Chapter 27
Chapter 27
alheri a wajen aikin sa Yana tunanin ma zai fara gini A Abuja" Ni dai Jin sa kawai nake dan ni kadai nasan me nake ji a jikina a yanzu ma kaikaiyi nake ji sama sama sai naji kamar abu ya zubo. A haka na kwanta ni ba bacci ba ni ba Ido biyu ba,wajen uku dai bacci ya daukeni sai na hau mafarki Abban Nusrah ya Kai mu wani gidan bene wai gidansa ne nazo shiga na fada wani Rami dake gaban gidan,sai na hau ihu Ina mikawa Abban Nusrah hannu akan ya taimaka min na fito,a madadin ya taimaka min sai ya hau watso min kasa. Ihu nake da iya karfina amma ba mai jina sai da ya kusa gama rufeni da kasa na farka a gigice Ina sallati nabi na hada zufa,a hankali na kalli wajen da Abban Nusrah ke kwance naga baccin sa kawai yake har da munshari,a hankali na Kara tuno mafarkin da nayi Ina wane irin mafarki ne wanan Jina da nayi a jike kamar wacce tayi fitsarin kwance yasa na Kai hannu na shafa wajen da nake kwancen naji a jike,cikin mamaki na fara k'ok'arin mik'ewa tsaye Dan kamar dai fitsarin nayi,yadda naga zanin jikina a jike. Koda na cire zanin na Kai hannu jikina na shafa ruwan na Kai hancina dan na shinshina naji ko dai fitsarin nayi kasan zuciyata kuwa sallati kawai nake ko da na Kai hannu hancina wani irin wari naji nayi saurin cire hannuna hankalina a balain tashe "Wanan ruwan daga ina"? Na tambayi kaina Ina cire wandon jikina gabad'aya na Kara Kai wandon hancina naji wani irin wari Kamar gurbatacen kwai ya daki hancina na wurgar da wandon jikina na d'aukar rawa mai ke Shirin faruwa dani haka?wane irin ruwa ne wanan yake fitowa a jikina. Kuka na rushe dashi daya saka Abban Nusrah tashi a firgice Yana "Sajeedaa lafiya Mai ya faru"? "Abban Nusrah na Shiga uku na lalace kaga ruwa mai doyi ke fita a jikina innalillahi wa Inna ilaihi rajiun Na Kara rushewa da ihun kuka Ya taso daga kwancen da yake ya zagayo wajen da nake tsaye Yana "wane irin ruwa Kuma Sajeeda"? "Farkawa nayi daga bacci najini a jike,kaga wajen da na kwanta Abban Nusrah kaga zanina mai ke Shirin faruwa dani Abban Nusrah tunda jiya nake Jin wani iri a jikina Abban Nusrah,tun jiya da ka kusanceni ban Kara jina daidai ba" "Bangane baki Kara jinki daidai ba Mai kike nufi?watakila infection ne dake ki kwantar da hankalin ki gobe da safe sai mu koma asibiti kije bandakin ki gyara jikinki" "A Ina zan samo infection Abban Nusrah idan ba kai ne ka saka min infection ba a ina zan samo" "Ta Ina Zan saka miki nima ki daina kukan nan kije bandaki ki gyara jikin ki gobe idan muka je asibiti sai muji Mai ya kawo Miki farin ruwan" Kuka kawai nake da iya karfina Gwara kowane rashin lafiya da wanan masifar dake neman Samuna,Taya ruwa zai ringa zubo min Mai wari, tunda nake a rayuwa ko discharge ban taba ba,amma dare daya na tashi ruwa na zubomin mai wari,nan ko maganin Mata indai na matsi ne bana amfani dashi saboda tsoro. Idan har ba Abban Nusrah ne ya kwaso wani abun yazo ya saka min ba Kuma iya sanina ba maneman Mata bane sai dai idan Wanan tsinanne abokin nasa ne zai dora shi a hanya mara kyau. Baccin da ban koma ba kenan na Shiga bandaki na wanke jikina da ruwan dumi da Dettol na samo sabon pant na saka,wanan tashin hankalin da na tsinci Kaina a ciki ya