Chapter 8
Chapter 8
Nusrah ya shigo da Jan zani daure a kugun sa hannun sa rik'e da tukunyar kasa,sai na Mik'e da sauri cikin tsananin tsoro na fara kwallawa Abban Nusrah Kira akan ya tashi,dan ba iya abokin nasa ne ya shigo ba har da wasu a bayan sa suma da tukunyar kasa a hannun su,ihu nake iya karfina na kasa d'auke idona daga kansu na Kai hannu na dan na tashi Abban Nusrah sai na ji baya gefe na har suka zagaye gadon da na ke kwance na cigaba da ihu Abokin Abban Nusrah ya fusgoni da k'arfi ya Kai hannun sa wajen zani na, na saka ihu!" A daidai lokacin da naji an rik'e ni ana girgiza ni na bud'e ido na da sauri tare da mik'ewa zaune kirjina na dukan uku uku a lokacin da na farka na ga ashe mafarki nake duk na jike da gumi,na Kankame Abban Nusrah da ya rik'e ni gam yana "lafiyarki kuwa"? "Mafarki nayi Abban Nusrah innalillahi wa Inna ilaihi rajiun innalillahi wa Inna ilaihi rajiun" Na cigaba da sallati Ina kallon k'ofar dakin mu dake rufe dan sai nake ganin kamar ba mafarki nake ba "Kiyi Addu'a ki koma ki kwanta" "Abban Nusrah mafarkin abokin ka nayi" "Gwara da ki ka ce mafarki ba gaske ba ki koma bacci dan Allah" Ya fara k'ok'arin cire ni daga jikin sa na Kara Kankame shi mu ka kwanta ahaka. Mafarkin da nayi na nan daram a idona,ko kad'an ban runtsa ba dan gani nake ko Yaya na rufe ido zan ga sun shigo bansan Mai yasa nayi mafarki da abokin Abban Nusrah ba,Mai ma'anar wanan mafarkin da nayi. Idona biyu har aka Kira sallah Asuba na tashi na daura alwala Abban Nusrah kuwa sai sakin munshari yake,a yanzu baya sallah akan lokaci sai nayi ta tashin sa kafin ya tafi massallaci. Duk tashin da na masa bai tashi ba da na dame shi ma tsawa ya daka min hakane yasa na rabu dashi nayi Sallah ta ina ta mamakin canjin da nake gani a tare dashi,sai Kuma na tuna wai abokinsa yace zamu bar gidanan take naji wani irin tsoro da fargaba ya rufeni da na tuna mafarkin da nayi dashi,jikina na gaya min mutumin nan baa a banza zai taimake mu ba bansan mai yasa jinina bai d'auke shi ba ko dan na saka shi a raina shi ya sa nayi irin wanan mafarkin dashi. Har na fito Muka hada abincin karyawa da Yesmeen zuciyata cike take da tunani har sai da Yesmeen tayi ta tambaya ta mai ke damuna nace mata ba komai. Karfe tara da rabi su Saifullahi suka shigo dan su karya fuskar su a washe,Annur kuwa ya zauna a gefe na bayan duk sun gaisheni yace "Umma nifa yanzu kullum sai nayi mafarki Abba yayi kudi" Da sauri na daga masa hannu Ina "ka ringa mana Addu'ar idan alheri ne kudin Allah ya tabbatar mana" "Ai yama tabbatar in Sha Allah yaro babban ka ya zama Mai kudi,Umman ka ke so mu cigaba da zama a talauce ba cigaba" Naji maganar Abban Nusrah a baya na na waiga Ina kallon sa a daidai lokacin da ya iso gefena ya zauna fuskar sa d'auke da murmushi Yana amsa gaisuwar da suke Masa. Ya janyo faranti ya fara zuba dankali yana cigaba da magana "Saifullahi Kai da Faisal yanzu idan muka gama karyawa zamu je ku rakani gidan da abokina ya bar min kyauta nasan zaku ga kwana biyu na dan samu kudi,wani aminina ne tun muna primary Allah ya hada ni dashi Mai kudine sosai hakane yasa yace zai taimaka