Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 92

Chapter 92

Rufaffen Sirri Book 1 Complete Hausa Novel 1,229 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

sai ka rantse min ba wallahi ko duk duniya zasu taru su ce kudinka ba na halal bane sai Inda karfina ya kare wajen Kare maka mutuncinka ni nasan ba yadda zaka tab'a haka,shi yasa na cewa Nusrah Kar ta sake ta fadawa kowa wanan maganar abinda za'ayi yanzu zan koma na Kara kwantar mata da hankali gobe da sassafe zan dawo kawai na cigaba da kula da Sajeeda dazu Gwaggo ta kirani Wai Asmau tazo Abuja wai har yanzu bata iso ba"? "Banganta ba da yake kinsan na fita da na dawo Kuma banganta ba yanzu ma Tasha zanje na dubata,gashi Yesmeen yanzu ta kara kunna min wani wutan" "Karka damu fa wallahi yanzu nan zan tsara Nusrah na gwada mata sharrin Yesmeen ta maka dan ta maka sata ka Kamata shine ta zuba maka wanan sharrin" "Ki taimaka min Yaya Abu ki koma Kar Nusrah ta sake Kiran wani ta fada Masa kinsan Yara ne su zasu iya yarda" "Ba matsala in Sha Allah ka taimaka ka Nemo Mana yarinya nan nasan tana cikin Abuja ba inda ta sani ba Kuma tasan hanya ba ka nemota ka daure Mana ita" "Zan nemota Yaya Abu ngd da Kika yarda dani, zan miki gaggarumin kyauta in Sha Allah da wata ce ba lailai ta yarda dani ba" "Kai haba wallahi na yarda da Kai karka damu bari na koma gidan,yanzu dai dole na taho gobe tunda akwai su larai a gidan,sai su cigaba da kula da Nusrah idan anyi suna sai su dawo gabad'aya" "Toh Yaya Abu ngd dan Allah duk yadda kika yi da Nusrah sai ki kirani ki fada min" Daga haka Kabiru ya kashe wayar ya dora kansa akan steering Yana "Rabiu ban Shiga kungiyar nan a saa ba,tunda na Shiga nake cikin tashin hankali yanzu idan Nusrah ta kira wani fa ta fada masa"? Kaja motar nan mu tafi wajen shugaba ya mana aikin da zaa rufe bakin yesmeen din a rufe bakin koma waye,duk matsalar nan Kai ka jefa kanka a ciki,da ka yarda ka bada wadatacen jini da yanzu duk baka tsinci kanka a wanan halin ba har yaushe ka Shiga kungiya da zaka fara nadama,kasan Allah ka bada jinin wanan matar ka huta yanzu shugaba duk zai kau ma da matsalar ka,Kai wallahi ko da duk duniya sun gano abinda kake ciki,zai maka aikin da zaa rufe bakin kowa,yanzu amfanin mai take maka ka bada jininta idan an kwana biyu sai ka samo matashiya ka aura,idan ka kwashe arzikin ta sai ka saketa ka Kara auren wata kamar dai yadda nake yi" " Bazan iya ba Rabiu wallahi bazan iya kashe Sajeeda ba,ko amfani da nayi da ita wallahi ba'a san raina bane Amma muje ya dubo min inda yarinya nan ta Shiga wallahi ita zan bayar idan ma da kaina yake so nayi ferfesun ta yi zanyi,Sajeeda ma ba sai na kaita can ba tunda ba magana take ba ko Yesmeen ta fada mata ba bakin da zata fadawa kowa, asibti zamu fara kaita inyaso idan an fara dubata sai mu wuce wajen shugaban" Kabiru kenan da barin ta da kayi a raye tana Shan wanan wahalar ba gwara kawai ka karasata ba" "Bazan iya ba Rabiu Kai karasa Ateeka kayi ba adaki ka killace ta ba mai ya hana kai ka karasata ko ba amfanin da take min inaso na ganta a raye" Daga haka Kabiru ya tada motar a madadin yayi hanyar wajen shugaban ya d'auki hanyar asibiti,dan tsoro ma yake ji shugaba yaga Sajeeda yace ya kawo jininta, yafi so ya bada jinin Yesmeen. Nusrah Tunda Yaya Abu ta fita ta kwanta tana ta