d'auke min tunanin mafarkin da nayi. Sai da nayi Sallah Asuba bacci ya daukeni. Yesmeen Bata wani samu baccin kirki ba dan gani take tana kwanciya Kabiru zai iya shigowa d'akin,a duniya ba Wanda take tsoro sama da Kabiru,a jiya sau uku tana taka abu dan ta cire glass din fitilar d'akin ta tsoro na hanata tasan akwai abu a cikin fitilar, mafarkin da tayi da ta kunna wutar d'akin ta hau ihun idonta ya tsaya Mata a zuciya,sai ta tafi tunanin yadda Annur ya kurmance tasan ita Kabiru ya so ta kurmance Allah ya tsallakar da ita,shine ya Kara biyo wa ta wanan hanyar dan ya makantar da ita tunda tasan sirrinsa sau uku tana mafarki iri daya ta kunna fitilar ta makance,bata mafarki a banza dan Sajeeda ma hanata take ta Fadi mafarkin da tayi,dan Haka ma mahaifiyar ta take indai tayi mafarki sai ya tabbata saboda ance tana da Aljannu,shiyasa da aka gano itama in tayi mafarkin tabbata yake aka hanata fadar mafarki saboda Kar a fassarata. Tasan da akwai matsala indai ta kunna fitilar d'akin Koda ta iddar da Sallah asuba bata koma bacci ba azkar kawai ta ringa yi zuciyarta na wajen Sajeeda rabin adduata akan Sajeeda ne, Karfe shidda ta fito daga daki dan ta fara aikace aikacen da ta saba dan su koma hutun makaranta tana ss2 a yanzu. Yau gabadaya bata ji motsin Kabiru ba. Koda ta Gama share ko'ina Dustin bin din kitchen daya cika da shara ta d'auka dan taje ta zubar a a katon Dustin din dake wajen hanyar fita. Tana zuwa ta zubar da sharan muryar Kabiru da taji Yana magana a waje yasa ta tsaya cak kirjinta na bugawa da Jin ya ambaci sunanta. Hakane yasa ta Kara gyara tsayuwarta tana Jin Mai yake cewa,abinda taji yasa ta zaro ido jikinta na d'aukar rawa sallati kawai take a zuciyarta hankali a tashe ta koma cikin gidan ya shige daki ta hau safa da marwa in ta zauna bata tsira ba in ta gudu ma bata tsira ba dole tasan nayi kafin Kabiru ya samu cikar burinsa a kanta tuni taji bama zata iya zuwa makarantar ba. Tana Jin motsin Hamza da Annur Amma ta kasa fitowa. Jikinta rawa kawai yake har taji Kabiru ya shigo Yana tambayar su Hamza inda take ya hau kwalla mata Kira ta fito a guje. Ya daka mata tsawa akan ta hada wa su Hamza tea su Sha shayi su tafi makaranta. Jiki na rawa ta shige kitchen ta hau hada breakfast. Sajeeda Ban farka ba sai wajen goma da rabi na safe Koda na farka ba kowa a d'akin,Ina k'ok'arin mik'ewa tsaye naji wani irin kaikaiyi a gabana tuni na saka hannu na fara susa da na tuna ruwan daya zubo min jiya mai wari sai naji hankalina ya Kara tashi Ina cikin susa Abban Nusrah ya shigo da faranti a hannun sa. "Kin tashi"? Ban iya bashi amsa ba har ya zauna Hannuna a cikin zani Ina susa,wai jikin naki ne har yanzu" Tun dazu nake so na tashe ki ki karya na Kai ki asibiti a duba ki bansan Mai ya kawo Miki wanan ruwan ba" Karbi shayi ki sha da magungunan ki idan kin gama sai mu tafi. Bata abinci nake ba hakane yasa na girgiza Masa Kai akan bazan ci ba ya dage min akan sai na karya Koda na karya na shirya dan muje asibitin yayata Abu ce ta kirani akan suna hanya ita da yar kanwar babarmu Asmau sun kusa isowa. Hakane yasa na cire hijabina na koma na kwanta nace masa ya bari
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111