min yanzu haka jiya nida mahaifiyar ku mun je jiya ta masa godiya ba iya kyautar gida kawai yace zai min ba har aiki zai bani a companyn sa zaa ringa biyana miliyan daya duk wata" Ihu Suka saka gabad'aya suka hau murna har da tsalle Yesmeen itama sai murna take "Abba yanzu kana nufin sabon gida zamu koma Wanda yafi wanan"? Saifullahi yace cikin tsananin murna da farinciki "Sabon gida zamu koma ai zamuje kuga gidan daga nan ma sai muje ku masa godiya" Murna kawai suke Yesmeen kuwa jiki na rawa ta d'auko wayarta ta Kira Nusrah ta hau labarta mata naji itama ta saki ihu ta cikin waya tana zata zo gidan. Nidai da ido kawai na ringa bin su banji Ina murna ba na rasa dalili hakika cigaba ne yazo mana Wanda ban tab'a tunani ko mafarkin sa ba amma na rasa mai yasa naji a madadin naji ni cikin Farin ciki nake Jin akasin haka har ga Allah bana san mu bar gidanan abokin Abban Nusrah sam bai kwanta min ba Ina addua Allah yasa tarayyar su ya zame Mana alheri. Yaran ko ta kaina basu Kara bi ba suka yi waje duuu dan Abban Nusrah ma cewa yayi duk suzo su tafi suga gidan. Basu dawo gidan ba sai wajen laasar bakin su Kamar gonar auduga sai labarta mun kyaun gidan suke da haduwar sa ,suka d'auko Dubu hamsin suka bani akan abokin Abban su ne ya basu kyauta,sai fadar kirkin shi suke suna murna wai Abban su ya zama Mai kudi nidai ban iya ce komai ba sai dai sake sake a zuciya dan ban samu fuskar ma da zanyi wata magana ba. Sai da muka zo kwanciya Naga na kasa jurewa dan Abban Nusrah cemin yayi a gobe goben nan zamu tashi mu bar gidan Kuma baza mu dau komai ba dan akwai komai a gidan Duk da nasan magana ta zata b'ata masa rai haka na daure na fara magana Ina "Abban Nusrah daga haduwar ka da abokin nan naka ina ga ko sati ba'ayi ba har a cikin Yan kwanakin nan ya maka irin wanan alherin har dasu kyautar gida Abban Nusrah Kar idon mu ya rufe ya Kamata muyi bincike a kansa kafin mu koma gidan da ya bamu,ya Kamata mu tabbatar da irin sana'ar da yake yi saboda mu samu kwanciyar hankali wlh zuciyata bata dauki wanan abokin naka ba tsoro nake ji Kar ya zama bata hanyar halak yake samun kudin sa ba Abban Nusrah" "Ya isa haka Sajeeda na fada miki Mai kudine Yana harkar Mai Kuma babban dan kasuwane bansan sau nawa kike so na fada Miki ba, ya za'ayi cigaba ya zo mana har gida ki tsaya kina wani kananan zance an gaya Miki banyi bincike akan sa ba Mai kudine na fada miki dan haka idan Zaki saki jikinki mu ci arziki toh idan bazaki saki ba wanan matsalar ki ce" Yaja dogon tsaki ya kwanta tare da juya min baya "Allah ya baka hakuri Abban Nusrah ai bansan kayi bincike akan sa ba Allah yasa mu koma gidan a saa" "Ameen" Kawai yace ya Kara Jan bargon saman kansa. Wlh a ranar sai naji na kasa bacci kallon dakina dana kwashe shekaru a ciki kawai nake sau uku Abban Nusrah na farkawa ya leka fuskata idan yaga idona biyu sai ya koma ya kwanta yaja tsaki ana hud'u da ya leka fuskata muka hada ido sai ya Kara Jan tsaki Yana "Wai me kike yi baki yi bacci ba"? "Bana Jin baccin ne Abban Nusrah Ina ta jimamin yadda zamu tashi mu bar
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111