kuka,sai a yanzu komai ya ringa dawo mata,dan yadda Kabiru yayi arzikin dare daya dole a dasa Masa ayar tambaya,sai a yanzu ta tuna kalmar Sajeeda da tace mata "Nusrah Abban ku ya kasheni" Ashe maganar da take so tayi mata kenan inama ma ta matsa mata a lokacin ta fada Mata,dama duk tsawon lokacin nan Yesmeen tasan irin wanan maganar amma ta boye mata,ko dan Sajeeda ba mahaifiyar ta bace shi yasa taki fadawa kowa Kabiru ya cigaba cutar musu da uwa, Mik'ewa tayi Kamar an tsikareta ta d'auko wayarta da taji Yana ta ringing ganin lambar da Yesmeen ta kirata dashi ne yasa ta dauka cikin ihun kuka ta fara magana tana "Allah ya isa tsakanin mu dake Yesmeen,duk tsawon lokacin nan kinsan dama abinda yake damun Umma baki tab'a fadawa kowa ba,ko bazaki fada wa kowa ba ai ya Kamata ki fadamin ko dan umma ba mahaifiyar ki bace, shi yasa Kika barta duk tsawon lokacin nan a kwance Muka rasa sanin wane irin cuta ne yake damunta, tun kafin ku bar garin nan Yesmeen kinsan Abba ya cutar da umma a madadin ki fada da wuri,mu ceto umma amma kikayi shiru Yesmeen wallahi idan Abba ya Kara cutar da Umma bazan tab'a yafe Miki ba wallahi kinfi abba mugunta har kuka koma Abuja su Saifullahi sun dade kafin su tafi baki fada musu ba yesmeen kece ma kika kashe umma ba Abba ba,kina tunanin da ace yau mahaifiyar ki na raye naga abinda zai cutar da ita bazan taimaka Mata ta hanyar fadawa mutane su Kai Mata agaji ba" "Ya isa haka Nusrah ki barni nayi miki magana Mana ki saurareni mana, Abba ya wuce duk Inda kike tunani yanzu ba lokacin da zaki Tsaya ganin laifina bane,ki kirawo Gwaggo ki fada mata halin da ake ciki,mama bakinta daya da Abba wallahi itama so take ta kashe umma sau uku tana gwada saka wa umma guba a abinci,idan kika fada Mata wallahi ba abinda zatayi akai kiyi sauri ki kira Gwaggo Nusrah" "Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun Yesmeen Allah ya tsine Miki albarka duk kinsan wanan masifar baki fadamin ba sai da na tura mama wajen Umma idan har wani abu ya samu umma wallahi bazan yafe miki ba muguwa azzaluma" Nusrah da jikinta ke balain rawa ta kashe wayar tana jin numfashinta na neman d'aukewa. Hannunta rawa kawai yake ta nemo lambar Saifullahi na waje da yake yawan kiranta dashi,sai da ta Masa miscall uku a na hudu ya dauka,tana Jin muryarsa ta saka ihu tana "Saifullahi Abba ya kashe umma, Ashe Abba kudinsa bana halal bane ashe Abba shine silar jefa umma a halin da take ciki" "Bangane ba Aunty Nusrah mai ke faruwa ne kimin bayani yadda Zan gane" Nusrah labarin da Yesmeen ta bata duk ta kwashe ta fada masa ta Kara da "wanan wane irin balai ne, akan kudi Abba ya kassara rayuwar Umma,ga itama yayarta itama farautar ranta take mai umma ta musu da zafi haka Yesmeen ta cucemu wallahi idan har mama ko Abba Suka cutar da ita bazan tab'a yafe Mata ba Saifullahi yanzu mai abin yi banida lafiya ya za'ayi mu ceto umma bana so mijina yasan halin da ake ciki" "Zan kiraki yanzu Ina zuwa" Kiit taji Saifullahi ya kashe wayar a daidai lokacin da Yaya Abu ta turo k'ofar ta shigo ta zuba mata ido tana kallonta ta kasa yarda wai yayar mahaifiyar ta ke san kashe ta" Yaya Abu kuwa jakar hannunta ta fara k'ok'arin ajiyewa tana "Nusrah wai kuka kike har yanzu ki daina kuka haka wallahi karyar

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});