Chapter 10
Chapter 10
*Page 5* Hankalin sa a tashe ya kashe kyandir din ya rarumo rigar sa ya saka hankalin sa idan yayi dubu ya tashi dan a sharadun da aka bashi har da Kar ya sake ya yarda a gan shi idan har aka gan shi da matsala. Tukunyar kasar ya d'auka yaje ya ajiye a d'akin da ya ajiye duka Abubuwan da aka bashi akan yayi amfani dasu,dan kafin su dawo gidan duk Suka kawo Abubuwan su musamman Suka ware d'akin ta bayan gidan. Yana rufo k'ofar d'akin. Ya nufo wajen window cikin sand'a addua kawai yake Allah yasa ba ganin sa Yesmeen tayi ba dan kamar daga dakin ta ya jiyo karar faduwar abu. Fuskar sa ya Kara a window ya hau lek'a d'akin sai dai ba abinda yake iya hango wa. Jiki a sanyaye ya koma ciki sai daya je har k'ofar d'akin Yesmeen ya Kara kunnensa yaji ko zai ji motsin ta sai dai har ya karaci tsayuwar sa bai ji motsin komai ba. Addua kawai yake Allah yasa ba ganin sa akayi ba dan yasan da matsala. Jiki ba kwari ya nufi d'akin su Yana tura k'ofar d'akin yaci Karo da Sajeeda tana ganin shi ta Kankame shi tana sauke numfashi. Ture ta yayi daga jikin sa dan yasan yanzu zata ce mafarki tayi Kara ruko shi tayi jikinta na rawa ta fara kuka tana "Abban Nusrah akwai matsala wanan mafarkin da nake ba haka kawai bane Mafarki iri daya sau uku Abban Nusrah wlh wanan abokin naka bana Jin mutumin arziki ne" Wani irin tsawa ya daka mata idon sa jawur dan yanzu sam ba'a hayyacin sa yake ba abinda aka ce yayi a yau har da wankan bai samu yayi ba fada ya rufeta dashi akan daga yau Kar ta Kara fada masa tayi mafarki ya gaji da halin ta idan ba za ta zauna dashi ta bar masa gida. Yaja dogon tsaki ya kwanta ya bar Sajeeda da jikin ta ke Karkarwa saboda tsoron mafarkin da tayi na yau ya da tayi ya munana dan har yanzu zafi take ji a gaban ta kamar a gaske,dan mafarki tayi abokin Abban Nusrah ya zura mata hannu a gabanta ya Ciro abu tana ta ihu, tsoro yasa ta kwanta a bayan Kabiru ta Kankame jikinta tare da rufe fuskarta. Allah yasan Kabiru fin karfin ta kawai yayi amma jikin ta na gaya Mata akwai wani abu game da Abokin nan nasa ba abanza take mafarki dashi ba daga ranar da ta fara zuwa gidan sa ta ga Yana ta kura Mata ido ya zama dole ta tashi tsaye da Addu'a. A haka tayi zuru har aka Kira sallah Asuba da yake tana fashin sallah sai ta Shiga bandaki ta gyara jikinta ta canja pad dinta ta saka Wanda ta cire a leda da zumar idan gari ya waye sai ta Kai bola dan haka take yi daga lokacin da take flushing din pad ya toshe pipe din ruwa ya daina tafiya ta daina sakawa a toilet. Ko da ta fito daga bandakin kwanciyarta tayi Dan tasan sai Abban Nusrah yaga gari ya kusa wayewa yake tafiya massallaci abin na matukar bata mamaki. Tana kwanciya bacci yayi awon gaba da ita dan baccin take ji. Duk abinda take yi Kabiru na sane rufe idonsa kawai yayi sai da ya tabbatar da tayi nisa a bacci ya mik'e ya Shiga bandakin ya d'auke pad din dan Yana ta addua ta cire dan zai Kai ayi amfani dashi Yana d'auka yayi waje da sauri dan so yake yaje ya samu Rabiu,suje yaji ya ko aikin da aka sa shi yayi. Yesmeen Rik'e numfashin ta kawai tayi da rarrafe