ashe duk kudin Nan da yake facaka dashi ba na Allah da Annabi bane,Ashe Kabiru kungiya ya shiga,tuni taji tausayin Sajeeda ya cike Mata zuciya,Ashe duk halin Nan da take ciki, Kabiru ne sila,ina ma tana da yadda zata tonawa Kabiru asiri,so take ta mik'e daga bayan motar ta hau danna ihu amma jikinta da zuciyarta sunki bata had'in Kai,tana ji tana gani zaa kaita Wai wani kungiya. Addua kawai take dan tasan Allah maji rokon bawansa ne Allah kadai ne zai tsallakar da ita. Tana Jin lokacin da suka iso ya kinkimeta daga bayan motar idonta a rufe yake, amma tana Jin lokacin da ya kwantar da ita Yana magana da wani,,addua kawai take a zuciyarta maganganun da taji suna yi akan Yesmeen ya matukar girgiza ta,ba iya fyade ma yake so yayi wa Yesmeen ba kasheta suke so suyi,mai Yesmeen ta musu da zafi haka, ko dai itama sirrinsa ta gano shi yasa suke so su kasheta,sai da taji maganar da suke ta gane Ashe Yesmeen ba makancewa tayi ba tana gani,ashe Yesmeen sirrin Kabiru tasani shi yasa tayi karyar makanta, haka ta kwanta Kamar mataciya har taji an taba kanta da Abu sau uku da kafin a tabata addua kawai take a ranta. Jin a watsa mata ruwa yasa ta ja dogon ajiyar zuciya ta dan bud'e idonta. Taji shugaban na yanzu ta samu tabin hankali suje su kaita wajen Tasha bazata tab'a iya tona musu asiri ba idan sun ajiyeta yaje yasan yadda zai nemi Yesmeen ya kawota su kasheta. Haka suka tayar da ita Suka jata mota,ta ringa yiwa Allah godiya da ba abinda ya sameta. Dan tasan ita dai a hayyacinta take,tana Jin yadda Kabiru ke tsalla gudu wai dan ya ajiyeta yaje wajen Yesmeen. Suna ajiyeta Suka ja motar aguje,sai da ta daina hango motarsu ta mik'e a hankali tana Jin jiri na daukarta,dan ji take kanta Kamar baa jikinta ba,bata san yadda akayi ta zub'e a kasa ba,sai muryar wasu maza taji a kanta rashin kwari da k'arfi ya hana ta motsawa,a haka suka kinkimeta sukayi chemist da ita,yadda bayan keyarta ya kumbure yasa suka dauka hatsari tayi ta buge a kai,tuni aka mata treatment wayanda suka kaita dayake masu mutuncine Suka biya kudin magani har abinci suka siya mata, da maltina tana ci kuwa ta dan ji kwari kwari,ta roke su akan tana so tayi sallah tafiya tayi gidan da tazo Bata same su ba ba Kuma Wanda tasani a garin,tuni mai chemist yace ta Shiga cikin gidansa dan chemist din nasa a jikin gidansa yake. Sai da ta rama duk sallolin dake kanta tana ta godewa Allah daya kareta daga sharrin Kabiru,ganin matar nada sakin fuska yasa ta nemi arzikin aron wayarta. Ta kuwa bata aron wayar ta saka lambar mijinta ta Masa flashing. Take kuwa ya kirata Yana Jin muryarta ya saki ajiyar zuciya yana "kin bi kin daga mana hankali Mai ya samu wayarki a kashe" Yaya Asmau kuwa tace Masa kalau take ta Yar da wayar ne ya taimaka ya saka mata kati ta layin nan yanzu ya Kuma turo Mata lambar Gwaggo,dan tasan idan har ta fada Masa abinda ke faruwa zai iya cewa zai taho a daren,ya Kuma dagawa kansa hankali,a yanzu fadawa Gwaggo halin da ake ciki kawai take so tayi,a samu aje a taimakawa Sajeeda da Yesmeen dan addua kawai take akan Allah ya Kare Yesmeen daga sharrin sa,sosai tausayin Yesmeen ke daiwaniya da ita,Ina ma tana da yadda zata je ta taimaka mata,duk tambaya da ya mata bata iya bashi amsa ba haka ya kashe wayar ya saka Mata katin dari biyar ya turo lambar