Chapter 102
Chapter 102
data haka ba,dan da ta sani da tuni ta nemawa kanta magani,tunda ni na gano amfani kayi dani dan biyan bukatar ka Saboda rashin tsoron Allah ka bani kudina na bar maka gidanan,wallahi da nasan amfani za kayi dani da ban dawo gidanan ba,na dauka Kai mutumin arziki ne" "Ke din ta arziki ce Abu?kina yayar matata kika sallama min kanki saboda kudi,kema ai ba matuniyar arziki bace tunda har Kika so ki kashe Sajeeda saboda ki Aureni,haka kawai Zan baki miliyan daya da rabi a cikin awa daya saboda jikinki na gwal ne? Abinda Kika nema Kika samu zan Baki sama da miliyan daya da rabi na Kara Miki miliyan daya kije ki dage da Neman maganin" Wani irin ihu Yaya Abu ta fasa tana "Allah ya Isa Kabiru Allah ya tsine maka albarka Allah ya tona maka asiri,yadda ka cutar dani,wallahi sai Allah ya wulakanta ka,ba iya ta gaba ka nemeni ba har ta baya saboda Kai mugu ne,wallahi sai na barbazaka a ko'ina sai na tona maka asiri na fadawa duniya kai dan mafiya ne ka bani kudin na bar maka gidanan" Kabiru kallonta kawai yake,zuciyarsa na raya Masa abubuwa da yawa,duk da asirinsa ya tonu,bazai so mutane su san halin da yake ciki ba,duk da yasan kila su Sajeeda na iya fadawa mutanen garinsu,sai Kuma yake Jin da wuya su tona Masa asiri ko dan yaran dake tsakanin su,idan har sunansa ya b'aci kamar sunan yayansa aka b'ata,yasan salihar zuciyar Sajeeda zata iya yafe Masa Koda bazata dawo gidansa ba. Tunanin da ya darsar Masa a zuciya yasa ya mik'e ya nuna Mata drawer akan ta kirga miliyan uku,ta fitar Masa a d'aki. Daga haka yayi waje ya barta duk da uban kaikaiyin da take ji,cikin murna ta nufi wajen drawer,dan da kudin nan zata nemawa kanta lafiya duk Inda ta bawa likitoci dubu dari biyar tsaf zasu wanke mata gabanta da bayanta sauran kudin Kuma ta siyi karamin gida tunda Babansu yace Kar ta taka taje gidan,gabanta faduwa yayi jikinta ya kwashi rawa a lokacin da taga bandir bandir din Dubu Dubu cike a cikin drawer,jiki na rawa ta cire zanin ta,dan da under wear a jikinta,ta hau zuba kudin a cikin zanin ta banda Kabiru zai gane da ta kwashe duk kudin,tasan bandir goma miliyan daya ne dan haka bazata tsaya daukar miliyan uku ba biyar zata dauka dan ba lailai ya gane ba, duk da Jan kyallen da ta gani daure a cikin Abu Mai gashi gashi akan kudin haka ta ringa zuba kudin a cikin zaninta tana murna. Kabiru Yana fita daga d'akin ya sauka kasa ya Kira shugaba a waya dan kila idan yayi wanan dabarar shugaba yace ba sai ya kai karya wajen mahaifiyar sa ya kwanta da ita ba. Shugaban na dagawa Kabiru yace "Shugaba zan iya kawo jinin wata ayi amfani dashi ba sai na nemi karyar nan ba Ina tsoron mahaifiyata ta gani,Ina tsoron asirina ya tonu,bansan dalilin daya sa ka dage sai dai na Kai karyar gidanta kafin na iya saduwa da ita,bani da saa a duk abinda akace nayi,bana san mahaifiyata tasan halin da na jefa kaina a ciki,ka taimaka na kawo jinin nan ba sai naje ba" "Idan ka kawo jinin a yanzu zaayi maka aiki da zaa rufe bakin matarka da duk Wanda Suka San sirrinka,amma dole ka Kai karyar nan can gidan mahaifiyar ka ka sadu da ita,idan kasan akwai jinin da zaka iya kawowa ka kawo Mana yanzu Nan" Kabiru gyada kansa yayi ya kashe wayarsa dan yasan Abu zata iya tona Masa asiri kamar