Chapter 109
Chapter 109
ki ba,in Sha Allah yadda Kika godewa Allah da wanan jarrabawa Zaki gode masa da k'ofar da zai bude miki,dama baya kaunarki dan da yana kaunarki bazai rabu dake akan laifin da ba ke Kika aikata ba,dan kila da bai sakeki ba haka zai addabi rayuwarki da gori har ki kasa samun kwanciyar hankali,Allah yasa hakan shi yafi Miki alkhairi" "Ameen umma wallahi banji komai ba dan dama na dade Ina ji a jikina zamu rabu din Allah ya bani wanda ya fishi" "Ameen "nace Ina Jin sanyi a zuciyata ban tab'a kawowa zata iya wanan dauriyar ba Saifullahi ya cigaba da musu nasiha da hakuri da irin kalubalen da zasu fuskanta a gaba,na tsangwama da gori daga mutane,Yana rokon su akan Kar su sake su damu,dan ba Wanda ya rubuta kaddarar sa da hannunsa ba Kuma abinda baya wucewa watarana zai wuce kamar baayi ba. Godiya na ringa yiwa Allah da ya bani Saifullahi da nake mamakin hankali da nutsuwar sa,yau gashi har dani yake yiwa nasiha a karshe ya gargadi kanennsa da kusantar haram,na dauka idan Yara suka fita waje lalacewa suke sai gashi nawa yaran Allah ya dafamin a tarbiyarsu a nutsen su suke ba mai yarda ma Nusrah ta girmeshi duk da shekarun da ta bashi daya da wata biyar ne. Allah ya bani yaron da ko faduwa nayi na mutu zai iya kula da kannensa,dan Allah ya Buda masa kwakwalwa baiwar zanen da yake dashi yasa kudade suke shigo masa. Tuni ya dauki nauyin gidan,Ya maida Yesmeen makaranta,ban taba binsu asibiti dubo mahaifinsu ba,dan duk sati haka suke zuwa asibti duba shi,a fadar su daure shi ma ake ya daina Haushin karen Yanzu Amma indai ya gansu haka zai zubo musu ido Yana kallonsu. Nidai ba abinda nake iya cewa Ina dai yi Masa addua a zuciyata, Yanzu na dan dawo da jikina Ina Shan magungunan da Saifullahi ke siyomin,matsalata daya har yanzu Ina fitar da ruwa mai doyi, watakila wanan shine kaddarata,bazan warke gabad'aya ba,taya ma Zan warke gabadaya an sadu da kare an zo an sadu dani,da wuya na warke. Alhamdulillah komai na dan tafiyar mana daidai,dan Nusrah itama ta koma makaranta da taimakon Saifullahi dan Saifullahi yasan manyan mutane,idan ta tafi makaranta sai ta barmin takwarata. Yesmeen kuwa tsallake aka mata dan tana da k'ok'ari sosai ban kawo tana zana jarrabawar gama secondary zata ci ba,sai gashi ta fito da sakamako mai kyau. A irin wanan lokacin gwaggo da Yaya Asmau Suka kawo.mana ziyara. Sunji dadin yadda suka ga nida yarana,duk da gori da tsangwama da muke fuskanta a wajen wayanda basu da ilimi hakan bai saka mun ki walwala ba. A Daren ranar kwana muka yi muna hira da Gwaggo muka yi ta zancen Yaya Abu da Gwaggo ke cikin damuwa saboda ita,dan tace ko bacci batayi tafiso tasan halin da take ciki saboda tasan irin addua da zata ringa yi mata hannun ka baya rubewa ka cire ka Yar. Har ga Allah nima kwana biyu tana raina, dan idan inaso na tunata sai na tuno halinta mai kyau dan bazai yu nace bata da hali Mai kyau ko guda daya bane. Ni na ringa kwantarwa da Gwaggo hankali Ina ta cigaba da Addu'a in Sha Allah zamu gano Inda take Addu'ar iyaye na tasiri akan yayansu. Yaya Asmau ce ma naga bata wani damu ba,wajen Sha biyu muna hira da ita nake fada mata yadda na ke neman maganin da zai warkar dani na daina zubar da ruwa mai doyi dan yanzu shi kadai ne matsalata. Tambayata tayi ko na gwada na gargajiya na girgiza Mata Kai sai