ta kwanta ta Kankame jikinta dake ta karkarwa ba abinda take gani a idon ta sai Kabiru da ta hango Zigidir Yana zagaye wuta,gani take kamar a mafarki tana jin takun tafiyar sa har zuwa lokacin da taji karar bud'e k'ofar da yayi Wanda hakan ke alamunta Mata da shigowa yayi,Jin motsin sa a bakin k'ofar d'akinta yasa taji Kamar ta saki fitsari saboda tsananin tsoro,ita dai tasan ba tabin hankali ta samu ba Wanda take yiwa kallon mahaifinta taga yayi tsirara Yana zagaye wuta,mai hakan nufi?Mai yake yi da tsakar dare da kowa ke bacci,duk yadda ta so ta gano ma'anar abinda yake yi kwakwalwar ta tak'i bata had'in kai, dan a iya sanin ta a film take ganin irin wanan tashin hankalin ta Kuma san Abban ba boka bane ba maye bane. Baccin da bata koma kenan ba ta Kankame jikinta tana Addu'a a zuciyarta sai take ganin kamar ma dai idon ta ne ya gane mata Abba amma bashi bane. Umman ta zata fadawa taga Abba da tsakar dare tsirara ko Saifullahi Ko dai Aljani ne da siffar Abban,amma dai taji motsin shigowar sa cikin gidan. Haka ta kwanta bata motsa ba sai da aka Kira sallah Asuba ta mik'e ta daura alwala duk ba'a nutse tayi sallahr ba sabida tunanin abinda ta gani. KABIRU Yana fitowa daga gidan ya hango motar Alhaji Rabiu a nesa da gidan dan dama sun yi akan za su hadu da sassafe dan shi ma zai je can wajen shugaban nasu. Yana Shiga cikin motar Rabiu yace "dafatan ka yi abinda shugaba ya saka Kuma ba'a samu kuskure ba"? "Jiya na fara yi na ji Kamar motsi ina tsoron ace ganina aka yi ko wankan ban samu nayi ba" "Ya za'ayi a gan ka ba karfe biyun ka tashi ba"? "Karfe biyu na tashi wlh motsi naji Wai dole a gida zan yi Abubuwan nan ba zan iya yi a wani wajen ba"? "Aikuwa dole a gida zaka yi Kuma indai an gan ka wallahi da matsala ka samo jinin nata"? "Eee gashi nan a Aljihu na" "Tom bari mu karasa,tunda tak'i bamu hadin kai ayi ta baya kaga kuwa Dole a biyo mata ta bayan gida" "Kasan me ke damuna wai tana yawan mafarki dakai abin na damuna dan har ta fara nuna min Kamar kudin da kake bani bana halal bane tana da saurin gano abu fa Ina tsoro asirina ya tonu da Wanan mafarkin da take" "Ni mai hadina da ita da za ta yi mafarki dani ai da Kai ya Kamata tayi mafarki bani ba" A haka suka cigaba da hira har Suka karasa wajen. Ta baya Suka Shiga d'akin da shugaban nasu ke zaune kafin su karasa su zauna shugaban ya daka musu tsawa Yana "ku dakata!! Cak suka tsaya Cikin wani irin murya shugaban nasu ya taso da kana masa kallo daya sai gaban ka ya Fadi a d'akin da yake har da kwarangwal din kawunan mutane cikin wani irin murya yace "Rabiu abokin ka jiya ya bata min aiki dan ya bari an gan shi" Ido Kabiru ya zaro ba dama yayi sallati cikin tashin hankali yace "Shugaba waye ya gani" Akwai yarinyar da ta gan ka Kuma kasan ka'idan aikinmu indai wani ya ganmu sai mun d'au mataki dan bazamu so ta tonawa wani sirrin mu ba" Gaban Kabiru ne ya yanke ya Fadi dan Yana tsoron matakin da zaa d'auka akan Yesmeen dan ya gano itace ta gan shi dan ita kadai ce mace a gidan. "A cikin abu uku dole ayi daya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111