yadda ta fada tunda sallamamiya ce gwara kawai ya bada jininta. Saman ya koma Yana tura k'ofar sukayi kicibis a bakin kofa ta rungume zaninta a hammatar ta. Kabiru ya saki murmushi Yana "Hajiya Abu wanan runguma da kikayi wa zani haka har nawa Kika dauka Haka" Yaya Abu hade rai tayi ta sake Kankame zanin a jikinta tana " ka bani hanya na wuce dan bazan kwana a gidanan ba" "Nima mukulli zan dauka na fita sai na rage Miki hanya "Ba sai ka rage min hanya ba cuta ce ka riga da ka cutar dani" Kabiru hanya ya baya ta fita daga d'akin da sauri,tana murna da bai karbe zanin ya duba kudin da ta kusan kwashe masa gabad'aya da tabbas kudin haram ne na jini,amma haka za tayi amfani dashi,d'akinta ta shige ta saka doguwar riga ya dan Debi Kaya kala biyu da duk a gidan Kabiru ta siye su,kaikaiyin da taji da danshin da taji a bayanta yasa ta shige bandaki ta hau wanke jikinta tana tsinewa Kabiru. Tana tsoron ta koma kamar Sajeeda babban burinta yanzu gari ya waye ta Kai kanta asibtin kudi,ta wangale musu su wanke Mata koina ta basu kudin. K'ofar da Kabiru ya turo yasa ta tsaya tana kallon shi ji take kamar taje ta rufe shi da duka. Kabiru kuwa yace mata zai fita Kuma kulle gidan zaiyi tazo suje ya sauketa a hanya ko hotel ne ta kwana. Yaya Abu Jakarta ta dauka tana zabga Mai harara,ta tusa daya hannnun nata a zaninta tana susa,dan.kaikai Kamar ta cire zanin ta ta Yar. Ahaka tabi bayansa ta Shiga motarsa yaja Suka tafi. Suna zuwa titi tace "Ka saukeni anan" Kabiru ko kallonta baiyi ba ya kulle k'ofar motar ya cigaba da tafiya Yaya Abu kuwa cikin masifa ta hau magana "baka ji Mai nace bane ka saukeni dalla ko baka jine"? "Hakuri zakiyi zan saukeki ni bansan Mai yasa kike Jin haushina ba,zan karbi kudi a wajen wani abokina Naga kin kwashe min kusan Rabin kudin nawa,idan na karba sai na Kara Miki sai na saukeki tunda kin dage" "Dole ai ka Kara min tunda kasan ka cuceni" Daga haka taja tsaki tana murnar yadda tayi kudi lokaci guda bata damu da kudin haram bane,tunda baa rubuta a jikin kudin ba,so take ta fara samawa kanta lafiya kafin ta san Mai za tayi da kudin, tana da yaqinin zata warke tunda zata Kai kanta asibiti da wuri. Kalle kalle take har Suka iso. Kabiru ya Shiga ciki Yana ta jira shi a mota yanzu zai fito. Da ido ta bishi har ya shige haka kawai taji gabanta ya yanke ya Fadi,ba dai kabiru kawota yayi ya yankata ba,sai a lokacin hankalin ta ya dawo jikinta dan kudin da ta gani ya rudata. Tuni taji hankalinta yayi mugun tashi dan sai a yanzu ta tuna ai Kamar bayan gari ya kawota Kuma gidan Kamar shi kadai ne ba wasu gidajen. Hankali a tashe ta hau k'ok'arin bud'e motar,a daidai lokacin da ta ga wasu sanye da Jan zani a kugu su biyu sun nufo wajen motar take,gefensu Kuma Kabiru ne ihu ta fara zunduma tana azo a taimaka Mata,a daidai lokacin da suka iso Kabiru ya bud'e motar masu sanye da Jan zanin Suka jawota suka daga ta sama,ta fara ihun "Kabiru mai nayi maka kake so ka kasheni innalillahi wa Inna ilaihi rajiun ku saukeni Kabiru idan dan ka bani kudinka kake so ka kasheni dan girman Allah ka dauki kudinka bana so Kabiru nice fa Abu mai na maka da zafi haka kake so ka kasheni? Ihu kawai take har suka direta a wani daki
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111