Gwaggo ta layin Tana Kiran Gwaggo ta dauka tana Jin muryarta itama ta hau godewa Allah tana Mai ya samu wayarta Mai ya sameta? Yaya Asmau da ta fita can waje ta hau labartawa Gwaggo duk halin da ake ciki,ba abinda ta rage har yadda ya kaita kungiya dan ya haukatata, Gwaggo ihun sallati kawai take har sai da taji mahaifunsu Sajeeda ya karbi wayar shi ma ta labarta masa tana a taimaka a ceto Sajeeda daga hannunsa a taimaka a ceto Yesmeen. Hankalin Abban su Sajeeda a tashe ya hau cewa ta taimaka ta kirawa Kabiru Yan sanda Yaya Asmau kuwa tace bazai yu ba tunda Yana da kudi,zai iya Basu cin hanci,anan baban Sajeeda yace zaiyo shatar mota gobe da safe suzo shi da Gwaggo su dirar masa idan sun iso zasu kirata ta layin su hadu su je gidan. Da haka sukayi sallama washegari kuwa suna isowa Suka kamo hanyar gidan Kabiru kowane bakinsa d'auke da Addu'a Allah yasa Kabiru bai cutar da Sajeeda da Yesmeen ba, Gwaggo kuwa sai kuka take Kabiru Ihu ya fasa da "Shikenan asirina ya tonu" Yaja da baya jikinsa na wani irin rawa ya zubawa Asmau ido da take kallonsa. Yaya Asmau kuwa ta saki murmushi tana "Kana mamakin ganina ko?ka dauka na haukace ko ka dauka zaka cigaba da samun nassara a duk abinda ka saka a gabanka na zalinci ko? Kabiru da Allah na dogara ban hada bautarsa da kowa ba,shi yasa ya tsareni ya kareni daga mugun nufinka,Duk abinda kayi jiya Ina kallonka ba Suma nayi ba har kungiyar da ka kaini da kake tunanin an taba kaina saboda na samu tabin hankali Ina cikin hayyacina, Kabiru,na gano sirrinka a yau asirinka ya tonu,dan su Gwaggo ma sun san Kaine ka cutar da Sajeeda Kabiru da jikinsa ke balain rawa da kafafu zubewa yayi akan gwiwarsa ya sunkuyar da kansa Yana Jin Kamar numfashinsa ya d'auke saboda tashin hankali kukan Sajeeda kawai ke tashi da na Gwaggo da ta rungimeta,Sajeeda kuwa cewa take "Gwaggo mijina uban yayana shi ya nakastamin rayuwa saboda ya samu kudi, Gwaggo ko a mafarki ban taba tunanin Kabiru zai tab'a min haka ba,umma yayata da muke uwa daya uba daya wai ita take so ta kasheni saboda ta samu ta aure shi,Yaya Abu haka ta ringa saka min guba a abinci wai dan naci na mutu Allah na kareni,Yesmeen na kareni,a yanzu saboda san kudi ta sallamawa Kabiru kanta ya nemeta Wanda nasan dan biyan bukatarsa ya nemeta,mai na musu haka da na cancanci haka daga wajensu,cikin kuka Sajeeda ta hau labarta musu yadda Kabiru ya kwanta da Kare yazo ya kwanta da ita Wanda daga lokacin ta kwanta rashin lafiya,tana Basu labari tana kuka, Su Gwaggo kuwa Suka kaure da sallati, Kabiru kuwa da ke ji dama kasa ta bud'e ya shige ya Kara sunkuyar da kansa Yana Jin kirjinsa na bugu fiye da misali,mai ya rage masa Kuma Babu asirinsa ya riga da ya tonu fakar idonsu yayi,duk da ba riga a jikinsa yayi waje da balain gudu dan bazai iya kallon su ba,Yanzu dama duk tsawon lokacin nan Yesmeen ta fadawa Sajeeda sirrinsa Ashe duk tsawon lokacin nan Yesmeen ta San komai a kansa,Ashe lokacin da ya kwanta da Kare Yesmeen ta ganshi, motarsa ya fada ya samu wani riga a bayan motar ya saka ya tadda motarsa dan bai fiye zare mukullin mota ba a jiki yake bari. Jikinsa rawa kawai yake ya figi motar dan horn din fitar hankali ya ringa dannawa Mai gadi. Yana kallon lokacin da Yaya Asmau ta biyo shi a

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});