Chapter 100
Chapter 100
Ganin yarana a tare dani da suke murnar warkewa ta yafi komai faranta min,ni nasan karshen Kabiru yazo tunda asirinsa ya tonu,alkadarinsa ya karye tunda har muka warke nida Annur. Yanzu Kuma Yesmeen ce a Raina tunda Gwaggo tace bata je ba,Yaya Asmau itama sai maganarta take muna Kan hanya tana Kara daga min hankalin maganganun da taji Kabiru nayi da Yan kungiya a kanta,akan zasu kasheta Tuni na fara kuka wiwi dan zan iya d'aukar komai, matakin da zan dauka akan Kabiru na rabuwa ne,Zan rufe sirrinsa ga mutane saboda yarana bana so laifin mahaifin su ha shafe su,amma indai Kabiru ya tab'a Yesmeen wallahi sai Inda Karfina ya kare har kashe shi zan iya yi, Yesmeen bani na haifeta ba amma kaunar ta a zuciyata take,matsalar ba wani sanin wajen dangin mahaifinta tayi ba,gashi bata fadamin Inda zata gudu taje ba. Har muka iso Tasha Hankalina baa jikina yake ba, Mahaifina ya fara laluba Mana motar da zai Kai mu har can,muka samu waje muka zauna. Ina Jin Gwaggo da Yaya Asmau nata hirar Kabiru Nusrah na kuka,Hamza da Annur sunyi jingum jingum,amma ni zuciyata na wajen Yesmeen. Wani bakin mota ne ya shigo ya wuce ta gabanmu nabi motar da kallo,dan gaba da mu naga motar ta tsaya,Kamar wacce ake bawa umarni na zubawa motar ido, wani kyakyawan saurayi ya fara fitowa daga motar kafin a bud'e daya bangaren wata sanye da farin hijabi ta saka nikaf itama ta sauko daga motar, Haka kawai naji kirjina ya buga,sai na zubawa mai nikaf din ido, da ta bamu baya. Saurayin ya zagayo ta wajen da take tsaye ya hau magana Yana wuwurga hannu Yana nuna motocin,dake zube a Tasha. Ni dai ido na zuba musu bansan dalili ba naga saurayin ya nufi wajen da aka jera motocin katsina Dan akan motar na gane motar katsina ce dan an rubuta a jikin wani katako an dora akai. Mai niqaf din Kuma ta jinjina a jikin motar,ni kaina bansan Mai yasa na zuba Mata ido ba har saurayin ya dawo ya mata magana yayi gaba ta fara bin shi a baya a hankali kamar wacce bata so,har Suka isa wajen motar kallon su kawai nake saurayin kuwa sai magana yake Yana leka fuskarta,haka kawai nake hango Yesmeen a tare da mai niqaf din,irin tsayuwar Yesmeen da tsayinta,bansani ba ko dan Ina tunaninta yasa na fara hango yanayinta a wajen mai niqaf din,suna tsaye idona akanta,da alama a takure take dan saurayin ya dage sai zuba yake idan tayi hanyar motar sai ya sha gabanta sai mika Mata wayar hannun sa yake,nidai ido na zuba musu suna tsaye na Kuma kasa d'auke idona akansu har sai da babana ya dawo Yana mu tashi ga mota can,a hankali na mike Ina k'ok'arin d'auke kaina daga kansu naga ta daga niqaf din ta sama,naga Yesmeen dita ce idan har ba gizo idona ke min ba,Yaya Asmau ce a gefena hakane yasa na damko ta Ina "Yaya Asmau duba min can Kamar Yesmeen nake gani ko idona ne? Da sauri ta waiga sai ji nayi ta kwalla mata Kira da "Yesmeen"!!! Yesmeen ta juyo da sauri tare da kallon Inda taji sunanta. Tabbas Yesmeen ce ba gizo idona ke min ba,a daidai lokacin da ta kwaso da mugun gudu tana isowa gabanmu kamar wacce wuta ya jata ta daskare a tsaye tana kallona bakinta a bud'e. Ni kuwa hawayen farinciki ya hau wanke min fuska nima Ina kallonta, Kamar Mai koyon magana tace "Umma kece ko mafarki nake yi? "Nice Yesmeen ba mafarki kike ba" Wani Irin cafka ta kawomin ta rungumeni ta fashe da kuka