tace mai zai hana na nemi maganin wata a katsina maganin ta nada kyau,tasan wacce itama ta ke fitar da ruwa mai wari a gabanta tana Shan maganinta ta warke ,jiki na rawa nace ta hadani da matar da tayi amfani da maganin ta na tambayeta naji,sai tace min bata da lambarta amma zata Kira wata ta turo mata lambarta,sosai naji sanyi a zuciyata dan zanji dadi yau na wayi gari ruwan nan ya daina fita a gabana. Kwana biyu kawai Suka yi da suka zo tafiya ta bani lambar matar da tayi amfani da maganin. Koda na kirata ban samu ta dauka ba sai da yamma ta biyo Kiran Muka gaisa da ita na fada mata yadda akayi na samu lambarta da taimakon da nake so tamin,cemin tayi Kar na damu yanzu nan zata turo min lambarta matar a katsina take maman mujahid maganinta na da balain kyau ko da baka discharge maganinta na fitar da dattin Mara 08162859027 bari ta Tiromin lambarta na kirata na Mata bayani. Godiya nayi Mata Ina kashe wayar sai gashi ta Tiromin lambarta 08162859027. Duk da munyi waya da ita ta bani tabbacin zan warke idan har na Sha maganin ban yarda ba Zan dai gwada naga ko zan dace. Sai da Saifullahi ya dawo ya tura mata kudin,yace min akwai abokinsa zai taho daga katsina zai taho min dashi ya hau bani labarin yaje wajen Babansu ya dubo shi a asibiti da alama yana dan samun sauki,dan sai kallonsa yake Kamar ya gane shi,ce masa nayi Allah toh ya bashi lafiya dan zanso ya samu lafiyar ya gyara lahirarsa daya bata, zanso ya samu lafiya ya gyara kura kuransa,a yanzu babban burina naga Yaya Abu nasan tana cikin mawuyancin hali dan ba dama na kwanta sai nayi mafarki da ita,kwana biyu a tsakani Saifullahi ya zo da dalaleliyar motar da aka masa kyautarsa a wani company kera motocin da ya musu zanen da suka yaba duk da sun biya shi kudinsa sai da suka hada da masa kyauta,banda Ina ganin labarai nasan Saifullahi da guminsa yake samun kudi,da tuni na tsorata dan har ga Allah ba abinda ke bani tsoro sama da kudi,nafisan rayuwa rufin asiri,amma Allah ya kaddara Saifullahi Yana da rabon arziki Wanda da babansa baiyi gaggawa ba da a yanzu tare zamu ci arzikinsa cikin rufin asiri,kwana uku nayi Ina Shan maganin da na siya a wajen maman mujahid na fara ganin canji a jikina,dan ruwan ya rage zubo min na Kuma ji dadi sosai,dan har kudi na sake tura mata akan a Karo min jarka biyu. Ina zaune a palo Ina duba wani littafin addu'oi da Yesmeen ta mallaka naji dirin motar Saifullahi dan Yana cigaba da makaranta anan buk dan har ya kusa kamallawa,su Annur kuwa suna level one tare da Yesmeen dan ban da Yesmeen ta bar zuwa makaranta da yanzu tana level 3,Yana shigowa ya zauna sai da ya gaisheni ya hau cemin gobe zai tafi Abuja akwai aikin da zaije yayi jibi zai dawo na Masa addua. Murmushi na saki Ina sai dai na Kara Masa addua Amma kullum a cikin adduata suke bakina bai tab'a yankewa da musu Addu'a gabad'aya ba,a yanzu sai naji banida burin da ya wuce naga ma Saifullahi yayi aure dan ba Mai kallonsa ya dauka bai Kai talatin ba, saboda yadda ya girma, duk wani rufin asiri Allah ya mishi dan har gini yake Mana, wani mallamin su Nusrah ya makale mata akan Yana santa kamar yadda wani Saeed ya makalewa Yesmeen Yana kaunarta Saeed shine Wanda mahaifinta ya taimakawa yesmeen a lokacin da ta gudu,har nan yake biyota Amma
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111