tana "Umma Ashe akwai ranar da zan Kara Jin muryarki,umma ashe akwai ranar da zan ga kin tsaya akan kafafunki,dan Allah karku tasheni idan mafarki nake. Nima kankameta nayi cikin kuka Ina "Ba mafarki kike ba yesmeen Allah ya warkar dani,Allah yayi ikonsa akaina Allah ya amsa adduar da kike Dade kina min" Cikani naga tayi ta zub'e akasa tare da yin Sujadda sai kuka take tana "Alhamdulillah ya Allah Alhamdulillah Alhamdulillah Allah nagode maka" Sai da ta dade a haka daidai da mahaifina sai da idonsa ya ciko da kwalla, Tana dagowa tana "Umma a yanzu da Kika fara magana Zaki wankeni a wajen Nusrah,tace ni muguwa ce saboda ba ke Kika haifeni ba shiyasa naki fadawa kowa halin da kike ciki,umma ke zaki wankeni a wajensu" Har ga Allah ji nayi raina ya b'aci na kalli Nusrah dake zare ido na fara magana Ina "Au haka kikace dan bani na haifeta ba shi yasa bata fada muku ba, kunsan abinda Yesmeen tayi min kuwa?so kuke ta fada muku mahaifinku ya kasheta" "Umma dole naji haushinta kema kinsan yadda nake da ita,idan ta fadamin bazan nunawa Abba nasan komai ba iyakaci na Kira Gwaggo a waya na fada mata da kila baki dade haka ba umma ace duk tsawon lokacin nan Yesmeen tasan abinda ke faruwa sai ta ja bakinta tayi shiru umma dole naji haushinta" Ina k'ok'arin magana mahaifin mu ya dakatar dani Yana ya isa haka mu wuce ana jiranmu. Yesmeen kuwa tana ganowa Annur na magana ta Kara fasa ihu tana hamdala tama kasa tsayawa waje daya. Kuka hade da farinciki haka muka ringayi har Haka muka je Shiga mota Ina godewa Allah da ban wahala wajen Neman Yesmeen ba,ko Wanda ya kawota tashar bata kara kallon wajen da take tsaye ba har muka tafi. ta rik'e hannuna Tama kasa cikani sai tambayoyi take min akan ya akayi na warke?Ina Abba ya akayi su Gwaggo Suka zo? Ta hau bani labarin yadda ta fito taga su Kabiru da yadda ta gudu wasu bayin Allah suka taimaka Mata,ta kwana a yanzu ma dan mai gidan ne ya kawota tashan dan karya ta musu. Murmushi kawai nake dan da alama Yar tawa tayi saurayi Sosai nake k'ok'arin danne zuciyata dake san tuna min Yaya Abu da ta cutar da kanta akan kudin,da zaa mutu a bari a gidan duniya,yau akansa ta kassara rayuwarta,tsigar jikina sai tashi yake da na tuna irin wahalar da na Sha. KABIRU Yana fita daga gidan ya hau neman Rabiu a karamar wayarsa sai ihu yake Yana "Ka cuceni Rabiu ribar Mai na samu a Shiga kungiya,yau gashi asirina ya tonu,tun ban mori kudina ba,duk wahalar nan da na Sha ko shekara biyu banyi ba,Sajeeda ta gano sirrina,iyayenta sun gano sirrina yarana sun gano sirrina mai ya rage min kuma" Kuka kawai yake yana cigaba da Kiran Rabiu da bai San adadin miscal din da ya Masa ba. Yana k'ok'arin ajiye wayar yaji an dauki wayar hayaniyar da yake ji yasa ya kasa Jin Mai ake cewa ya kashe wayar ya sake Kiran wayar. A madadin yaji muryar Rabiu sai muryar wani yaji Yana "Mai wayar nan yanzu nan wani tirela ya murkushe motarsa ko shurawa baiyi ba,dan trilar ta tsatse shi" Wani irin ihu Kabiru ya saki tare da taka birki da k'arfi Yana "Rabiun ne ya mutu yanzu kana nufin ya rasu" Kashe wayar yayi ya fito daga motar a kidime kamar sabon mahaukaci haka ya ringa zunduma ihu dan ko a yau haka Suka ringa waya dashi,yana fada masa ya samo tsalalliyar yarinya zai je ya kwashe arzikin ta.
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111